Showing 18001 words to 21000 words out of 112633 words
Chapter 7 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt
zai iya aikata abinda Mummyn tace, ya kuma rasa dalilin sa na son kin amincewa bukatar ta. Shafa kansa ta shiga yi tana ayyana yadda komai yake tafiya.
"Babana..." Ta sake kiran sunan sa
"Kana son Aminatu ko.?" Da sauri ya dago kansa jin tambayar a bazata, abinda yake ta kokawa da zuciyar sa kenan, ya rasa dalilin da yasa yake jin yarinyar har cikin ransa, komai nata yana jin kamar an haɗe shi da rayuwar sa ne, yanzu da Mummy ta kawo zancen rabuwa sai yaji kamar zare wani abu me muhimmanci ne a cikin rayuwar sa. Be san me haka yake nufi ba, sai dai yana daukar ta a matsayin wata babbar ƙaddarar sa.
"Kana son ta ko?" Ta sake maimaitawa
"Nima ban sani ba Dadah, kawai ina jin tausayin ta ne, She's too young for that, sannan na mata plan na good future,."
"Shikenan, Ina da shawara, amma dole sai da taimakon mahaifiyar ta, kaga ni yanzu mahaifin ku ya matsa lallai sai na tafi saboda ciwon kafar nan tawa daya matsa min, da babu irin taimakon da ba zan baka ba, toh mahaifiyar ta ita kadai ce zata taimaka mana, wajen ganin mun samu abinda muke so."
"Ta yaya kenan Dadah?"
"Ka kai ta boarding school, ka damka amanar ta wajen mahaifiyar ta, ka sanar mata da kudurin ka nason ganin ta zama wani abu,nasan babu mahaifiyar da zata ki cigaban yar ta, kai kuma kaga sai ka dawo kayi wa mahaifiyar ka biyayya, kayi karatun ka, ka kara mallakar hankalin kanka, lokacin babu wanda zai fada maka yadda zaka yi da rayuwar ka, a lokacin sai ka dawo, ka cika burin ka."
Da sauri ya tashi ya rungume Dadah,
"Shisa nake sonki Granny, wallahi you are the best."
"Ja'iri." Tace tana kai masa duka
"Allah kuwa, gashi kin kawo solution cikin sauki, idan Daddy yaji labari sai nace masa makaranta na maida ita nima zan koma tawa, kinga ba zai ce komai ba."
Daga masa kai tayi tana murmushi.
Tashi yayi da karfi da kuzarin sa ba kamar dazun da ya shigo ba.
"Bari naje na sanar wa Mummy na amince da komai data ce, sai na fara shiri." Ya fada cike da farin ciki.
Fita yayi da sauri, a kofar dakin sukayi kicibis, basarwa tayi kamar bata gama jin komai ba tayi gaba ya bi bayan ta. Zama tai kawai ya shiga tsara mata zance.
"Mom na amince da bukatar ki, amma dan Allah karki yi mata komai, bata da laifin komai bata san komai ba, idan ma hukuncin ne ni zakiyi wa, amma yanzu zan rabu da ita, zan biki mu tafin idan hakan zai saki farin ciki."
Murmushi ta k'ak'alo wanda ya tsaya a iya saman fuskar ta tace
"Madallah da kai, ka kyautawa kanka, ka kyauta mata, sai ka fara shirin tafiya dan bazan tsaya bata lokaci ba."
"Kiyi gaba dan Allah, zan biyo bayan ki wallahi nayi Alk'awari, ki bari na dan karasa wani abu dana fara, ba zan dau lokaci ba."
Dan jim tayi tana tunanin amince wa, kamar tace a'ah sai kuma tayi wani tunani.
"Shikenan ni zan koma gobe, saura kaki abinda nace, kasan dai sauran ba sai na fada ba."
"In Sha Allah hakan ma ba zata faru ba."
"Jeka toh zan dan kwanta."
Fita yayi ya ja mata dakin, ya wuce dakin Aminatu, budewa yayi ya haye saman gadon nata yana lumshe ido, tunanin yadda komai ya fara ya shiga yi, daga san da ya fita daga gidan zuwa yanzu da yake shirin daukar wani babban tsani a rayuwar su. Yadda komai ya zama kamar a film haka ya dinga bin komai daki-daki. Murmushi yayi ya mirgina gefe yana sake duban komai daya zama mamallakin ta a dakin sai yan abubuwan Amal.
