Showing 63001 words to 66000 words out of 112633 words

Chapter 22 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt

Advertisement

07 Aug 2025

9131

ya kamata su sassauta masa, idan yaje dakin Dadah bata wani sauraron sa, balle kuma Abidah da taso tafi kowa daukar zafi ita da mijin ta Uncle Aliyu da Safiyya na tayasu, sai yaji duk ya sake tsangwamar kansa.
  Haka akayi biki aka watse aka kawo amarya, ranar bai iya baccin kirki ba, atleast yaso yaji ta bakin ta akan dalilin daya sa tayi masa hakan, sai dai duk cikin su babu wanda yake da niyyar sauraron sa. Hakan kuwa ya taimaka wajen dasa mummunar kiyayyar su a zuciyar sa. Zuciya bata da kashi, tuni ta shiga ingiza shi, da sunan daukar fansa wanda yake ganin haka ne kawai mafita.

***BAKAR RANA!***

Tana kwance ta bubbbude curtains din dakin ta saboda yanayin da ake ciki na zafi, gashi ranar babu wuta sai zafin ya kara yawa. Motsi taji kamar ana taba kofar ta, ta dan cire kanta ta dubi kofar na dan wani lokaci, maida kanta tayi ta rufe idon ta dan yadda baccin ke fizgar ta, ba zata iya hakura ba.
  Yamma ce wajen karfe hudu da rabi, a ka'ida ba'a son baccin na rana, sai dai ita ta rasa dalilin jin nasa yau sosai, shiyasa ma ta kora Farouk da Ja'afar wajen Dadah tayi kwanciyar ta. Nan da nan bacci ya dauke ta me karfin gaske.

***Yau ranar daban take da dukkan ranakun da yake zuwa ganin gida, yau yana jin shi cike da son kasancewa da ita, yadda yayi kewar ta ba kadan bace shiyasa ma bai sanar da kowa zuwan nasa ba. A matukar gajiye ya shigo gidan, ya kalle bangaren Dadah sai ya wuce kai tsaye zuwa nasu bangaren, ta sallama ciki ciki ya tura kofar, yana son bata mamaki, shiru ko ina baka jin motsin komai. Ajiye kayan hannun sa yayi kai tsaye ya nufi dakin baccin su, da karsashi ya tura kofar ba tare da tunanin komai ba.

Runtse idon sa yayi ganin komai na dawo masa a ƙwaƙwalwar sa, hoton da ya riga ya zama permanent a cikin zuciyar sa ya shiga dawo masa, numfashi ya soma ja cikin fitar hayyaci jikin sa ya soma rawa, kokarin tashi yake daga wajen bayan ya saki diary din hannun sa ya kasa, sai ya koma yaraf ya zauna yana kokarin saita kansa yana bawa kansa k'warin guiwar tsayawa yabi komai.

Mugun gani kamar yadda ya kamata ya kira wannan rana, Abidan sa da kaninsa, a dakin sa na sunna cikin yanayin da zuciya da ruhi ba zasu iya dauka ba, da wani irin tashin hankali ya hau dukan su a tare dukka su biyun, duka irin na wanda yake jin kamar za'a zare masa numfashi ya bar duniyar.
  Kallon cikin ido Adam ke yi masa, kwatankwacin kallon tsanar da Daddyn ke masa, jifa yayi dashi ya bugu da bango kansa ya fashe, a take jini ya shiga malala a wajen babu alamun rai a jikin sa.
    Daidai lokacin ta kwalla ƙara tana kokarin neman abun da zata kare jikin ta, nufo ta yayi bayan ta samu nasarar jan dogon Hijabi ta zura ya shak'e ta, kakare ta hau yi kamar zata mutu, da kyar ta bude baki cikin galabaita tace

"Ka... Tsaya.. ka saurare ni, wallahi ba abinda kake tunani bane."

Wurgi yayi da ita ta fada a saman drower ya shiga kokarin zare belt din jikin sa, daidai lokacin Dadah ta fado dakin a hargitse, abinda ta gani ya firgita ta, bata san sanda tayi kan shi tana kiran sunan sa ba

"Kabir!!! Zaka yi kisa, innalillah wa inna ilaihi raji'un."

