Showing 9001 words to 12000 words out of 112633 words

Chapter 4 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt

07 Aug 2025

7429

yayi ya sauka cikin nata, wani irin abu yaji ya taba shi, wanda be taba jin irin sa ba, raunin da ya gani a cikin idon ta, yarintar ta da tsantsar tausayin ta suka hadu. Idan har yaji daidai abinda mai gari ya fada, yana nufin aura wa Garbati ita kenan, auren da yake nufin lalacewar rayuwarta har abadah, auren da yake nufin yanker war duk wani jin dadi na rayuwar ta, auren da yake nufin rayuwa da mutum wanda bashi da maraba da dabba, dabbar ma mafi kaskanci acikin dabbobi. Kasa dagowa yayi ya rasa me yake masa dad'i, yana jin sanda Maigari ya kira sunanta, yana jin lokacin da ya tambaye ta, kukan ta ya kara karfi, be san yaushe ba, be san yaya ba, kawai ya samu kansa da amsawa a maimakon ta tun kafin ta samu damar yin magana. Da wani irin karfi Daddy ya riko shi, ya shak'e shi, kakari ya fara kamar wanda yake shirin mutuwa cikin sauri Baba ya shiga tsakani. Yayi kokarin bangare shi daga rikon da yayi masa,

"Alhaji kar kayi mishi illah."
Ya fada cikin tashin hankali ganin yadda idon yaron ya kakkafe

"Barni na kashe shi, ya cancanci haka, ko ma fiye da hakan, barni dan Allah, harbe shi zanyi kowa ya huta." Ya sake riƙe shi sosai, bugu ya fara kai masa ta ko ina, tun Farouk na kokarin kwatar kansa har jikin sa ya saki ya shiga fitar da jini ta ko ina.

Lawan da sauran ne suka shiga tsakani, ganin haka yasa Garbati da Ilu sulale wa su bar dakin suna fita suka ci karo da sojoji, a darare suka gifta su suka bar asibitin da sauri.

Ba karamin duka yayi masa ba, da kyar suka kwace su, duk da haka sai daya hankad'a shi da karfi kansa ya fashe, Amal ce tayi saurin isa wajen sa tana kuka taa dago shi.

Haki kawai Daddy yake, kamar wanda ya shiga filin daga, cikin tsananin bacin rai ya nuna shi da hannu yana kallan su Maigari.

"Maigari, Malam da sauran wanda suke wajen nan, ku zama shaida, ga shi nan, duk hukuncin da kuka yanke akansa bani da ja, kuyi masa duk abinda kuka ga dama babu ruwana, karku duba girma na, arziki na ko khakhi na, kuyi masa hukuncin daya dace daidai dashi."

Ya dora...

"Sai dai ina neman alfarmar kowanne hukunci za'a yanke ya zama cikin kwana biyu, dan zan koma in da na fito."

Juyawa yayi ya nufi kofar fita da sauri yana jin ba'a taba bata mishi rai irin na yau ba. Daya bayan daya suke dinga zamewa suna barin dakin ya rage sai su Inno kawai. Tashi tayi ta dago shi tana kallon fuskar sa

"Baka aikata abinda ake zargin ka dashi ba, amma me yasa ka dauki laifi me girma ka dora akan ka?"

Ta tambaya tana karantar sa.

Mik'ewa yayi yana goge bakin sa yana kallonta

"Bansani ba, bansan dalili ba. Ina ganin hakan da nayi shine kawai mafita."

Juyawa yayi ya bar dakin Yana rangaji, Amal ta bishi da sauri tana kiran sa.

Kuka na fashe dashi, Inno ta harare ni tana zama a gefe na

"Kukan uban me kike?"

"Inno kinga fa kuka yake, duk kuma jini a jikin sa, yana da kirki sosai."

"Toh sai akayi uban me? Ke yanzu karamar ki dake kinsan wani yana kuka, baki ji maganar da mai gari yayi ba, idan na yarda akayi miki aure idan ranar da nake jira tazo nayi yaya kenan?"

"Na'am?" Na tambaya cikin rashin gane abinda take nufi

"Manta kawai, abu daya nake so dake, idan aka tambaye ki kice ba zaki auri kowa ba, babu inda zaki matsa daga nan sai ranar da Allah ya yanke miki wahalar nan."

