Showing 78001 words to 81000 words out of 112633 words

Chapter 27 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt

07 Aug 2025

7417

matsalar idon ki amma kike ta kuka haka, me yasa?"

"Kamal dole nayi kuka, yanzu muje kawai zan maka bayanin komai ko a waya ne, Baba Altine na chan na jira na."

"Shikenan." Yace yana bude min motar, shiga nayi ya tayar muka tafi. Muna zuwa kofar gida na ga motar Ya Anas a ajiye da alama yana ciki kenan, fitowa nayi na masa sallama ina shirin shiga gidan najii yace

"Kinyi mantawa fa a bayan mota."

"Mantuwa?" Nace ina kallon shi

"Zo ki duba ki gani."

"Ni da ba idon kirki ba, duba min menene?"

"Ki zo dai ki duba." Yace yana kunshe dariyar sa, hararar sa nayi na dawo na bude bayan motar na zura jikina sosai a ciki, ji nayi an jawo ni gaba daya ciki, har glass din idona na nemam faduwa nayi saurin rike shi, fuskata daf da tashi har ina iya jin sautin fitar numfashin sa

"Kina tunanin zaki guje min ko?"

Kokarin kwace wa na hau yi ya rik'e ni gam, baki na bude zan sa kuka yayi saurin sa hannu a saman bakin nawa

"Kina kuka sai na baki mamaki wallahi."

Da sauri na hadiye kukan, ya sake ni nayi saurin fita daga motar, fitowa yayi shima ya leka yace

"Kanina zaka iya wucewa ni sai gobe."

Dariya Kamal ya saka yaja motar sa ya bar layin

"Muje ko?" Yace yana kallo na, kasa daga kafata nayi saboda tunowa da nayi Anas na ciki, ganin naki motsi yasa shi kama hannu na ya shiga jana har cikin zauren gidan

"Shiga zakayi?" Nace ina tsayawa ganin da gaske ciki yake son tura kansa

"I want to see my daughter dan jikina ya bani baby girl kika haifa min, baki da right na hanani ganin gudan jinina kuma."

Ya cigaba da jana, da karfi nasa na fizge hannu na ina sa masa kuka

"Ohh shit.!" Ya dawo baya yana duba na

"Kina so idon ki ya kara ciwo? Naji kamal na miki maganar ido."

Cikin shassheka nace

"Anyi kidnapping Iman, an kuma bata min ido na, bansan inda take ba."

"Me!!!!!" Yace yana zaro ido waje, girgiza ni ya hau yi da karfi

"Tell me wasa kike min dan Allah."

Sai kuma yasa hannu ya shiga shafa saman ido na

"Me yasa na tafi? Me yasa ban kara jira ba, menene amfanin rayuwa ta!"

Yace a rikice yana jawo ni jikin sa, da sauri na fada ya saka hannu ya rungume ni sosai yana kokarin boye hawayen sa.

"Waye Anan?" Yace yana haske mu da torchlight ɗin wayar sa.



****
Hello mutanen arziki, I'm sorry for yesterday duk da dama nace idan na samu chargy zaku jini.

Ga wata yar tambaya zuwa ga malaman zafafa

"Wai shin idan namiji ya saki matar sa ba tare da sanin sa ba, shin ta saku ko kuwa? Menene hukuncin sakin da Farouk yayi wa Aminatu a littafin DG? Shin ta saku tun da da kansa ya rubuta sakin duk da baya cikin hayyacin sa, kuma ba da gangan ya sha abinda ya gusar masa da hankalin ba, ko kuma bata saku ba?menene hukuncin hakan a musulunce. Nasan muna da manyan malamai cikin mu.

I ll be reading ur comments.

Nagodea: DG*

               *34*

★★★★★

"Waye anan?"

Yace yana haske mu da torchlight ɗin wayar sa, da sauri nayi kokarin janye wa daga cikin sa amma sai yaki, ya sake kankame ni yana duban Ya Anas

"Baka iya sallama bane ko me?"

Wani banzan kallo Ya Anas yayi masa yana matsowa ransa na matukar suya da abinda ya gani, Aminatu rungume jikin wannan gardin, be taba tunanin ta a irin wannan yanayi ba, yana zuwa yasa hannu zai raba su Farouk ya nuna shi da yatsa yana maida ni gefe

"Karka kuskura kasa hannun ka jikin matata wallahi."

