Showing 57001 words to 60000 words out of 112633 words
Chapter 20 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt
ido na na ciccikowa nace
"Amal?"
"Abinda kunnuwanki suka ji haka yake, saboda haka karki bata min lokaci, kinga tafiya ta."
Ina kallon ta ta juya tayi hanyar fita daga layin, kuka nasa sosai, na kasa daga kafata daga wajen, ina kallo ta haura daga layin, tun ina hango ta har na daina, durkushe wa nayi a wajen na saki kuka sosai kamar raina zai fita.
Rano
8a: DG
24
★★★
Da kyar na mike kafata da tayi nauyi na karasa gida, a waja na tsaya na goge hawayen fuskata na shiga gidan, da kallo Altine ta bini tana karantar yanayin fuskar tawa, ciki nayi ba tare da na tsaya yar hirar dana saba mata ba.
Ina shiga daki na sake sakin kuka, kuka me cike da ma'anoni da yawa, a yau komai ya dawo min sabo, ina ji kamar a yanzu komai yake faruwa dani, idan har da gaske Amal take, Farouk ya aure ta, to tabbas ya manta dani, ya rufe ni a cikin babin rayuwar sa kenan, idan ko haka ne bai kyauta min ba, bai min adalci ba, bayan ya koyo min yadda zan rayu da son sa, ya tafi ya barni a sanda nafi bukatar sa.
Amal yar uwar sa ce, nasan shakuwar da ke tsakanin su, ban taba kawo hakan a nufin soyayya suke ba, sai yanzu nake hango wasu abubuwan da suka dangance ta din, ta yadda yake yake bata lokacin sa.
Har Ramlah ta dawo daga makaranta ban bar kukan da nake ba, ina ji a raina ina bukatar nayi kukan, ko naji sauƙin zuciya ta, yadda ta tarar dani ne ya sa duk ta rikice, a dan zamana da ita na shaku da ita da har bana iya boye mata damuwa ta, ko ba haka ba ma ina bukatar wanda zai fada ma kuka na ko da ba da nufin a share min kukan ba, sai dai ko yaya na zanji sauƙin abinda ke damuna.
Yanzun ma ban boye mata ba, na sanar da ita komai, girgiza kanta ta hau yi tana dawowa kusa sani sosai kafin tace
"Aminatu har yanzu baki san wasu matan ba, ya zaki yanke masa hukunci da abinda ta fada miki, ina kyautata zaton babu masaniyar sa a komai, a yaya kika ganta? A nutse take alamar wadda take cikin kwanciyar hankali tayi sabon aure, ko kuwa? Kuma baki yi tunanin abinda yasa ta yi miki haka ba? Bayan ko ni nasan yadda kika daukake ta a zuciyar ki? Abu daya ne, kishi take ko dai tayi kokarin samun abinda yake mallakinki bata samu din ba, ko kuma ta samu amma babu kwanciyar hankali."
"Kin batar dani Ramlah, kina nufin Amal nada hannu a komai?"
"Eh haka tunani na ya bani, ko da ba komai ba, amma a wannan lokacin akwai ayar tambaya akan, akwai babban dalilin da yasa tayi miki hakan."
"Taki bani damar da zan san inda take, ballantana na rok'i alfarmar ta hadani dashi ko da na dan sakanni ne, akwai tambayoyin da nake son yi masa ne, sannan na nuna masa abinda ya tafi ya barni dashi, shine kawai buri na."
"Shiyasa nace miki abinda tayi nada alaka da hakan, tabbas bata son haduwar ku dashi ne, idan har ya cire ki a ransa, ba zai ji shakkar haduwa dake ba, ita kuma kai tsaye zata hada ku dan tasan bashi da alaka dake, amma me? Sai taki ta hauki da cin mutunci, Allah ma yaso ta ba tare dani bane, wallahi da sai na saki shegiya na yar a wajen."