Sakin belt din hannun sa yayi yana ja da baya ya fita daga dakin da sauri, rudewa Hajiya tayi ganin jinin dake fita akan Adam, da sauri ta yo waje tana kiran Kabir ɗin. Chak ya tsaya lokacin har ya kusa fita daga gida, a gaban sa ta tsaya tana kuka sosai

"Dan Allah karka tafi, kar ya mutu ka taimaka wa uwar da bata san komai ba sai lafiyar d'an ta, dan Allah."

Hannun ta ya kama, ya rike gam yana sauke ajiyar zuciya, sakin ta yayi ya koma ciki da sauri, yana zuwa ya daga shi ya fito dashi, ya saka shi a mota yaja ya fita daga gidan.

***Da rarrafe ta isa gaban ta muryar ta ta dashe saboda tsabar kuka, ta rike kafarta

"Dadah dan Allah kiyi min rai, ban aikata ba wallahi bansan komai ba, bansan mai ya faru ba, nasan kin yarda dani, nasan zaki fahimce ni."

Ga mamakin ta sai gani tayi ta janye kafarta, ta bar wajen da sauri ba tare da tace komai ba.

Daki ta koma ta fada toilet ta sakar wa kanta ruwa, kuka take a cikin ruwan tana tunanin abinda ya faru, wannan wacce irin bakar rana ce? Waye zai saurare ta ya yarda da abinda zata ce? Tana nan zaune jigum har suka dawo daga asibitin, da sauri ta mike jikin ta na rawa ta yo wajen, tun kafin ta k'arasa ya dakatar da ita

"Karki ƙaraso nan, na sake ki saki uku! Keji ban yafe miki cin amanar da kikayi min ba."

"Yaya!"

Aliyu ya fada da karfi yana shigowa ciki, da sauri Safiyya tayi wajen ta ganin yadda take layi kamar zata fadi

"Babu ruwan ka Aliyu, ta chanchanci fiye da haka ma, dan dai hakan shine karshen hukuncin da zan mata, taje na barta da Allah!"

"Amma Yaya da ka tsaya kaji uzurin ta, haba yaya, Anty Abidah ce karka manta kafi kowa sanin halin ta, ya ba zaka bata damar kare kanta ba?"

A zafafe Dadah ta kalle shi

"Kayi min shiru Aliyu, babu ruwan ka."

"Dadah kema baki yarda dani ba? Baki san abinda zan iya aikatawa ba? Iya zaman da mukayi?"

Ta tambaya tana kuka sosai, girgiza kanta tayi

"Bani da sauran zama a inda ba'a san daraja ta ba, ba'a taba tsayawa a saurari uzurin ka balle kasa ran samun sauki, tir daku nayi dana sanin shigowa rayuwar ku, a yau ni Abidah na yanke dukkan wata alaƙa tsakani na daku, babu sauran komai tsakanin mu sai ta yarana guda biyu, dan yar uwata da Farouk, wanda su kuwa kamar dole na ne  duk da haka zan tafi na bar su tunda ba dasu nazo ba!"

Tana kaiwa nan taja hannun Safiyya dake kuka sosai ta fita daga dakin fita ta har a abadah.!
***     *DG*
      

         28

****
Da sauri ya rufa musu baya yana kwala mata kira, bangaren ta suka nufa, tana zuwa ta haɗa dukkan abinda tasan mallakinta ne, Farouk ne da Ja'afar suka shiga kuka ganin yadda iyayen su biyu ke kukan, tsaye uncle Aliyu yayi a dokin kofar ransa na mugun suya, mai yasa sam yayan nasu baya tsaya wa yayi bincike ne? Komai sai ya yanke hukunci a cikin fushi da bacin rai bayan ba haka Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya koyar damu ba, lallai duk wanda zai biye wa zuciya yayin da ransa ya ɓaci zai iya aikata komai, ciki kuwa har da aikin da mutumin da ya fita daga hayyacin sa.
   Gashi yanzu ya aikata abinda har ya bar duniya ba zai taba daina dana sani ba, saki uku, a lokaci daya? Saki da aka ce idan akayi shi al'arshi ce take girgiza. Anty Abidah bata chanchanci hakan daga gare su ba, matar data tsaya da dukkan karfin ta wajen ganin ta kyautata ma kowa.

