Showing 42001 words to 45000 words out of 112633 words
Chapter 15 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt
karbe ta ki sake gwada mata ko Allah zai sa a samu ruwan, kece ma dai kinki cin abinci, dole idan kika je gidan su tilasta miki sa wani abu a cikin ki, ruwan nono sai da abinci zaizo."
Hannu na mika na karbeta, na dora ta saman cinya ta ba tare da sanin takamaimai ta inda zan fara mata.
"Dauke ta ki sata jikin ki mana, shiririta."
Kamar zanyi kuka na daga hijabi na na sata ciki, juyowa yayi bayan muka hada ido dashi, da sauri na janye ido na ina kallon kasan kujerar,
"Hajiya ya za'a yi ne? Itan za'a fara kaiwa ko yaya?"
Gabana ne ya fadi, nayi kasak'e ina jiran amsar ta, waigo ni tayi tace
"Aminatu,wacce unguwar kuke? Kunga an kusa shiga Kanon mu fara rakaki gida sai mu wuce."
Rau-rau nayi da ido na da ya cicciko lokaci daya, na daure na cije nace
"Bansan kowa ba sai mutum daya, hasalima wannan ne karo na na farko dana zo Kanon, sai dai bansan inda zan same ta ba, wayar da xan kira ta na manta ta a gida."
Bude baki sukayi a tare suka ce
"Kina nufin baki san inda zaki ba?"
Daga kai na nayi ina sharar kwalla, ransa naga ya ɓaci, ya kalle me motar
"Idan kaje kwanar dawanau ka sauke mu, sai ta fada maka ita inda zaka kaita, nawa zamu biya gaba daya?"
"Anas..."
"Kiyi hakuri Hajiya, bana so daga taimako mu shiga matsala, kuma kinsan ni a rayuwata na tsani karya, me yasa zata boye mana gaskiyar ta? Sai data ga munzo zata ce bata san inda zata ba?"
"Shikenan."
Tace tana kallo na, kasa na sake yi da kaina ina kuka, zuwa lokacin jaririyar tayi baccin wahala, dan babu nonon sam yaki zuwa.
Sanda muka iso inda yace, inaji motar ta tsaya, ya fita da sauri aka bude masa booth, ya cire kayan su, bude mata kofar bangaren ta yayi yana sake daure fuskar sa tamau.
"Fito Hajiya."
Kallon da tayi masa ya dauke kai kamar be gani ba, ya maida kansa bangaren driver yana tambayar sa lissafin kudin tunda mu kadai ya dauko tun daga chan din.
"Kudin dukka kujerar zaku bayar, ita kuma idan na isa tasha sai ta sauka ta nemi wani abin hawar, iyakata tashar ne kawai."
Lissafa wa yayi ya ciro kudin ya bashi yana yin gaba, a hankali na furta
"Nagode Allah ya saka da Alkhairi."
Sarai yaji, dan har sai da yayi dan alamun kamar zai tsaya, kafin ya kara daga kafar sa Hajiyar na take masa baya. Kuka na saka sosai ina jin bani da sauran gata a duniyar nan. Rayuwata ta kare, ina ji a raina gab nake da mutuwa, sai dai idan na kalli yar karamar halittar dake hannu na, wadda yanzu dukkan rayuwar ta, na rataye a wuya na, sai naji komai ya sake min, zan rayu ko don sabo da ita, na kula da ita.
Ban yi aune ne na ganmu a tashar, sake rungume ta nayi sosai a jikina, motar na tsayawa na balle murfin na fito,ina sake karewa ko ina kallo, a karo na farko na zo Kano, ba tare da sanin inda zan dosa ba. Jakar nan ya fito min da ita, hade da sauran kayana, dauka nayi na matsa daga wajen ina neman inda zan fake don zuwa lokacin har ta kuma tashi tasa kuka, baccin nata baya nisa saboda yunwar dake damun ta. Chan na hango kasan wata bishiya, nayi saurin isa wajen, na rabe ina jijjigata. Nayi nisa a son ganin tayi shiru, kamar daga sama naji muryar sa a kaina
"Kin tabbata ba wani mugun abun kikayi kika gudo ba?"