Murmushi nayi ganin yadda ta hakikance, sai na zame na kwanta a wajen ina jin kamar wata dama na samu mai muhimmanci a rayuwa ta ta kuma kubce min. Yin ranar haka nayi shi sukuku, abincin kirki ma ban iya ci ba, daren wuri na lallaba Iman tayi barci ni kuma na hau kogin tunani.
Dan buga gadon tayi tana harara ta, sai a lokacin na lura da tsaiwar ta akai na
"Allah ki rage tunanin nan, is not good for ur health,ki taso Ya Anas na kira."
"Bacci fa na fara, Please kice masa nayi bacci kaina ke ciwo kinga kuma ina bukatar hutu."
"Kinsan shi sarai, sai ya zo har dakin, babu ruwana wallahi ki taso ni nayi gaba."
Ganin da gaske tayi ficewar ta yasa na mike da kyar na dauraye fuskata na zura dogon Hijabi na fito, idon sa kur akan kofar dakin namu, ina kallon yadda ya sauke ajiyar zuciya a boye ba tare da sun ankara ba, dauke kaina nayi na karasa na zauna a gefen Amal,.
"Bak'ya gajiya da zaman daki?"
Yace yana kallo na, da sauri Hajiya tace
"Bata fa dade da tafiya dakin ba, kaine dai zuwan ka kenan shiyasa."
"Duk da haka Hajiya, ta fiya takura kanta a daki, ya kamata ki dinga fitowa ana hira dan an riga an zama daya kin gane?"
Daga kaina nayi bance komai ba, maida hankalin sa kan Hajiya yayi
"Ina ganin shawarar siyan adaidaita sahun (babur mai kafa uku) ita kawai zamu dauka kawai, ko hudu ne a samu a siya sai a dinga kawo balance duk sati."
"Hakan yayi, Allah ya taimaka."
"Nace ba, idan tana da ra'ayin hakan sai a hada da ita, idan yaso ita ma sai a dinga kawo mata wani abu duk sati..."
Ya karashe yana kallo na,
"Kina da ra'ayin siyan abin hawa ana miki haya? Kudin ki zai isa ki sai guda daya ko ba sabuwa bace, idan Allah yasa miki albarka sai kiga kin maida kudin kin sayi wata."
Dadi ne ya kamani, dama ina ta tunanin abin yi, tunda zaman ba zai yiwu haka ba, ko ba dan Iman ba ko dan makaranta ta, da sauri na amince, dan shine kawai abinda nasan za'a yi min ɗin ba tare da ya shiga lokacin makaranta ta ba.
Murmushi yayi, daga ganin yadda na amince din yayi masa dad'i, dan shi mutum ne mai son a yarda shi, kuma kai tsaye yake nuna maka yadda yaji game da kai.
"Shikenan, Nagode da damar da kika bani, sai a hada a siya dukka Hajiya, hakan ina ganin yayi ko?"
"Yayi." Tace Muryar ta a dan ciki
"Yauwa Anas, wai ya maganar da mukayi ne tun ranar? Shiru fa nake ji ya kamata kasan abinda kake ciki, shekarun ka kara ja suke."
"Hajiya kenan, ai ina ganin lokaci kawai nake jira na bayyana miki komai, ki tayani da addu'a kawai ta karbi tayi na, dan nasan zaki yi farin ciki sosai da zabi na."
"Ah masha Allah, shine tuni baka sanar dani ba? Ka barni ina ta tunanin wa zan binciko maka a dangi."
"Na hutassheki Hajiya, ke zaki fara sani bayan ita, kuma nasan zaki yi farin ciki sosai dan yarki ce ma."
"Toh madallah, Allah ya tabbatar mana da Alkhairi."
"Amin ya ALLAH."
"Naji kamar kuka ko? Jeki duba ko tashi tayi."
Mikewa nayi na musu sallama, kallon k'asan ido naga yayi min, nayi gaba da sauri ina jin faduwar gaba.
****
Kamar wadda aka koro haka ta shiga gidan tana waiwaye, ajiyar zuciya ta sauke da karfi ganin bata biyo ta ba, lock ta saka wa kofar ta shige ciki. Kallon tuhuma Dadah ta bita dashi kafin tace
"Ina kika je ne nake ta neman ki, baki fada min zaki fita ba kuma."