"My Destiny." Ya furta a hankali kamar me rada.
Eh dole ya kira ta da Destiny dan shine kadai sunan da yake ganin ya dace da ita, ƙaddarar sa ce, wadda a yanzu yake jin babu wani abu da zai iya raba shi da wannan ƙaddarar. Haka ya jima a dakin har gabanin magriba kafin ya mike a kasalance ya fada toilet din dake manne a dakin. Alwala yayi ya fito ya tsaya gaban mirror yana kallon fuskar sa.
"A yau shafin rayuwar mu zai fara Aminatu, daga yau ba zan sake barin wani abun ki, ko cutarwa yazo kusa dake ba, nayi alkawarin zame miki babban tsanin cikar farin cikin ki ko da kuwa hakan na nufin... Ko da kuwa hakan yankewar nawa."
A fili yayi maganar, sannan ya juya cike da karshashi ya bar dakin, sallah ya fara gabatarwa kafin ya nemi driver su tafi dauko ta.
***Ina zaune Inno na gefe tana ta aikin lissafin Kudi,yadda ta tsare ni a dakin gaba daya ya sa naji duk na gaji, tun Karime na tayani hira har itama ta gudu ta barni, gashi Inno ta kafa ta tsare ko ina, ina jin su suna wasa a tsakar gida kamar inyi ihu. Sai data gama ta tattare kan kudaden ta bude inda take ajiye wa tayi musu kyakkyawan boyo, har ta rufe sai kuma ta sake budewa da jawo wata jaka, bude cikin ta tayi ya dudduba sannan ta mayar ya rufe, ina kallon ta, ganin zata juyo yasa nayi saurin janye ido na, kallo na kuwa tayi tana juyawar.
"Bacci kike?" Ta tambaya tana matsowa
"Wasa nake son zuwa nayi nida su Karime dan Allah."
"Ba zaki ba." Kawai tace tasa kai ta bar dakin, kuka na saka cike da jin haushi, duk sai naji dama ban zo ba, kallon tagar dakin nayi naga duhu ya fara zuwa alamun dare kenan, Ya Farouk be zo ya tafi dani ba, duk sai naji ina son tafiya. Addu'a na fara yi Allah yasa yazo. Jin shiru shiru yasa na kwanta lamo ina jin haushin kowa, da haka bacci ya fara fisgata. Sama sama naji Inno na taba ni.
"Keeee...ke." Ta bubbuga min jiki na
A gigice na tashi
"Ya Farouk!" Na ambata ina mik'ewa, kallo na tayi kawai cike da mamaki.
"Na'am."
"Tashi maza ku wuce, kin hangame baki kina bacci ko tuwon baki ci ba."
Da sauri na mike, na yayimi mayafi na na fito, a kan tabarmar gidan daidai kofar Baba na hange shi, kallo na yayi nayi saurin jan kafata zan karasa wajen, ji nayi an riko ni, Inno ce ta banka min harara, da sauri nayi kasa da kaina.
"Ku wuce dare nayi." Tayi magana tana kallon bangaren su Baban. Tsam ya mike, yayi sallama da Baban sannan y fita, sai a sannan ta sakar min rankwashi a kai sannan tace su Karime su rakani.
"Uwar rawar kai."
Ta ambata tana jan tsaki. Daki ta fada cike da tunanin abin da zatayi. Ga maganar da yazo da ita wai makaranta zai sata ta kwana, kenan babu ranar da zai sake ta, bayan Harira ta karbi kudin ta tace ko wata biyu auren ba zai ba, sai gashi ana maganar wata biyar, idan tayi sake kuwa sai dai taji ana maganar suna. Dolen ta gobe ta koma taji in da aka kwana, ba zai yiwu ta zuba ido haka nan ba.