Gid'a mata kai nayi ina share hawayen dake faman kaikawo a fuskata kamar an kunna fanfo.

Tashi nayi ta taimaka min na wanke fuska ta, ina zama ya shigo fuskar sa anyi dressing ya dire kayan tea ba tare da yayi magana ba ya juya ya sake fita.

***
A hargitse ya shiga gidan, Dada na zaune a falo tana jira shigowar sa, ganin yanayin sa yasa tasan komai ya ɓaci, be zauna ba, ya shiga kwala wa su Ja'afar kira, sai daya tara su duka sannan ya hau fada, sosai yayi musu fada sannan yace duk su shirya kaya zasu bar garin a ranar. Duk suka amsa da toh sannan ya sallame su. Zama yayi cikin kujerar falon yana zare butiran din hannun sa.

"Dadah yaron nan ya amsa laifin sa, dan yau dama ka haife shi ne baka haifi halin sa ba."

"Yanzu menene abin yi? Kana nufin shi baban nawa ya amsa laifin?"

"Ya amsa har ma sun yanke hukuncin bashi auren ta."

Da sauri ta tashi

"Aure kuma? Dududu Baban nawa nawa yake? Karka manta alƙawarin da kayi wa Marigayi."

"Toh ya za'a yi Dadah, tun da yasan ya bata wa yar karamar yarinya rayuwa ai gwara a aura masa ita kawai kowa ya huta, idan yaso sai ya hakura da karatun nasa su zauna anan ɗin tunda irin rayuwar da ya zaba ma kansa kenan."

"Amma ka tabbata shi ya aikata?"

"Nima da ina ta tunanin hakan, amma daga baya daya amince da laifin nasa kinga ai babu maganar tantama, ya aikata din"

"Kai wannan abu beyi dadi ba, amma ita yarinyar fa? Bata fadi kowa ba?"

"Kin ganta dai Dadah, karama ce sosai dan ko Amal ta fita girma da cika ido, ga kuma kauyanci da rashin wayewa, bayan haka ba'a kai ga tambayar yarinyar ba ya amsa laifin sa, kinga ai babu bukatar kuma wani dogon bincike da dai be amsa bane."

"Toh Allah ya sauwake, amma sam banji dadin abin nan ba, amma dai ƙaddara ce dan sam ba haka halin babana yake ba kai ma ka sani, bansan dai me ya faru ba, Allah ya kara kiyaye wa."

"Amin ya ALLAH."

"Bari na shiga ciki, in sha Allah da an gama komai jibi zamu wuce baki daya, su yaran suyi gaba yau, nima ina da ayyukan yi da yawa, dalilin admission din farouk din ne ya shigo dani garin wallahi."

****
Tafiya yake a kasa bayan ya bawa driver umarnin ya maida Amal gida, be san ina yake saka ƙafarsa ba, ya dai san kawai yana tafiya ne akan kasa, sai dai kafatanin tunanin sa ya tafi ne akan abinda ya faru a yan awannin da basu wuce ashirin ba, gaba daya rayuwar sa ta chanja, ya rasa duk wani girma da kima a idon mahaifin sa, haka Allah yake ƙaddara wa bawa ƙaddarar sa, ba tare da ya shirya ma hakan ko yayi tunanin hakan zai taba kasancewa dashi ba.

Tsaiwar babur a gaban sa ce yasa ya dakata yana kallon na kai, Garbati ke da Ilu, cikin kazamar shiga irin ta yan Iskan kauye, sigari Garbati ya busa masa a fuska yana dariya.

"Ango ango."

"Lafiya?"

" Ita ce ta kawo hakan, ka dai ga kadan daga aikin Garbati ko?"

"Bani da lokacin tsayawa magana daku, kamar yadda ban dauke ku a cikin jerin mutane masu hankali ba."