"Kati naje na siyo, ina so nayi waya na kasa siya ta bank shiyasa."
"Shine kike abu kamar baki da gaskiya?"
"Ni ba abinda nake kece kika ga hakan."
Tayi cikin dakin ta, tana shiga ta murda dan key din jiki ta cire mayafin ta ta haye gadon tana kiran number. Kasancewar akwai rata da tazara me yawa tsakanin su, sannan akwai banbancin lokaci yasa suka tsara sanda zasu dinga magana a waya, tun da tazo gidan sau biyu kawai sukayi waya. Kamar ba za'a daga ba, dan har ta fara cire rai, sai kuma taji an daga ɗin, cikin magana k'asa-k'asa ta shiga bayanin komai, bata wani dau tsawon lokaci ba ta ajiye wayar tana murmushi.
Duk ranar da Farouk ya gama boye-boyen sa zai fito, daga lokacin zai karbe ta a matsayin matar sa, dolen sa ne, tilas ɗin sane hakan,da shi kadai zata iya rayuwa.
Sam tafiyar sa bata dame ta ba tun bayan da aka tabbatar mata da ita din matar sa ce, aure ya dauro, zata jira shi komai daren dadewa, sai dai ba zata taba gangancin barin sa ya hadu da Aminatu ba, wannan Alk'awari ne tayi wa kanta, tunanin yadda akayi ma har Aminatu tazo nan ɗin, ayi sanin ta bata da wasu data sani a garin na Kano, sai gashi ta hadu da ita a lokacin da haduwar tasu tamkar yankewar farin cikin tane, kuma a unguwa daya da wadda take rayuwa a yanzu, shin dama tasan inda Dadahn take zaune ne ko kuwa co-incidense ne? Amma ta yaya? Idan har ta sani ba zata nemi ta kawo ta ba ai, toh amma? Kanta ya cunkushe ta rasa kalar tunanin da zata saka.
Koma dai menene, ba zata taba barin ta ba, ko da kuwa hakan na nufin tonuwar asirin dake rufe shekaru masu yawa ne!
★★★
Riga ce karama da dogon wando a jikinsa ya dora doguwar Jacket a sama, kansa ruf da woody cap sai bakin glass me matukar duhu daya rufe ilahirin kwayar idon sa, tun sanda abin ya faru yake cikin garin na Lagos, bai taka ko nan da chan ba sai a yau da zai bar k'asar, bolt ya kira suka zo har gaban hotel din daya sauka ya fito suka dauki hanyar filin jirgi.
Sai da ya daidai ta a cikin jirgin sannan ya ciro wayar sa ya kunna, sakonni suka fara shigowa, sai daya tabbatar sun gama shigowa tsaf,sannan ya saka wayar a airplane mode ya shiga duba sakonnin.
Daga na Daddy, Mummy, Ja'afar, Amal sai Dadah ne kowanne da abinda yake cewa, kai tsaye ya goge dukka baya son jin komai daga gare su, idan ba so suke su k'arasa shi ba, dan a yadda yake jin zuciyar sa yasan tabbas ba daidai take ba.
Gyara kujerar sa yayi sosai ya kwanta, sakonnin su kadai sun sashi ya tuna da komai. Zuciyar sa ba zata taba daukar cin amana daga mutane uku ba, Ja'afar, Amal da Dadah! Sune mutanen da ya yarda dasu fiye da kowa a duniya, fiye da iyayen da suka kawo shi duniya. Amma ta yaya hakan ta kasance? A lokacin daya gane akwai sa hannun Amal bai shiga tashin hankali ba kamar sanda take sanar masa da komai, Dadah! Why? Ya kasa gasgata hakan, gashi ya gaza samun hujjar da zata kare daya daga cikin su, shiyasa ya gaza hakuri, ya kasa juriya, ya bar su, bari na har abadah, duk kuwa da yana sa ran haduwa da Aminatu komai daren dadewa, sai dai akwai lokaci, kafin sannan, yana fatan Allah ya bashi aron rai da lafiyar da zai iya fuskantar ta, ya kuma nuna masa gaskiyar komai.