***Tun da muka fita bamu wuce gida ba, zakayi kawai muke tayi har bayan sallar isha'i, a mota suka barni suka yi sallah sannan ya je ya siyo mana tsire, sanda suka dawo har na fara bacci, tashi na yayi ya bani naman, ina ci na sake komawa na kwanta. Bansan yaushe muka koma gidan ba, ashe baya so mu hadu da Mummy ne shiyasa yayi ta jan komawar. Ban san me ya faru ba, nidai na farka naganni a dakin Dadah, tashi nayi na koma daki na na sake maida kai na cigaba da bacci na cikin kwanciyar hankali. Wajen bakwai da rabi na sake farkawa, sallah nayi na kwanta akan carpet din na cigaba da bacci. A hankali aka turo kofar, kallon gadon ya fara yi sannan ya hange ni a kasa. Banji takun tafiyar sa ba, kawai sai ji kayi an daga ni sama, dan karamin hijabin danayi sallah ya shiga kokarin cire min, na sake runtse ido na kamar me baccin gaske, ina ji a cire ya ajiye a gefe ya kwantar dani a gadon, ido na ne ya fara rawa alamun baccin karya ne. Murmushi yayi me sauti ya mintsine ni a hannu na
"Wayyo." Na bude ido na ina kokarin yin kuka
"Baccin karya ko?"
"Na gaske ne fa, kaine ka tashe ni."
"Umm amma idon ki yake ta rawa."
Dariya nayi na tura baki gaba, kallo na naga ya tsaya yanayi sosai, babu ko giftawa, hannu nasa naja gashin idon sa cika da tsokana.
"Ouch, kai kika min haka?" Ya tambaya yana taba idon nasa
"Abu zan cire maka fah."
"Karya ne."
"Da gaske." Na saka dariya ina matsawa. Riko ni yayi ya dawo dani kusa dashi.
"Kina son kiyi karatu ko?"
Da sauri na daga masa kai na
"Good... Zan saki a makaranta. Kina so?"
"Ina so wallahi." Na faɗa cike da murna
"Ok Tam, zan saki amma sai kinyi min alƙawarin zaki yi karatu sosai, sosai."
"Zanyi Allah."
"Good."
"Toh yaushe zaka sani, kuma aina makarantar take."
Shafa kansa yayi alamar tunani kafin yace
"Yau zan fara zuwa neman makarantar, in Sha Allah zanyi kokarin ganin an samu, duk da ma anci term daya amma hakan zaki shiga ciki, sai kiyi kokari sosai ki kamo su."
Murna na hau yi sosai kamar zanyi rawa, hannun sa ya rataye a saman kirjin sa yana kallo na, sauka nayi na jawo littafan da muke karatu dasu na fara jera su daya bayan daya. Be yi magana ba, sai murmushi kawai yake. Chan ya mike da sauri yana dafa kai, shaf yaso mantawa da tafiyar Mummy, abinda ma ya tashe shi da wurwuri kenan. Fita yayi yaja min kofar na cigaba da hada littafan cike da farin ciki.
***Har airport ya rakata, ba zatayi tafiyar mota ba wannan karon wai Lagos zata wuce akan wani kasuwancin ta, dole sai dai driver nata yabi bayan ta a mota ya koma gida, sanda suka isa ta kara jaddada masa alkawarin su, amsa mata yayi da toh da haka sukayi sallama. Be koma gidan ba, sai kawai ya bazama neman makarantar da zatayi daidai da Aminatun sa, makaranta yake so me kyau me tsada wadda zata taimaka mata kwarai wajen cikar burin ta, be damu da ko nawa za'a kashe ba, kudin da ya karba wajen Mummy da wanda yake dashi dana Daddy zasu ishe shi komai. Shi dai kawai ya samu ya tabbatar yayi wa dukkan su abinda suke so ba tare da ya fifita daya ba. Sai yamma sannan ya samu ya gama wasu abubuwan, duk da ba dukka ya gama ba amma yaci karfin komai, ya samu makarantar da tayi masa, har ma sun bashi damar ya kawo ta interview. A gajiye ya shiga gida, sallah kawai yayi yaci abinci ya sake shiryawa ya fita, gidan su ya wuce kai tsaye dan yana so su sake magana da mahaifiyar ta, a kafa ya taka a hankali kunnen sa sakale da earpiece suna magana da Ja'afar, har ya kusa karasawa gidan suna magana yana fada mishi yadda komai yake tafiya a gida. Daga nesa kadan yaga ta fito, cikin zulumi, kallo daya zakayi mata kasan ba a nutse take ba, da sauri ya kashe wayar yana kokarin tsaida ta yaga ta kara sauri, har zai juya sai kuma yayi tunanin ko babu lafiya, da sauri yabi bayan ta don tabbatar da babu wata matsala dan yanayin ta kawai ya nuna ba kalou ba. Tafiya take tayi hakan kuma shima be fasa bin nata ba, kamar daga sama ta hango Harira tana nufo ta, ja tayi ta tsaya jikin wata bishiya har ta ƙaraso, ganin haka yasa yayi kokarin juyawa, sai dai kalmar da yaji yasa shi dakatawa yana kokarin ganin yaji komai
"Wai Menene wannan kiran haka, kinga fa shiyasa kawai na yanke shawarar fitowa mu hadu a hanya dan yan gidan ma har sun fara zargin wani abu. " Hariran ta fada tana karasowa.