"Matar ka? Idan naki fa? Iskancin ya kai har ka biyo ta cikin gida saboda tsabar rashin mutunci ko?"

"Waye wannan?" Yace cikin bacin rai

"Ya Anas ne!" Na furta a dan tsorace dan duk na gama tsorata da yanayin sa

"Ya Anas, me yake anan? Me ya kawo shi?"

"Baka da bukatar sanin abinda ya kawo ni." Yace yana duban shi, sai kuma ya dube ni rai a bace yace

"Zo ki wuce ciki."

Ina kokarin daga kafata naji Ya Farouk ya rike ni

"Don't you dare, idan kika daga kafarki anan wallahi sai ranki yayi mugun ɓaci."

"Idan kai ka haife ta ba? Sai ka hanata, zo ki wuce kafin kiga fushi na."

A hasale na dakatar dasu ganin suna neman charja min kai, cikin kuka nace

"Dan Allah ku kyale ni da abinda yake damu na, ku dukka kuna da dama a kaina, dan haka babu wanda zan wa abun da yake so na bar daya."

"Ya Farouk wannan shine Ya Anas, mutumin da ya tallafi rayuwa ta ya dubi maraici na ya rik'e ni tsakani da Allah dani da 'yata."

"Ya Anas wannan shine Ya Farouk, tsohon miji na kuma mahaifin Iman."

Tana kaiwa nan tayi saurin fadawa ciki tana rufe kofar da zata sadaka da zauren gidan, da sauri Anas ya fice daga gidan ba tare da ya sake duban inda Farouk yake tsaye ba kamar an dasa shi.
Iska me matukar zafi ya furzar yana sake kallon gidan maganganun ta na masa yawo a tsakar ka, kenan tana nufin bata da alaka dashi a yanzu kenan? Da kyar ya iya jan kafafun sa ya kai kansa bakin titi ya tari abin hawa ya wuce gida.

A zaune ya tarar dasu dukan su, magana suke a tsakanin su, kai tsaye dakin daya saba sauka ya wuce yana jin kansa na matukar sarawa.
Har ya kwanta ya tuno da Kamal, dakin daya san zai same shi ya wuce kai tsaye, yana kwance yana kallon wani video a wayar sa yaji an turo,tashi yayi ganin Ya Farouk yasa shi dan sosa kai yana murmushi

"First time na kwanan ka gidan nan right?"

Daga mishi kai yayi yana dariya

"I see."

Sai ya mika masa waya

"I need her number please."

"An gama." Yace yana dariya, karba yayi ya saka masa, yayi godia ya juya ya koma in da ya fito.

Sai daya fara duba jakar sa ya ɗan samu cookies yaci sannan ya kuskure bakin sa ya kwanta yana kashe komai na dakin.

Aminatu na kwance ta rasa me yake mata dadi kiran sa ya shigo, kamar kar ta tashi haka take ji saboda yadda ko ina na jikin ta ke mata ciwo, ga wani irin ciwon kai me tsanani daya addabe ta tun ranar da aka rasa iman, duk da tana ji a ranta yarinyar ta na nan da rai sai dai hankalin ta ya gaza kwanciya musamman data fuskanci kamar akwai wata rigima data shafi Daddy da wanda ya dauke tan, da tunanin ta masu garkuwa da mutane ne su nemi kudi, sai dai a yanzu ta tabbatar wani game ne ake so a buga da rayuwar yar ta.
Tun tana kuka da hawaye ta dawo na zuci, ta dukufa fadawa Allah dan shine kadai zai iya kawo mata dauki a cikin halin da take ciki.
Ganin me kiran da gaske yake yasa ta lallaba da kyar ta jawo wayar, bata iya ganin me kiran ba saboda babu glass a idon ta, saboda haka daga kawai tayi tana maida kanta saman filon data tashi.

"Assalamu alaikum."

Tayi sallama a hankali, shiru ya biyo baya ta sake maimaita sallamar karo na biyu, jin babu alamun amsawa yasa tayi yunkurin kashe kiran yayi saurin katse ta

"Karki kuskura ki kashen waya wallahi."