Da haka ya rabe ta gefen su ya wuce, yana jin Garbati na kutuntuma masa ashar, be bi ta kai ba, burin sa kawai ya isa wajen da babu kowa.
   Kansa ya haɗa da gwuiwar sa, ba zan iya fadar yanayin da yake ciki ba, zuciyar sa ta yi nauyi, ta cunkushe kamar zata budo kirjin sa ta fito, so yake yayi kuka ko zai samu sauki, sai dai babu ko digon hawaye sai na zuci da ya ka faman yi. Da fari ya so ya tabbatar da gaskiyar sa, ko dan irinsu Garbati masu halin dabbobi, sai dai furucin auren da yaji ne ya rusa komai, ba zai iya barin yarinya karama Kamar Amal ta rayu da Garbati ba, rayuwa irin ta aure me cike da tarin matsaloli, dalilin hakan yasa yayi ma kansa mugun dauri, daurin da yake tunanin har karshen rayuwar sa zai cigaba da bibiyar sa.
    Ya jima sosai a wajen, ba zai iya lissafa adadin awowin daya bata ba, ya dai mike ne kawai da niyyar zuwa gidan ko me zai faru ya faru. Sai a lokacin ya lura da irin nisan tafiyar da yayi. Har ya karasa gidan be bar fargabar haduwa da Daddy ba, ya san shi sarai yasan abin da zai iya aikatawa akan shi, abun mafi tsoro a tattare dashi shine bakin sa, baya son wata kalma ta muzantawa ta fito daga bakin sa, ba zai iya daukar hakan ba sam.
   Tura gate din yayi yaji shi a bude, a nutse ya tura kansa cikin gidan bakin sa dauke da addua, jami'an tsaron dake zube birjik a gidan ya fara cin karo dasu, duk suka zuba masa ido suna kallon sa, dauke kansa yayi ya haura kofar da zata sadaka da falon gidan. A dan tsorace ya tura kofar yana tarrradin abinda zai tarar, cikin tsawa aka dakatar dashi.

"Tsaya anan!" Da sauri ya tsaya yana maida hannayen sa baya kamar me shirin arcewa.

"John!" Daddy ya bud'e murya ya kwala kira, a guje ya shigo ya tsaya gaban sa.

"Lock him up."

Ya fada yana nuna masa Farouk dake tsaye kamar an dasa shi, yasan dama hakan zata faru.

"Yes sir!" Ya amsa da sauri ya chakumi wuyan Farouk kamar kayan wanki. Tirjiya ya fara yi yana magiya

"Daddy please ka saurare ni, dan Allah Daddy."

Ko gezau beyi ba, sai ma hade rai da ya sake yi yana wa John mugun kallo

"Me kake jira ne?"

Da sauri ya karasa janshi, ya fita dashi.

Tsaki Daddy ya ja ya tashi ya bar falon baki daya.


DAURIN GORO😢😢😥😥😓

ZAFAFA BIYAR

KAUNAR MU: MAMUH GEE

ALKAWARIN ALLAH; HUGUMA

GUDU DA WAIWAYE: BILLYN ABDUL

DAURIN GORO:HAFSAT RANO.

IGIYAR ZATO: MISS XOXO

LITTAFI DAYA 200
BIYU 300
UKU 400
HUDU 450
BIYAR 500

*_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_*

2260792279
_MARYAM SANI_
_ZENITHBANK_

saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇
*07067124863*

*_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇

*09032345899*

_Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_
: *DG*

*ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*

07067124863

*Ko kuma*

09032345899

*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽

https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo

    ©️Rano
                    (6)

***
Ina kwance ina ta kallon inno tana hada kan abubuwa da suke dakin, Nura ne ya shigo ya karba sannan ya fita dasu, kamani tayi ta lulluba min wani babban Mayafi muka fito, a hankali nake tafiya cikin wani yanayi mara dadi da ba zan iya tantancewa ba, har muka isa gaban motar da ban taba ganin irin ta ba, soja ne ya bude mana gidan baya muka shiga, ya rufe sannan muka dauke hanyar kauyen mu, kasancewar motar rufe take ruf da bakin gilashi hakan ya hana mutanen gari kallon mu, sai dai na lura duk in da muka bi sai an bimu da kallo. A kofar gida ya ajiye mu, Inno ta sake jan mayafin ta kare min fuska ta sosai ta fito dani, mata ne a tsaitsaye kowacce ta fito jin mota, da sauri Inno ta ja hannu na muka shige gida tana hararar su. Muna shiga matan gidan mu suka taso, kowa yana min sannu wadda ta kasance da biyu, daki Inno ta tura ni ta dawo wajen su tana amsa gaisuwar da suke min ta munafurci da gulma. Sun dan jima ina jiyo sautin karadin su, har suka watse, daga nan bacci ya dauke ni, ban sake sanin me yake faruwa ba.