"Maganar Aminatu ce kin sani ai, fisabilillah bayan kin min alƙawarin ko wata biyu ba za'a yi ba zai sauta ta dawo gida, shiru kake ji gashi ana maganar watanni biyar, kinsan me hakan zai haifar nan gaba."
"Toh nidai bansan ina matsalar take ba, a gabanki na dauki kudin na bawa malam Tsalha da zauren gidan mu, ya tabbatar mana da ba za'a dau lokaci ba, toh ni bansan ina matsalar kuma take ba."
"Ni duk ba wannan ba, yanzu gaba daya bani da kwanciyar hankali wallahi, ni idan zai yiwu kawai ki nemo Hajiyar nan, ayi magana, ta in da ake hawa ta nan ake sauka, na fasa wallahi gwara su karbi yar su."
"Kamar ya? Abinda aka yi yarjejeniya, da zarar yaron nan ya kai matsayin da ake so ya kai din, sai ayi komai cikin sauki, amma yanzu daga farawa kice kin gaji, me ma akayi?"
"Ba zaki gane ba, dalilin baki san yadda yaya suke a zuciyar iyayensu ba, ni kam gaskiya ba zan iya ba, nayi nadamar abinda kika sani na aikata, yanzu zuwa zakiyi ki bani addireshin su, na je na same su a warware komai, na maida musu da yar su, tun kafin ranar da nadama ta ba zatayi min amfani ba."
Wani banzan kallo Harira tayi mata
"Amma dai kamar ba a hayyacin ki kike ba ko? Kar ki manta su waye mutanen da kike cewa zaki je, kina tunanin zasu tsaya sauraren ki? Bayan haka ma wacce hujja kike da ita da zaki nuna musu?"
"Jini ba karya bane Harira, wallahi suna ganin Aminatu ko ba'a fada ba zasu gane tasu ce, bayan haka kinsan dai ina da hoton mijin dana matar da muka dauka a saman file din asibitin su."
Dariya Harira ta saka sosai hadda tafa hannu
"Lallai Innaro, bansan ma kwata kwata tunanin ki baya ja ba sai yau, kinsan kuwa me kike shirin yi? Ina tabbatar miki da kina zuwa zasu kamaki su rufe ki, daga ke har zuri'ar ki kuwa babu wanda zai tsira."
"Ki fuskance ni, akwai matsala ne idan aka cigaba a haka, wadda zamu shiga sai tafi ya yanzu wallahi, idan muka samu yaron nan ya tsinke igiyar auren, sai mu tattara mu mayar musu da yar su, in yaso ita matar data tsara komai sai su kare chan, nidai Buri na d'ana ya dawo, rashin sa ya fara tabani. Nayi nadamar komai wallahi."
"Da kika gama kafa kanki da kudin da kika karba ba, ke fa wallahi san kanki yayi yawa, wato kinci moriyar ganga ko, toh bari kiji in fada miki gaskiyar magana, bansan in da suke ba, bansan aina za'a same su ba, rabona da su tun sanda muka rabu a asibiti, na yagi rabona, bayan wannan bansan komai akan su ba, ke wallahi ko sunan su ban sani ba, na sai tuna sanda Hajiyar take fada mana sunan da take so a sawa jaririyar, Aminatu MD. Daga wannan bansan komai akan su ba."