Zuwa tayi zata wuce ta gefen sa yayi saurin tare kofar yana jin kamar alamun kukan shima

"Anty yanzu tafiya zakiyi? Dan Allah karki tafi."

"Uncle Aliyu kenan, zamana ya kare a gidan nan, karka manta da babu igiyar auren yayan ka yanzu akaina. Alfarma daya zakayi min, ka taimaka min ka kular min da Farouk da Ja'afar, yayana ne dukkan su saboda haka amanar su na hannun ku ku biyu."

Girgiza kansa yake ya rasa ina zai tsoma kansa, gaba yayi ya sake baya ganin yadda yaran ke kukan fitar hayyaci, hannu yaga ta bude musu suka tawo jikin ta gaba dayan su. Runtse idon ta tayi hawayen da take kokarin makalewa suka shiga saukowa.

"Allah yayi muku albarka!"

Sai ta janye su tayi hanyar barin gate din Safiyya na take mata baya.

***
A zafafe ya fada falon, wurga idon sa ya shiga yi har ya sauke su akan Adam dake jingine da kujera kansa na kallon kasa. Da sauri ya isa gareshi ya ci kwalar rigar sa, idon sa daya rine yayi ja ya sauke masa aka cikin matsanancin fushi yace

"Me yasa zakayi mata haka? Me yasa zaka manta alkhairin ta gareka musamman, baka san halacci ba?"

Kwace wa yayi daga rikon daya yi masa, cikin fushin shima ya taso masa

"Just stay out of this idan ba so kake kaima ka shiga lissafi ba."

"Idan naki fa? Me zakayi?"

Murmushi yayi ta gefen bakin sa ya juyar da kansa

"Ka shiga taitayin ka, na wuce yadda kake tunani wallahi, zan iya yin komai."

Dukan kirjin sa yayi ya tura shi baya,

"Babu abinda ka isa kayi sai abinda Allah ya ƙaddara akaina."

Yana kaiwa nan ya juya ya bar masa dakin.

Bangaren Dadah yayi yana riƙe da hannun yaran, tana zaune ta rasa ina zata saka kanta, da sauri ta dago tana ganin shine ta mike

"Aliyu, dan Allah karka ce zakayi bincike akan abinda ya faru yanzu akan yayar matar ka, karka ce zaka tsaurara bincike na roke ka."

Durkusawa yayi a k'asa ya kaskantar da kansa yace

"Ke mahaifiya tace, idan har kike bani umarni dole nabi ko da hakan zai zamar min matsala, wajibi ne nayi idan har bai sabawa Allah ba, sai dai a wannan karon zan nemi afuwar ki tun kafin àbinda zai kasance ya kasance, zan tsaya wa Anty Abidah na bi mata hakkin ta, ba zan hakura ba har sai sanda gaskiya tayi halin ta. Ki yafe min."

Kuka ta saka ta shiga yi mishi magiya ya bar komai kar ya tsaiwata bincike, babu alamun zai saurare ta, tashi yayi da nufin barin dakin tayi saurin rike shi tana kuka sosai.

Yana tsaye kyam a bakin kofar dakin ya harde hannun sa a saman kirjin sa, cikin isa da gadara yacw

"Barshi, wanda bai ji bari ba, shine zaiji hoho."

Juyowa Aliyu yayi a fusace ya bar dakin da sauri, kukan yaran dana Dadah ya hautsina dakin, be bi ta kansu ba ya wuce uwar dakin ta, yar jaririyar sa na kwance tana jujjuya kafarta da alamun ta jima da tashi har tayi kuka ta gaji, yau ne karo na farko daya mata kallon tsaf tun ranar da aka kawo ta gidan, babu maraba tsakanin ta dashi sai ta banbancin jinsi. Shafa kanta yayi makogaron sa na kaiwa da komowa yace

"I ll come back for you one day!"