A bangaren gidan Maigari kuwa ya aikata aka kirawo su Baba da Daddy. Inno najin hakan ta rufo ni a daki ta yafa mayafinta ta bisu, Baba be isa ya hanata ba sai dai babu yadda ya iya. Suna zuwa Daddy ma yana zuwa cikin shigar fararen kaya manya, cikin girmamawa suka gaisa gaba daya, Inno na makale a gefe tana jiran taji dalilin kiran.

"Abin da yasa na tara ku anan..."

Maigari ya soma

"Maganar da mukayi akan yaran nan, da kuma alfarmar da shi Alhaji ya nema ta a yi koma a kwana biyu, ina ganin abu daya da zamuyi wa yarmu shine aure, dan babu wani mutum a kaf kauyen nan da zai karbi auren ta, dan hakan ta taɓa faruwa a baya, a karshe saboda yadda yaran gari suka sako ita yarinyar a gaba yasa ta aikata abinda duk beyi mana dadi ba, shiyasa muka yanke hukuncin idan hakan ta sake faruwa, toh duk wanda aka tabbatar da ya aikata hakan xa'a aura masa yarinyar."

"Gaskiya ne." Duk suka amsa cikin gamsuwa.

"Toh yanzu Alhaji idan ka shirya, sai a gabatar da komai a nan."

"A shirye nake ranka ya dade, duk abinda ake bukata sai a sanar dani."

"Gaskiya ina da ja wallahi." Maganar Inno ta katse su,

"Ina dah ja maigari, ya kamata ace a matsayi na na uwar yar nan anyi shawara dani, amma ace kawai a yanke hukuncin yi mata aure babu izini na, yarinyar da dududu nawa take, gaskiya ni ban yarda ba."

Da tsananin mamaki suke kallon ta, babu uwa daya a kauyen nan kaf da irin hakan zata faru har ta tsaya jayayya, kamar bata san kalar wulakancin da yarinyar zata fuskanta ba?

"Menene dalilin ki, na kin abinda muka zo dashi?" Maigari ya wurgo mata tambayar

"Allah ya taimake ka, ni dai kawai bana so ne, ban yarda ayi mata aure yanzu ba, batun maganar mutane kuwa suyi tayi, zan san yadda zan ɓullo musu."

"Kaji abinda maidakin ka tace Malam Ayubah, yar nan dai yarku ce, ku kuka haife ta, duk soyayyar da zamu nuna mata ba kamar wadda kuke yi mata ba, menene ra'ayin ka akai?"

"Ranka ya dade ni dai na amince da maganar auren, ina ganin hakan shine kawai sauki."

Ya fada ba tare da ya kalli bangaren Inno ba, dan yasan idan ya yarda suka hada ido ba zata taba barin sa ya aikata zabin zuciyar sa ba.

"Sauran yan uwan yarinyar, shin kun amince ko kuwa?"

"Mun amince."

"Masha Allah, toh ke sai kiyi hakuri, dama aure a hannun Iyayen maza yake."

"Alhaji Bismillah."

Matsowa Daddy ya sake yi ya zura hannu a aljihun sa ya ciro kudi, alama yayi wa da driver sa ya fito da sauran kayan dake booth ɗin, ganin haka yasa Inno fashewa da kuka ta yi saurin fadawa gidan mai gari. Bisa ga shaidu da wakilan kowanne bangare aka shiga gabatar da daurin auren da ya zamo tsanin farko na duk wata rayuwa da Aminatu zata taka a gaba.