Zare wayar tayi daga kunnen ta, ta kalli saman screen din kafin, kafin ta maida kunne ta

"Tell me, me ya sami 'yata,wanne progress aka samu neman ta "

"Ban sani ba nima, su Daddy ne akan case din."

"Yasan yarmu ce?"

"Ya sani jiya."

Ajiyar zuciya ya sauke da karfi

"Me yasa kika ki jin magana a gaban trash din nan, kinsan yadda maganganun ki sukayi hurting din na?"

"Uhum "

"Kiyi hakuri." Yace murya a kasa, bata amsa ba ya sake cewa

"I'm sorry for everything."

"Uhum."

"Talk to me Dan Allah, ki min masifa ma if you like, in ma duka na zakiyi ki dake ni idan zai sa ki hakura."

"Iman." Tace muryar ta na rawa

"Taci abinci? An mata wanka? Lafiyar ta lau, She's just a child ya kake tunanin zata iya coping without her mother,abinda ya damen kenan Please Farouk!"

Ta fadi sunan sa kai tsaye, tashi yayi zaune zuciyar sa na zafi yace

"Nayi miki alƙawarin dawo miki da ita sound and in a good health, karki manta 'yata ce nima, responsibility nace ba tasu Daddy ba, zanyi duk yadda zanyi."

Kukan ta na ya kara tsananta ya dafa kansa yana daidai ta zaman sa sosai

"Tell me anything da kike tunanin zai bani hint wajen neman yata, fada min komai."

Shiru tayi tana nazari, chan Amal ta fado mata da wayar data ji tana yi dazu

"Adam, shine first suspect yanzu duk da bansan takamaimai alakar su da Daddy ba, Ina tunanin game ne yake so yayi playing da su, yasan wace ni yasan alaƙa ta daku tsawon lokaci yana bibiyata."

"Sannan..." Sai kuma tayi shiru

"Sannan me?" Yace

"Amal, naji jiya tana waya, ban yarda da wayar da take ba."

"Will you be my personal lawyer?" Yace yana murmushi

Murmushin tayi kadan tana runtse idon ta

"I love everything about Aminene ta."

Yace yana jan numfashi, wani iri taji ta sake danna kanta sosai a saman filon data ke kai, tana jin sautin fitar numfashin sa a hankali.

"Goodnight, kiyi mafarki na da Iman mun saki a tsakiya kinji?."

Daga kai tayi kamar yana ganin ta ta ajiye wayar tana lumshe idon ta.

File din ta dake kusa da ita ta daga filon tasa ba tare da ta buda shi ba kamar yadda tayi niyy.

***
Yana ajiye wayar ya shiga zagaye a dakin, badan dare ba sai yaje dakin Amal. System ɗin sa ya ciro cikin kayan sa ya kunna ta, e-mail ɗin da akayi masa wajen 3days back yaja hankalin sa sosai, a tsanake yake bin komai yana gid'a kansa cike da tsananin farin ciki


***
Kukan da take ne ya katse sakamakon wayar ta data dauki suwwa,da bayan hannun ta ta goge fuskar sannan ta daga tana karawa a kunnen ta.

"Baby kina jina? Karki bari asan muna waya dake, zan dan daina kiran ki kwana biyu amma ina so kizo address din da zan turo miki akwai abinda nake so na baki kiyi min wani aiki akai kinji?"

"Toh." Ta amsa a cunkushe

"Me ya faru?" Yace jin muryar ta a shake

"Ba komai."

Tace tana kashe wayar, ba'a jima ba text message ya shigo, bata bude ba ta cillar da wayar tana kwanciya a kasa, babu abinda yanzu take bukata face ace auren ta da Ya Farouk na nan, ganin Aminatu da tayi yau ya kara dagula mata lissafi. Kishin ta take sosai kamar zata mutu. Da kyar ta samu bacci barawo ya sace ta ba tare da ta shirya ba.

Da safe ta tashi a makare idon nan duk ya kumbure, tana jin maganganu a falon tayi tsaki ta fada toilet, wanka tayo tazo ta gyara fuskar ta kafin ta duba text message ɗin da yayi mata, duba address din tayi ta ajiye ta karasa shiryawa ta fito falon.