Dagowa nayi idonmu suka sarke waje guda, da sauri na daga kaina alamun Eh
"Idan kinyi alkawarin sanar dani gaskiya, zan taimaka miki."
"Nayi Alk'awari."
Hannu ya mika ya dauki kayan nawa, na tashi da sauri nabi bayan shi.Daurin Goro*
*18*
© Hafsat Rano
ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*
07067124863
*Ko kuma*
09032345899
*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽
https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo
18
***
Adaidaita sahu naga mun dosa, muna zuwa ya mika kayan ciki yace wa Hajiya
"Ku tafi bari na hau wani, zan sameku a gida."
"Shiga." Yace yana nuna min ciki, shiga nayi Hajiya ta miko hannu ta karbi yar jaririyar.
"Kiyi hakuri kinji?" Tace min tana kallo na. Murmushi kawai nayi muka dauki hanya ba tare da sanin takamaimai inda muka dosa ba.
Unguwa ce tsaf tsaf babu cinkoso balle hayaniya, a kofar wani dan madaidacin gida naga mun tsaya, ni na fara sauka sannan ta fito,
"Dauko kayan Aminatu."
Kayan na kwaso ta bude yar karamar kofar jikin gate din muka doshi cikin gidan, da wata dattijuwar mata muka fara haduwa tana zaune gaban fanfo kayan wanke-wanke ne a gabanta tana yi, da murnar ta ta taso ta tare mu,
"Sannu da dawowa Hajiya."
"Yawwa Altine, ana ta aikin ne?"
"Wallahi, jiya mukayi ta zuba ido shiru har dare sannan Ramlah ta hakura ta kwanta."
"Wallahi kam."
"Sannu." Tace tana kallo na, gaishe ta nayi ta amsa sannan muka dunguma zuwa cikin falon, ko ina a share tsaf na samu gefe na rakube ina jin su suna cigaba da hirar tasu inda na fuskanci ita Altinen me aikin Hajiya ce, mika mata kayana tayi tace ta shigar min dasu dakin Ramlah.
"Jeki ki huta Aminatu, nasan kin gaji."
Tashi nayi nabi bayan ta, a gefe ta ajiye kayan, dakin a hargitse duk an barbaza kaya, tattarewa ta hau yi tana mitar halin wadda aka kira da Ramlah ɗin, tana gamawa ta fita, da sauri na haye gadon na kwanta dan ji nake kamar zan fadi, anya ma ina da isheshen jini a jikina ma kuwa? Na tambaya kaina ina karewa ko ina na jikina kallo, na dashe nayi fari tas ga wani matsanancin ciwon kai da jiri da nake ji. Shiru nayi ina ayyana yadda zamu kwashe da Anas, dan da alama mutum ne mai zafi, zan yi kokarin sanar dasu gaskiyar labari na, dan na samu na makale kafin zuwa gaba naga yadda Allah zaiyi dani.
Kukan da naji yana doso dakin yasa na tashi na zauna sosai, Hajiya ce ta shigo rik'e da yarinyar dake faman tsala kuka, zuciyata ce ta tsinke da tsananin tausayin ta, bata da damuwar komai sai ta cikin ta, yunwar dake damun ta itace ta hanata sakat, waya take da alama da Anas ɗin take yi, kafin ta ajiye yana mika min ita.
"Karbe ta ki sake gwada mata, kafin a kawo mata madarar da tausayi sosai wallahi."
"Toh."
Nace na karbeta, fita tayi ta jawo mana kofar, yadda zan fara bata ne ma sam ban iya ba, kici-kici nake tayi na kasa, gashi sai kara karfin kukan nata take, duk na rikice na rude, a haka ta sake shigowa ta tarar dani, hannun ta dauke da bakar leda, da sauri ta ƙaraso tana ajiye kayan kafin ta karɓe ta,
"Baki iya bata ba Aminatu? Na shige su, ai na zata kin iya, shiririta kenan."