A hankali sanda jirgin su ya lula sama sosai ya furta!
"Sai wata ranah!"
★★★★★
Kullum idan na dawo daga makaranta sai nabi hanyar ko zan sake ganin ta, sai dai ko mai kama da ita ban sake haduwa da ba, tun ina saka rai har na hakura na cire na barwa Allah komai na rungumi karatu na, duk bayan sati biyu ake kawo mana balance, da su nake amfani wajen hidimar makaranta ta da abinda ba za'a rasa ba, tun Anas na fada har ya daina ya zuba min ido, daidai gwargwado yana kokarin sa a kaina duk da hakan, tun da mafiya yawancin lokuta shine yake ajiye ni a makaranta,bana cin komai har naje na dawo shiyasa ba wani kudi nake kashewa ba, nidai burina nayi karatun na taimaki kaina da yata.
Tun bayan fara zuwa na makaranta haduwar mu wajen bakwai da Kamal d'an gayu, duk sanda ya ganni sai yayi kokarin min magana a haka har na saki jiki dashi muke gaisawa, anan na gane course din da yake business adminstration. Na lura kwarai ba karamin dan masu kudi bane duba da yadda mutane keyi masa a duk lokacin da suka ganshi, bashi da girman kai ko kadan sai dai dan gayu ne na ajin farko, kullum cikin sabuwar shiga yake komai masa abin kallo ne tun daga kayan sawar sa har zuwa takalman da yake sawa.
A hankali sabo ya shiga tsakanin mu, har mu kan zauna muyi hira duk da bata fita tsawo ba, kullum maganar sa guda daya ce Kakar sa, ko da zaman mintuna biyu kayi dashi zaka tabbatar da irin shakuwar da ke tsakanin su, tabara da tsantsar gata take nuna masa fiye da tunanin mai tunani.
A off-campus yake zaune, gida guda ne yake zaune a cikin sa, duk da ba karamin takura yayi ba a yadda ya saba, amma hakan yake zaune ala dole bisa tursasawa mahaifan sa, duk weekend a gida yake yi, sai Monday da safe yake dawowa wani lokacin ma sai Tuesday, bashi da matsalar komai duk abinda yake so shi yake yi.
Ina ta sauri zan fita daga makarantar ganin yau har la'asar ta taho ban isa gida ba, mota ce ta tsaya a gabana,na daga ido na dubeshi, daman nasan sai shi, fitowa yayi ya tako har wajen da nake, ina sanye da dogon Hijabi maroon har k'asa, sai jakata dake makale jikin sangalalin hannu na.
"Gida kikayi ne irin wannan sauri Meena?"
"Wallahi yau na dade, shiyasa nake ta sauri."
"Lemme drop you mana idan ba damuwa."
"A ah Ina, bashi na samu bus ta fita dani, see you."
Nayi gaba ina nufar wajen da cincirindon mutane suka kowa na jiran abin hawa, dage kafadar sa yayi ya jingina jikin motar sa yana kallon mu, mota daya ce tazo, aka hau rububin hawa, kasa shiga nayi ina kallo aka cika ta, na sake matsawa gaba. Tsawon lokaci muka dauka shiru babu alamar zuwan wata motar, gashi ranar kudi na kenan, idan nace zan fita titi na hau normal abin hawa ba zai ishe ni ba, waigawa nayi gefe na hange shi still yana inda na barshi, muna hada ido ya saka dariya yana turo bakin sa alamar gwalo, da sauri na dauke kaina na yi gaba ina sauri ganin wata motar ta tawo, ita dinma hakan ce ta kasance, ina kallo aka gama shigewa aka barni, dafe kaina nayi dake ciwo na sake kallon sa, gani nayi ya fada motar sa ya bata wuta, yazo ya wuce ni, duk sai naji babu dadi, na hau takawa a kafa, ga yunwa gashi rashin nawa Iman abincin ta da banyi ba yasa duk sun cika sosai har na fara jin zazzaɓi na neman rufeni.