"Idon ki kenan Amal? Duk jiya baki ji alamun akwai baki gidan nan ba?"

Dadah ta tuhume ta cike da mamaki

"Na shigo da magriba kuna sallah, bacci nayi da wuri kinsan na kwaso gajiya."

"Okey yayi kyau, baki ga bakuwa ba?"

"Ina kwana?" Tace a gajarce

"Lafiya lou." Anty Safiyya ta amsa kafin tace

"Girma ba wuya Amal an zama yan mata."

Haushi ne ya kama Amal ta tashi ta koma daki ta zauna tana tunanin yadda zata fita ba tare da kowa ya gane ba.
Duk tunanin ta ya tsaya ta rasa ya zatayi gashi daga ganin alamun zaman da Dadah tayi a falon babu ranar tashi.
Curtains ta yaye jin alamun za'a ta da mota, Kamal ne tsaye suna magana da Farouk, jingina tayi da bangon tana kare masa kallon tsaf, zuciyar ta bata san komai ba sai soyayyar sa, yayi kyau ya sake mirjewa kamar bashi ba. Ganin ya juyo yasa tayi saurin sakin labulen tana sauke ajiyar zuciya.
Cigaba tayi da tunanin mafita har zuwa sanda ta sake jin maganganu sun sake karuwa a falon
Alamun taba kofar dakin taji kafin tace wani abu ya budo ya shigo kai tsaye.


"Come out!"

Yace daga bakin kofar kafin ya juya, hadiye yawu tayi da k'yar ta tashi kamar wadda kwai ya fashe wa a ciki ta fito falon. Daya bayan daya ta shiga raba idanun ta tana binsu d kallo, kafin ta shiga jan kafar ta isa gaban su tana zama kasa. Daya Daya ta gaishe dasu Daddy zuciyarta na cike da tsoron kiran da aka mata


"Ina wayar ki?"

Ya Farouk ya mika mata hannu alamun ta bashi, gaban tane ya fadi ta hau rawar jiki. Daka mata tsawa yayi data firgita ta tayi saurin miƙa masa wayar, kai tsaye call log dinta ya fara shiga ya duba numbers din datayi waya da call duration kafin ya fita ya shiga messages, da sakon shi ya fara cin karo ya yi shiru yana karanta sakon, tabbas hasashen da Aminatu take gaskiya ne, Amal nada masaniya akan komai, number ya dauka akan wayar shi da message ɗin ya isa gaban Alhaji Marwan ya mika masa wayar yana komawa wajen zaman sa.

"Menene dalilin tara mu da kayi anan Farouk?"

Alhaji Marwan yace yana kallon wayar Amal din ba tare da ya duba ba.

"Daddy ka rike wayar ko da za'a kira, ina da maganar da zanyi kafin a gangaro maganar wayar."

"Toh muna jinka."

"Da farko dai ina neman yafiya a bisa laifin dana aikata na tafiya na bar kasar,hakan ya faru ne a bisa dalilai na da nake ganin sun kai na zartar da komai. Sai dai ni kaina bani da masaniyar takamaimai abinda ya faru, tun bayan da ƙaddara ta haɗa ni da Aminatu har aure ya shiga tsakanin mu zuwa sanda na bar gari zuwa wani aiki da dawowar da nayi na tarar da mugun labari da bani da masaniya akai."

"Naso kwarai Daddy ya bani dama ko sau daya na kare kaina amma hakan be samu ba, a dole na tsananta bincike anan ne na gano akwai hannun Amal a cikin abinda ya faru daya jawo rabuwa ta da Aminatu."

"Na kirata na tuhume ta da laifin dana kamata dumu dumu na kuma bukaci na ji wanda ya sakataa, to my surprise sai gashi ta kira sunan mutanen da nafi kusanci dasu, Dadah da Ja'afar wanda duk duniya ina ganin idan akwai wanda na yarda dasu toh su biyo bayan su,wannan dalilin shi yasa ni tafiyar dole dan bazan iya zama ina kallon su da abun ba."

"Innalillah wa inna ilaihi raji'un."

Dada tace tana kallon Amal kallon tsantsar mamaki.