Sauke kaina kasa nayi, ta cigaba da jijjiga ta, shigowar Altine da tea flask yasa ta ajiye ta ta shiga hada mata madarar a sabuwar feeding bottle din da aka siyo tare da Madarar, ina zaune ina kallo har ta gama haɗawa sannan ta shiga bata, da sauri da sauri take sha gwanin tausayi, kwalla na share a ido na ta gefe ina godiya da Allah daya kawo min mutanen nan a lokacin da nake tsananin bukatar wani a kusa dani.
Ana gama bata ta koma bacci, kwantar da ita tayi, tana dariyar yadda take fitar da numfashi a hankali.
Kura mata ido nayi bayan fitar su daga dakin, murmushi na saki a hankali na kai hannu na saman kanta ina jin sabuwar soyayyar ta na bin dukkanin jikina.
Ruwan wanka Altine ta haɗa min, ta kawo dakin, ganyen darbejiya naga ana shigowa dashi dakin, kuka yazo min, kukan farin ciki, bansan da wanne bakin zan gode wa wannan matar ba, da kanta ta shigo ta saka ni a gaba tayi min wankan, wankan jegon da iyaye keyi ma kowacce yarsu, a lokacin da nake tunanin na rasa wannan gatan, a lokacin Allah ya aiko min da ita rayuwa ta. Wankan da nayi ba karamin jin dadin jikina nayi ba, ina gama shiryawa aka aikon da abinci lafiyayye irin wanda ya kamata mutumin da yake irin yanayin da nake ciki yaci, sosai naci abincin dan rabona daci tun kafin komai ya sake canja min, dadin dadawar ta tabbatar min da idan ban ci abincin ba, jaririyar tawa ba zata samu ruwan nono ba, hakan ya kara min kaimi wajen ganin naci abincin sosai.
Ina gamawa nabi lafiyar katifar, sam bana son nayi tunanin maganganun Inno, dan ba karamin hargitsa min lissafi suke ba, na kasa gasgata abinda ta sanar min, duk da na riga nasan ba zata taba min karya ba, amma kuma zuciya ta sam ta kasa aminta da maganganun.
Dawowar shi naji yo muryar sa a falon, gabana ne ya fadi da tunanin yadda zamu kwashe dashi, ina nan kwance aka turo kofar, Hajiya ce a gaba sai shi a bayanta, yar karamar kujerar dake dakin yayi wa kansa mazauni, inda Hajiyar ta zauna a gefen gadon tana kallon jaririyar
"Kinga ashe baiwar Allah yunwa ce, gashi yanzu sai baccin ta take."
"Uhum." Nace ina kokarin daidaita zama na saboda yadda naji duk na kasa sakewa.
"Ya jikin?" Ya jeho min tambayar,
"Da sauki."
"Good."
"Kamar yadda kika ganmu, wannan mahaifiya ta ce, sai kanwata Ramlah, sai Altine dake taimakawa Hajiya da yan aike aiken gida, wadda ta zama kamar ma yar uwa ta jini. Babu bukatar dogon bayani mu, mu kadai ta haifa, mahaifin mu ya rasu, sai dangin sa dake Katsina inda muka hadu dake munje wata gaisuwar rashin da akayi, dangin Hajiya duk yan Kano ne, yan karamar hukumar Kibiya, kuma yawancin su suna chan. Ina aiki da federal mortgage bank, in da kanwata take matakin farko a jami'ar northwest."
"Haduwar mu wani iko ne na Ubangiji, duk da haka, ina so ki sanar damu gaskiyar abinda ya dangance ki daya dace muji, ki sani bana bukatar komai sai gaskiya."
Share hawayen dake faman bin fuskata nayi tun lokacin daya fara magana, a nutse na shiga sanar dasu rayuwa ta. Duk da ba komai na sanar musu ba, amma nayi kokarin sanar dasu abinda ya dace su sani kamar yadda ya nema.
Ina kallon yadda yake girgiza kansa, Hajiya kuwa kuka ta saka cike da tausayi na, ina kaiwa karshe ta taso da sauri ta rungume ni.
"Baa kyauta miki ba Aminatu, ba'a kyauta miki ba."
Shine kawai abinda take ta nanatawa, mik'ewa yayi tsam ya iso gaban gadon, idanun sa cikin nawa, yasa hannu ya dauke ta, murmushi yayi min tare da girgiza min kai alamun nayi shiru.