***
Cikin dare ta kasa bacci, babu abinda take sai juyi, bata san yadda zatayi ba, idan har auren nan na nufin katanga da cikar burin ta, zata iya komai akai, duk da babu wanda yasan abinda ya faru sai mutane uku kachal a duniyar nan, amma ba zata bari damar ta ta karshe ta kwace mata ba, wanda auren nan yana nufin rugujewar komai. Har akayi asubah tana bitar abu daya, bata jira gari ya gama haske ba, ta tashi Aminatu ta bata kunu, ta ballo mata magungunan ta ta bata sannan ta dauki yar karamar purse din ta da mayafin ta, ta fice daga gidan. Tafiya me nisan gaske tsakanin kauyen nasu da wanda ke makwabtaka dasu, sanda ta isa gari yayi haske sosai, mutum daya jallin jal data san sirrin ta, sirrin da yake shirin zama tarihi idan har ta aminta da wannan auren, wajen ta tazo, dan samun mafita. Da sallama ta shiga gidan duk matan gidan suka kalle ta cike da mamakin wannan zuwan nata da sassafe haka, gaishe su tayi a tsaitsaye bata damu da irin kallon da suke mata ba ta fada dakin wadda tazo wajen ta.

"Akwai matsala kenan." Ta fada tana kallon ta har ta ƙaraso ciki.

"Ita ce ta taso ni, ina cikin matsala wallahi harira, bansan ya zanyi ba."

"Lallai ai naga alama, me ya faru hala? Ko dai wani abun ya samu yar mutane ne?"

"Kusan haka." Ta cire mayafin ta ta zauna gefen gadon, sannan ta shiga bata labarin komai. Ajiyar zuciya Harira ta sauke bayan ta gama sauraron ta

"Kema dai Inno kinyi sakaci, bayan kinsan dalilinmu da kudurinmu a nan gaba, amma kikayi sakaci da yarinyar mutane har wannan abin ya faru da ita, kina ganin zasu yarda ne su kyale mu duk ranar da gaskiya ya fito? Bayan irin rikon da sukayi wa namu d'an."

"Duk nayi dana sani wallahi, zuciya ce ta d'ebe ni, amma yanzu na gano kuskure na, ki taymaka nidai da shawarar yadda za'a yi da auren nan, idan yaran nan ya dauke ta suka bar kauyen nan kina ganin zai sake dawowa da ita ne?"

"Gaskiya dai, gashi kince an riga an daura auren."

"An daura wallahi."

"Toh mafita daya ce gaskiya idan zaki iya..."

"Zanyi koma menene idan akan d'ana ne."

Murmushi harira tayi ta matso kusa da ita.


***
Kamar kayan wanki haka suka fito dashi, a kwana biyun da yayi duk yai baki ya rame sosai kamar ba shi ba, kauda kai Daddy yayi daga kallon sa, sun riga sun fito a shirye zasu tafi, Dada kawai za'a bari itama dan tace babu inda zata ne, gashi ba zai iya musu da ita ba. Su Ja'afar kuwa tuni suka tsufa a can sai dai Daddy ya ja musu kunne akan maganar, baya son kowa yaji har sai ya dawo da kansa zai sanar musu. Atm card ya ciro ya wurga masa, sai mukullayen gidan.

"Gashi nan, tun da kalar rayuwar daka zaba ma kanka kenan."

Da sauri ya kalli daddyn, sanin hakan me yake nufi ne yasa ya hau rokon sa

"Daddy dan Allah ka tsaya ka saurare ni, wallahi ban aikata abinda ake zargi na dashi ba."

Da wani mugun kallo ya dube shi

"Ni sa'an ka ne Farouk? Ko ka fara shaye-shayen ne dai da gaske?"

"Wallahi ban taba shan komai ba, ka saurare ni kadai nayi maka bayani, wallahi bani da laifin komai."

"You must be a fool, nace baka da hankali sam, idan har kana ganin zan tsaya sauraran ka bayan da kanka ba wani ya matsa bakin ka ba ka amsa laifin ka a gaban kowa, sannan yanzu kazo min da wani banzan zancen ka, toh kayi karya wallahi."

Riko ƙafafuwan sa yayi da sauri yana sake sakin kuka

"Wallahi ban aikata ba, bansan me ya hau kaina ba na amsa, dan Aallah Daddy kar kuyi min haka."

Buge hannun sa yayi ya janye ƙafarsa yana matsawa.

"Idan ka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login