***
Tsawon sati kenan Daddy na rufe a bangaren sa, baya zuwa ko ina ko sallah ma a daki yake yin ta, sosai abin ya taba shi, yana ganin kiran Alhaji Marwan amma sam yaki dagawa, duk sanda ya runtse idon sa su yake gani, sun cutar da zuciyar sa, sun dasa masa wani babban al'amari da zai ta bibiyar tunanin sa.
  Tsawon satin nan babu wanda ya leko tsakanin Aliyu da Adam, yaran uku dake gaban ta su kadai take kalla taji hankalin ta ya tashi, bata taɓa fatan ko tunanin abinda zai zo ya wargatsa musu kwanciyar hankali ba cikin d'an kankanin lokaci, gaba daya gidan ya fita daga kanta bata fatan cigaba da zama cikin sa, zaman da zai cigaba da yi mata famin abinda ya faru.

Sai da Alhaji Marwan yayi da gasken gaske sannan ya samu Daddy ya fito, yayi muguwar rama da baki, fada yayi ta masa amma bai sanar dashi abinda ya faru ba, labarin yafi gaban a bada shi ba, duk kuwa da yadda suke da karfin abota amma ba zai iya ba.
   Tubure musu Dadah tayi akan lallai sai ta bar gidan, ba kuma Katsina zata koma ba, bata son duk wani abu da zai tuna mata komai, ganin ba zata amince da kokarin kwantar mata da hankalin da suke kokarin yi ba yasa suka yanke shawarar sama mata gida a Kano, wannan shine asalin komawar Dadah Kano tare da Farouk, Amal da Ja'afar.

***
Daddy na rurrufe ko ina na gidan dan komawa aiki Adam ya shigo, har lokacin kansa rufe yake da bandage, dauke kai Daddy yayi kamar bai ganshi ba, ya wurga masa keys din bangaren sa

"Ka duba komai naka ka kwashe ka bar min gida."

Dage kafadar sa yayi ya tsuguna ya dau keys din, bud'e dakin yayi ya dauke abinda zai dauka ya fito,kamar yadda ya wurga masa keys din shima hakan yayi, ya gefe shi dashi cikin keta yace

"Sai watarana!"

A kusan tare suka bar gidan, sai da Daddy ya fara biya wa ta Kano ya duba Dadah, kafin ya wuce wajen aikin daya dauki lokaci mai matukar tsawo kafin ya sake waiwayar gida.
   Samun babban matsayin da yayi shi ya rage masa nauyin abubuwan da yake, ya tattara hankalin sa waje daya yayo gida, Dadah na ganin shi tasa masa kuka, kukan dake nuna tsantsar halin da take ciki, sai a sannan take sanar mishi ta mutuwar Adam din, hatsarin mota ne ya rutsa dashi daga Lagos zuwa Kano ko gawar sa ba'a kawo ba.
  Babban tashin hankalin ta bai wuce daina ji daga Aliyu da Safiyya ba, tun bayan rasuwar, taje gidan yafi a kirga amma magana daya take samu daga makotansu shine sun yi tafiya.

Takanas Daddy yaje da kansa har wajen aikin Aliyun, sai a sannan ne ma yake jin labarin ai ya bar aiki tun da jimawa, abun ya matukar daure masa kai, haka ya dawo a sanyaye gida ya sanar wa Dadah, wadda hakan ba karamin sake gigitata yayi ba,tun daga nan basu sake k'ara ji daga gare su ba, a hankali suka manta, kamar an cire musu su da abinda ya shafe su daga ƙwaƙwalwar su, babu wani daga cikin su daya sake yin maganar sa har kawo yanzu!

****
Sake shiri yayi, ya fito a cikakken mutum mai cikar zati da haiba, sai dai yanayin fuskar sa kadai zata tabbatar maka da ba daidai yake jin jikin sa ba, bayan mota ya fada ya d'an kishingida kadan yana lumshe idon shi, tabbas yana bukatar ji daga gareta, yana so yaji komai daga bakin ta ko da kuwa ba zata saurare shi ba zai gwada sa'ar sa.
Su biyu ne kaɗai daga shi sai driver sa, yau baya jin zai iya yin wannan tafiyar da masu kula dashi, bayan haka ma baya bukatar hayaniya yana so yaje mata a Kabir ɗin sa, Kabir ɗin data sani shekarun baya ba na yanzu ba..