"Wanne suna za'a sa mata?"
Ya fada yana tsura min ido, bance komai ba, na maida kaina kasa ina share hawayen fuskata hade da yiwa Allah godiya, sake maimaita wa yayi a karo na biyu, a hankali na furta
"Duk sunan da ka sa mata yayi."
Murmushi naga ya sake yi, sannan ya kara bakin sa a kunnen ta yayi mata huduba, dagowa yayi yana sauke ta a saman gadon kafin ya kalle Hajiya
"Na sa mata Fatima."
****
Har suka isa kauyen na Shagari babu wata magana data hada su, Allah Allah Farouk yake su isa gidan. Suna isa yayi saurin fitowa ba tare da ya jira Ja'afar ya gama daidaita tsayuwar motar ba, cikin zauren gidan ya shiga yayi sallama da d'an karfi dan babu yaron da zai aika.
Inno na zaune taji sallamar sa, gabanta ne ya fadi ta mike da sauri, idan har ba gizo kunnenta yake mata ba, toh tabbas muryar sa ce, idan kuwa haka ne akwai gagarumar matsala. Sake sallamar yayi hakan ya sa ta kara tabbatar da shi din ne, da sauri ta ciri mayafin ta a saman igiya tayo zauren a rikice.
Zagaye yake a cikin zauren ya kasa tsayawa waje daya, da sauri ya kalli hanyar shiga gidan jin takun tafiya, gaba daya tunanin sa ya tafi akan itace, bayyanar Inno a gaban sa yasa ya dan ji faduwar gaba, yanayin fuskar ta ya nuna akwai matsala, a gajarce ya gaishe ta, ta amsa kai tsaye tana gyara tsaiwar ta.
"Dan Aallah ko zan iya ganinta? Duk da nasan ba lallai ta saurare ni ba, amma ina bukatar ganinta dan Allah."
"Me yasa sai yanzu kake dawowa? Me yasa sai da lokaci ya kure, bayan kayi min alƙawarin zama da ita komai rintse, tabbas dawowar ka a wannan lokaci Farouk bata da amfani."
"Nasan ni mai laifi ne, amma ina da uzuri, ina fatan idan mukayi magana da ita zata fuskance ni."
"Ka makara Farouk, Aminatu ta tafi, bansan inda take ba, bansan ina za'a ganta ba, ya zanyi? Na jira ka, tsawon lokaci baka dawo ba."
A wani irin yanayi ya kalle ta, kansa ya shiga juyawa, wani irin jiri ne ya kwashe shi, yayi taga taga zai fadi, Ja'afar yayi saurin tare shi, da karfin sa ya mike, ya kwace daga rikon da Ja'afar din yayi masa, kallon tsana da kiyayya yake bin ta dashi kafin ya nuna ta da hannu yace
"Me tayi miki da kika watsa rayuwar ta haka? Wanne irin rashin imani ne wannan? Baki san inda take ba, me hakan ke nufi?"
"Bani da zabi ne, zaman ta anan na nufin fadawarta mugun hannu."
"Yanzu kika san a hannun da take? Eh?"
"Ban sani ba."
"Toh wallahi babu wanda zan kyale, bayan sanin alakar dake tsakanin ku, babu abinda zan tsaya jira ko kunya, idan har zaki iya rufe ido, ki koreta a halin da take ciki, wallahi ba zan yi kasa a guiwa ba wajen ganin na bi mata hakkin ta."
"Ka saurare ni, banyi hakan don na cuce ta ba, bani da kowa da zai iya tsayamin, Harira ta wuce inda kake tunani, ya zanyi da raina? Kuskure daya tak, ya zama silar rugujewar dukkan farin ciki na."
Sosai ya koma mata kamar bashi ba, maganganu ya shiga fada mata duk wadda tazo bakin sa, cikin tsananin fushi da bacin rai, da sauri ya juya ya fita, ya fada mota ya bar wajen ba tare da yabi takan Ja'afar da ya biyo shi yana kwala masa kira ba, zauren ya dawo ya tsaya kawai yana tunanin inda Farouk din zashi,
"Dama nasan za'a yi haka, amma ya zanyi da rayuwa ta?"