Tafiya nayi mai nisa kafin na isa gate ina yi ina haki, a wajen gate din na hangi motar sa a fake a gafen titi, an bud'e kofar mai zaman banza daidai inda zan wuce, har zan dauke kaina muryar sa ta iso min tun kafin na karasa
"Miss... da kin cire komai kinzo na ajiye ki, after all ba cinye ki zan ba, idan ma na cinye ki, za'a iya kamani ai tunda nasan za'a ce an ganni tare dake last."
Bani da zabi, ila na shigan, a hankali na ja kafafuwana na zauna ina cin magani, dariya ya sa ya ja muka tafi yana yan kananan wake-waken sa da harshen turanci.
Hanya na dinga nuna masa har muka isa, sosa kansa yayi yana kallon unguwar,
"Kinga fa akwai gidan da Daddy yaso na zauna anan unguwar naki, babu nisa daga gidan ku."
"Kafi so ka zauna Off-k kaci karanka ba babbaka ko?"
"No ban saba squatting bane a rayuwa ta, kinga ba zan fara yanzu da girma na ba."
"Yayi, nagode sosai, sai Monday idan Allah ya kaimu."
Nace ina balle murfin motar. Daga min hannu yayi ya bar unguwar, na juya da nufin shiga gida, gabana ya fadi ganin shi a tsaye yau ma kamar ranar, ya harde hannayen sa a kirjin sa, fuskar nan tasa kamar wuta. Dakewa nayi naje zan wuce ta kusa dashi, hannun sa ya sauka a cikin hannu na, da wani irin karfi yasa ya fizgoni, ya tura ni cikin gidan, kamar zan fadi nayi saurin tsayawa a kafata fuska ta dauke da madaukakin mamaki.
Da hannu ya nuna ni, cikin tsananin bacin rai ya soma magana
"Baki isa ba wallahi,kinyi kadan kina kawo mana samari kofar gidan, samarin ma na jami'a, kanana yara wanda basu mallaki hankalin kansu ba, uban me wannan dan yaron zai baki, shiyasa kika yi zaman ki a makarantar bayan yau da wuri kuke gama lecture ko?"
"Ban gane ba." Nace ina matsawa baya ganin yadda yake matso ni
"Dama ba zaki gane ba,haka zaki ce kullum akayi miki magana, U act as if baki san me mutum yake ciki ba..."
Dukan kirjin sa yayi da hannun sa biyu
"Can't you see how much I love you? Nace baki gane ba? Ke makauniya ce? Baki da ido? Ko baki da wayo? Ba zan dauka ba, ke tawa ce, mine and mine alone! Kin gane? Get it straight to your filthy head, ni zan aureki saboda haka bazan dauki ganin ki da kowanne kazami ba."
Daya bayan daya na hau kokarin fahimtar maganganun sa, kamar ya zare haka ya cigaba da magana yana sake nufo ni, yaki bari na sam na gama digesting kalaman nasa, wasu yake kara min akan wasu, a bayan mu muka ji salati, muka juya da sauri gaba daya
"Na shiga uku,Anas mai zan gani? Tsintasshiyar magen zaka aura? Innalillah wa inna ilaihi raji'un, abinda nake gudu ya faru."
Rano DG
26
BARKA DA SALLAH!
★★★
Asalin su shine jihar ta Katsina, tun yarinta shakuwar su babba ce tunda daya baya iya komai ba tare da daya ba, sun shaku matuka har zuwa girman su babu abinda ya chanja na daga yadda suke.
Asalin amintar su ta fara ne daga kusancin iyayen su maza, kar kawo yanzu.
Kabir Aliyu Shagari kenan da aminin sa Marwan Muhammad Dikko. Duk inda kake neman shakuwa da yarda da juna toh sun hada, tare suke komai tun daga matakin farko na rayuwa har zuwa shigar su jami'a.
Tafiyar su jami'a bisa mabanbantan ra'ayi be sa sun chanja ba, Kabir ya zabi bangaren