"Ina zamu je ranka ya dade?"

"Kaduna." Ya amsa mishi a gajarce yana sake mikewa sosai.



***
Duk nauyin dake cunkushe a zuciyar sa yau yayi sauki har yana jin bukatar fara aiwatar da abinda ya kawo shi. Shigar manyan kaya yayi kamar ba a k'asar masu jajayen kunne ba, ya dora hula ya fito a cikakken bahaushe bakar fata, kai tsaye inda sukayi zasu hadu ya nufa da taimakon address din daya bashi.

Daga d'an nesa ya hango shi, tabbas shine mutumin nan na ranar nan, ya akayi suka sake haduwa? Daga kafar shi yayi cikin sauri ya nufe shi, daf da zai isa gareshi yaga ya bude wata mota dake ajiye wajen ya shiga, bai iya ganin fuskar sa sosai ba sai rabi kamar wanchan lokacin, kamar an dasa shi a wajen haka ya tsaya yana kallon motar har ta bar wajen, jan ƙafarsa yayi zuwa shagon yana kokarin ganin ya yakice shi daga zuciyar sa, ya rasa dalilin ma da yasa yake jin wani abu game da mutumin. Ganin zai bata wa kansa lokaci yasa yayi saurin shigewa ciki yana duba agogon hannun sa, yasan baturen mutam da ka'ida, baya so ka saba masa alkawari.
Tambaya yayi aka nuna masa inda zai same shi. Cikin aiki ya tarar dashi kacha-kacha, yana ganin shi yayi dariya, yana tura masa takardun gaban sa, da mamaki Farouk ya kalle shi amma kafin yayi magana ya riga shi

"No time to waste."

Gid'a kansa yayi a hankali ya furta

"Nima bani da lokacin batawar ai, I'm here for it"

Aikin ya shiga nuna masa,da yadda yake so komai ya kasance, babu wani bata lokaci ya fuskanci abubuwa da yawa sai dan abin da baza'a rasa ba wanda sai a hankali dama.
Ranar a gajiye likis ya koma gida cike da farin cikin fara aikin da yayi da shugaban shagon wanda dalilin social media suka hadu tun da dadewa, sai gashi yayi masa rana a lokacin da bai taba tunani ba.
Wanka kawai ya iya yi yasha tea ya kwanta dan sosai yake jin bacci, yana kwanciya kuwa baccin ya dauke shi wanda rabon da yayi irin sa ba zai iya tunawa ba. Gashi dama duk sanda yayi yunkurin baccin sai tunanin ta ya shigo masa, daga nan sai yaji sam baccin ya fita daga kansa, daga nan sai ya dasa sabon tunani har zuwa sanda baccin zai dauke shi ta karfin gaske ba tare da ya shirya ba.

*** *AMINATU*

Na cigaba da zuwa makaranta da taimakon Allah dana Baba Altine data zama wata babbar bangare na sabuwar rayuwa ta.
Bani da matsalar komai gefe ga Kamal daya zama abokin shawara ta. Ban yi watsi da duk abinda Anas ya ce min ba ina matukar kokari wajen ganin na kare mutunci na.
Lokuta da dama nakan tuna Baba, Inna da Karime, Yalwati da sauran mutanen da suka fi kowa kusanci dani a da amma babu ko daya cikin su yanzu a rayuwa ta, hakan ba karamin sani yake na kara tuna wacece ni ba, mara asali da tushe abar kyama ga kowa.
*DG*

             *29*

★★★★
Dukkan abubuwan bukatuwa na makaranta ta Kamal ya dauke min shi, tun ina fada har na kyale shi na zuba masa ido, ranar ina tsaka da duba wani handout ya iske ni wajen da muka saba haduwa, a dan gefe ya zauna yana leken cikin handout din

"Kaga yan allazi boko."

Yace yana dariya, harara na sakar masa ina janye handout din.

"Wai dan Allah yaushe zaki kawo min Iman ne, I'm dying to see her kinsan abinki da hanta da jini, daga zuwa sau daya shikenan nasan ma ta kara wayo."

"Sai dai ka shirya kaje da kanka, ni bazan iya dauko

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login