"Yaushe ta tafi?" Ja'afar ya tambaye ta
"Shekaran jiya."
Girgiza kai kawai yayi, yace Allah ya kyauta.
A kafa ya shiga takawa, ya nufin gidan Bature, a hanya yaci karo da motar yan sanda, sai Farouk dake gaban su, da sauri yasa hannu ya tsaida shi, tsayawa yayi ya bude masa motar ya shiga suka cigaba da tafiya
"Ya Farouk, kana ganin hakan shine daidai? Karka manta wacece a wajen ta fa."
"Na fika sani, ai na fada mata, idan wani abu ya sameta, wallahi bazan kyale ba, wanchan karon taci darajar Aminatun bata sani ba, ba kuma naso na data mata hankali, amma yanzu sai inda karfi na ya tsaya."
Duk da ja'afar be gane inda maganganun suka dosa ba, amma sai yayi shiru ba tare da ya sake cewa komai ba, suna isa gidan yan sandan suka fito, babu wani bata lokaci suka shiga suka fito da Inno, cikin kankanin lokaci kofar gidan ya dinke da mutane, yan kallo, Garbati na zaune a majalisar su labarin ya isar musu, da sauri sauri suka ƙaraso wajen, gaban sa ne ya fadi ganin Farouk ne, boya ya hau kokarin yi a bayan mutane be san tun zuwan sa wajen ya ganshi ba, yana kokarin guduwa yaji an chapke shi, turje turje ya fara yi, yana ihu ganin haka yasa kowa ya hau darewa, suka ingiza keyar shi suka sashi a bayan mota, Inno kasa dagowa tayi saboda tsananin kunya, kuka take har Karime ta ƙaraso wajen dauke da goyon Saddiku tana kuka, ganin Farouk yasa tayi wajen sa da sauri tana rokon sa, hakuri kawai ya bata ya basu umarnin su wuce zuwa kauyen da Harira take. Motar ya fada suka bi bayan su yana jin yau yayi abu na farko daya kamata ace yayi shi tun tsawon shekarun da suka wuce.
Hajiya Inno za'a yi kwanan cell😂😂
#Manage 🚴🚴🚴🚴🚴🤫🤲: Hansatu R
19
ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*
07067124863
*Ko kuma*
09032345899
*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽
https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo
★★★★
"Sunana Anas?" Hajiya ta tambaya cikin farin ciki, daga mata kai yayi
"Sunan ki nasa mata Hajiya, ina fatan tayi gadon kyawun halin kirki da nagartarki."
"Wai kin amince Aminatu?" Hajiyan ta juyo tana kallo na, da sauri na daga kaina sama, cikin wani yanayi na furta
"Bani da ja akai, kin chanchanci fiye da haka."
"Allah yayi muku albarka." Tace cikin farin ciki mara misaltuwa.
Gefe ya koma rike da Fatima, ya zauna yana jujjuyata a hannun sa, daidai lokacin ta bude idon ta, hade da sakin kuka, da sauri ya mike
"Iman ta tashi, kinga bakinta Hajiya?"
Yace yana mika mata ita, dariya suka saka baki daya kafin ta miko min ita tana faɗin, maza karbe ki sake gwada mata mu gani." Da sauri na sauke kaina kasa saboda kunyar data kamani, juyawa yayi da sauri ya bar dakin, sai a sannan Hajiya ya ankara, dariya kawai tayi ta cigaba da gwada min yadda zanyi, cikin sa'a kuwa aka samu sai dai babu yawa ga wani irin zafi, yarfe hannu na nake kawai ina cije baki Hajiya namun dariya.
Bayan ta koma bacci na kwantar da ita ina kwanciya a gefen ta, bacci ne ya dauke ni ba tare da na shirya ba.
Na jima sosai ina baccin har sai da mai dakin ta dawo, motsin tane ya data ni, muna hada ido ta sakar min murmushi, murmushi nayi mata kamin na mike ina gyara zama na.
"Sannu da tashi."
"Yawwa." Nace