Wani irin kukan kura Inno tayi ta damki wuyan Harira, tuni kokawa ta rikice tsakanin su. Farouk dake tsaye a gefe yayi mutuwar tsaye tun sanda ya fara jin komai har zuwa sanda abubuwan suka dau zafi. Sosai maganar ta taɓa shi, wani irin mugun tausayin ta ya kara dirar masa fiye da wanda yake ji a baya, an cuci rayuwar ta, an raba ta da gatan ta, sai dai ya kasa gane dalilin daya sa suka aikata hakan, kenan babu sanin mahaifanta, toh wacece wannan data zabi rayuwar yarinyar ta lalace akan wani banzan burin ta mara tushe. Ya kasa gano hakan sai dai ya dau alwashin sai ya tabbatar da duk ya warware wannan daurin, ko da kuwa hakan na nufin....
Jin yadda suke abu kamar yara ne yasa shi magana cikin tsawa dan ba karamin bata masa rai sukayi ba.
"Ku dakata!"
A firgice suka juyo, wani irin bugawa kirjin Inno yayi, ta ɗora hannu a kanta kamar zata fasa ihu
"Yanzu kune kuke kiran kanku matsayin iyaye? Masu tarbiyyar yayan su? Tir daku wallahi."
"Faruku... Tsaya kaji, duk ba abinda kake tunani bane wallahi, yaudara ta akayi..." Katse ta yayi cikin tsananin bacin rai
"Babu sauran girmamawa ko mutuntawa a tsakanin mu. A dah ina miki kallon uwa ne, wadda tasan ciwon kanta dana ya'yan ta, ina ganin girman ki,a matsayin wadda ta kawo Aminatu duniya. Sai dai a yanzu babu ɗaya daga cikin wannan da zai sa na cigaba da ganin girman naki, ki sani a yau ni Farouk, ni zan zame wa Aminatu uwa, uba da dukkan gatan ta, har zuwa lokacin da zan hada ta da iyayen ta, babu kuma daya daga cikin ku da ya isa ya raba auren mu, ƙaddara ce ta haɗa mu, kuma babu wani mutum da ya isa ya raba."
Yana kaiwa nan ya juya a zafafe ya bar wajen, kwala masa kira take cike da tashin hankali, amma babu alamun zai tsaya balle ya saurare ta,kallo Harira tayi cike da tsana tace
"Sai kin yi dana sanin abinda kika aikata min."
Dariya ta saka harda tafa hannu tace
"Ko ke kiyi dana sani ba, uwar yan son zuciya ai nice maganin irin ku."
Ranoa: Hafsat Rano
(10)
***
Rai a bace ya shigo gidan, muka bishi da kallo nida Dada, be tanka ba, dan ko sallama a ciki ciki yayi ta yayi saurin wucewa dakin sa, yana zuwa ya maida mukullin kofar ya rufe, shiru mukayi baki daya babu wanda yayi motsi, ni a raina mamakin abinda ya sashi wannan tsananin fushin haka nake, ita kuwa Dadah ina kyautata zaton tasan tabbas koma menene akayi mishi ba karami bane. Har dare be fito ba, naje na buga dakin nasa yafi sau nawa baya budewa, duk na rasa ina zaka saka raina. Komawa nayi na shige cikin kujera nayi lamo na kasa ko cin abinci. Ina kwance na fara kuka kasa kasa, bansan dalilin kukan nawa ba, kila hakan na da na saba da yunwar da ke nukurkusata ne, jin karar bude dakin sa yasa nayi saurin tashi, shi dinne ya fito cikin shigar kananan kaya, fuskar sa tayi fayau kamar wanda yayi ciwo, tashi nayi na zauna sosai ban bar hawayen dake zuba a fuskata ba ya karasa sauka. Da sauri ya ƙaraso gareni ya zauna yana leka fuska ta
"Kuka?" Ya tambaya yana mamaki.
Daga masa kai nayi ina sake matsar kwallar.
"Menene?" Ya furta yana