"Muna sauraron ka." Uncle Aliiyu yace

"Na tafi da clip din da aka dauka lokacin da nake rubuta sakin da kuma voice recording din da akayi lokacin da aka kirani a gaban kowa dan a tambaye ni dalilin abinda na aikata. Da fari na shiga rudani sosai dan bani da hujja da zan ƙaryata hakan, na farko dai murya ta ce gata nan, na biyu ni ne zaune ina rike da takarda da biro."

"Tsawon lokacin nan nayi shi ne cikin binciken yadda akayi hakan ta faru, ban samu ba, haka na hakura na bar wa Allah komai. Sai gashi jiya cikin hukuncin Ubangiji mutumin da ya taimaka min kwarai wajen bincike na yayi min e-mail inda yake tabbatar min da duk abin da yake cikin clip din da kuma abinda yake a recording din nan shiryayye ne anyi amfani da lastest technology da wasu set of intelligent agencies dake ƙasar Amurika ke amfani dashi wajen sauya abin, yana so na tsananta tunani na gano abinda ya faru a rana makamanciyar da abin ya faru."

"Tsawon daren jiya ban runtsa ba ina tunanin abubuwan da suka faru, tunani na ya dawo nan take sanda nake tuna tabbas Amal ta kawo min abu nasha a ranar sannan munyi hira data shafi Aminatu tana min tambayoyi ina amsawa sannan tabbas ranar ina rubutu ne ta tarar dani, wannan abubuwan su aka juya aka sauya zuwa komai, ba dani aka yi waya ba sai dai tabbas murya ta ce,magana ta ce aka hada yayi daidai da abinda Daddy zaku tuhume ni akai."

Murmushi yayi me ciwo yana janyo system ɗin sa ya tura ta gaban Daddy kafin ya dora

"Ina fatan wannan shaidar kadai ta isa ta wanke ni daga zargin da ake min sannan ina so ta fada a gaban kowa gaskiyar abinda yake faruwa. Me yasa lokacin dana tuhume ta ta nuna min tabbas na rubuta takardar kuma bana hayyacina, me yasa ta boye min gaskiya ta sake nisanta ni da matata da yata, me nayi mata haka mai zafi ta na chanchanci wannan?"

"Annamimiyar Allah!" Dadah tace tana saka kuka, kukan Amal take sosai itama ta kasa cewa komai, girgiza kai Daddy yayi cikin yanayi mara daɗi yace


"Adam yayi amfani da yarintar ta ya bata mata tunani."

Wayar ta Alhaji Marwan ya duba kafin ya mika wa Daddy shima yaga text message ɗin

"Amal me yasa ki aikata haka?"

"Daddy kayi hakuri."

"Tell me, zan saurare ki, me yasa? Saki yayi ko? Me yace miki?"

"Daddy ni tausayin sa nakeji, babana ne, ina son sa yace kuma kashe shi zakuyi tunda kai soja ne."

"Haka yace miki?"

"Eh."

"Shikenan daina kuka, mesa zamu kashe shi, ba haka bane kinji? Shiryawa zamuyi dashi mu nemi gafarar sa laifin da mukayi masa, can you help us?"

Shiru tayi tana tunani, kallon fuskar Daddy take, babu alamun karya a maganar sa, bayan haka ma be taba musu alkawari ya saba musu ba komai shi yake musu, sai ta samu kanta da daga mishi kai.

"That's my girl, bata wayar ta MD, text him kice kina hanya kinji? Kije ki gan shi babu damuwa."

Kallon sa tayi ya dage mata kai cike da gamsar wa

"Kije Allah yayi miki albarka, karki sanar dashi munyi maganar nan a waya sai kinje yanzu text kawai zakiyi masa."

Tashi tayi tana goge fuskar ta ta wuce daki.

"Me hakan ke nufi?"

A cewar Uncle Aliyu

"Shine kawai mafita, bin ta zamuyi dole sai an kama Adam a hannu komai zai warware."

"Lallai akwai banbanci, na kara tabbatar da kai din jami'in tsaro ne, kudos."

Duk sukayi murmushi banda Farouk da yake kallon su kawai.


****
Kiran wayar ta ya fara yi bata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login