Showing 1 words to 3000 words out of 110913 words

Chapter 1 - NAHUCE BOOK COMPLETE BY Sumayya Abdulkadir Takori Kabara .doc

??ࡱ?>?? ? ????????????? ? ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ????

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F? WordDocument????j0Table????????? Data
???????????????????? P?TvKSKS?j*????????pp????Ui??????? ? ? ? ? ? ? ? ? $% ?? *p??? ? ?????  ?i ? i?  i? ? ?i  SUMAYYAH ABDULKADIR TAKORI

07030137870

*NA HUCE!*



SHIMFIDA
ZAMFARA STATE, NAJERIYA

Yamma lis, a wata ranar Lahadi, wadda tayi daidai da shida ga watan Yuli, ta shekarar alif dari tara da casa'in da tara da misalin karfe biyar na yamma, majalisarsamarin unguwar Kofar Jange ta hadu, ta cika ta batse cikin birnin ZAMFARAN Najeriya. Opposite wannan majalisa ta samari wani gida ne da za'a iya kira ginin masu kudin da, koko a ce 'yan bokon da, wanda aka yi wa renovation daidai da zamani, gida ne mai asali da tsohon tarihi a unguwar ta (Kofar Jange) da yayi fice sakamakon kasancewar mamallakin sa tsohon dan boko kuma dan siyasa da aka dama dashi a gwamnatin Zamfara tun daga state har federal.

Ita wannan unguwa KOFAR JANGE unguwa ce mai tsohon tarihi wadda ta samar da jiga-jigan 'yan boko da masu fada aji a jihar Zamfara. A dalilin maigidan tsohon dan siyasa ne wanda ya kare rayuwar sa cikin hidimar al'umma. Wadanda suka gudanar da siyasar su ta gaskiya da rikon amana tun duniya na kwance, lokacin mulkin Janar Abdulsalami Abubakar. Duk wani Bazamfare ya kwana ya tashi da sanin tarihin gidan Alhaji Mustapha Bilyamin Nahuche.

"GIDAN NAHUCHE!"

Shine lakabin da ake kiran wannan gida a garin Zamfara. A saman gidan ma an rubuta hakan cikin rubutu na ruwan gwal. Gida ne mara tarin iyali domin matar aure daya ce tal tayi rayuwa a cikin sa ba tare da kishiya ba; su biyu ne kadai 'ya'yan gidan a wajen marigayi mahaifin su Hon. Mustapha Bilyamin da mahaifiyar su Hajiya Kaltume (Hajiyar Nahuche).
Wannan zama da samarin nan suka yi ba na komai bane na jiran isowar sa ne, shi kadai ran sa dan Nahuche jikan Nahuche.... da suke matukar kauna, ya kuma zame musu role-model wato mutum abun koyi a halayya da dabi'a, da kuma yadda yake gudanar da kafatanin tsarin rayuwar sa, bi ma'ana, shi mutum ne da suka yiwa kyakkyawar shaida ta saukin kai da girmama matasa; ga sukuni Allah ya bashi, ga tarin kuruciya da zuzzurfan ilmi amma babu ashararanci ko kankani a tare da shi. Bai gaji mahaifin sa ba ta fuskar siyasa, amma ya gaje shi ta fuskar ilmin boko, shi kawai dan boko ne mai ci da gumin, biron sa.
Tun safe suke zaune, har zuwa yanzu da rana ta tasamma faduwa, suna da labarin ya shigo Zamfara a safiyar yau yana gidan sa na GRA, kuma duk ranar da ya shigo matasa da masu neman aiki na unguwar su sun warke, shi ba dan siyasa bane (business tycoon) ne mai kishin matasan yankin sa, sannan mai connections a birnin Tarayyah, suna da tabbacin dole zai zo ya gaida mahaifiyar sa Hajiya Kaltume komai dare, ba zai kwana cikin Zamfara ba, ba tare da ya zo ya ganta da tilon Dan sa ba.
Karfe nawa zai zo ne basu sani ba, in kuma zasu kwana dakon zuwan sa bazasu gaji ba, dalilin zaman su kenan a majalisar kofar gidan Hajiya Kaltume Nahuche.
Hira suke irin ta samari masu jini a jika masu burin da babu ranar cika shi; duka burin su dai shine su zama kamar sa a komai; a ilmi, a dabi'a, a halayya, a kasuwanci, a taimakon al'umma, a irin motocin da yake hawa, a irin simplelife-style din sa, a farin jini.....a kyawun sura a komai da komai. A cewar su dai, yana daga cikin masu sa'a a rayuwa in ka dauke gwaurantakar sa da bata dada shi da kasa ba.
Abin kamar hadin baki rediyon hannun daya daga cikin su ta soma kwararo muryar sashen Hausa na BBC (British Broadcasting Corporation) cikin shirin su mai taken: "DOMIN MATASA....."
Mai gabatarwa yayi sallama sannan ya ambaci sunan bakon mako, wanda ya sanya samarin baki daya sakin ihu cikin hargagi irin na samari harda masu mikewa suna daga juna. Shiri ne da sukeyi duk karshen sati wato ranar Lahadi domin tattaunawa da talentedbusiness tycoons masu jini a jika irin "HABIBU NAHUCHE....". Domin karfafawa matasa wajen neman na kai da neman ilmi.
Mai gabatarwa, AbdulHadi Taheer, wakilin BBC a jihar Zamfara, ya ce "Assalamu alaykum masu sauraren muryar Hausa ta BBC, a yau muna tafe ne tare da "NAHUCHE", in nace Nahuche ina nufin HABIB, MUSTAPHA BILYAMIN NAHUCHE....... The propriator of NAHUCHE HOTELS & NAHUCHE GROUP OF HOTELS. Barka da zuwa wannan fili Engnr. Nahuche, matasan Zamfara na son sanin takaitaccen tarihin ka?".
Zuzzurfar muryar sa kasaitacciya ta mazan da suka hantse cikin ilmin addini dana zamani ta kwararo sallama da Bazamfariyar accent din sa, wadda banbancin ta da sakkwatanci kadan ne.....
"Assalamu alaykum, sunana Habibu Mustapha Nahuche, ni Bazamfare ne gaba da baya, nayi karatun firamare da sakandire duka a kauyen Nahuche kafin mahaifi na ya dawo birni a dalilin neman ilmi da neman abinci. Bayan kammala karatuna na sakandire na samu scholarship daga (Petroleum Technology Development Fund) da aka fi sani da PTDF zuwa kasar Germany, na karanci 'Hotels Administration' daga jami'ar Cologne, Germany. Nayi digiri na biyu duk a Cologne akan fanni guda. Na dawo gida a shekara ta 2000 na fara aiki da babban hotel din Najeriya na wancan lokacin (Nicon Noga) inda na rike manyan mukamai acan, daga baya na fara ginin hotel dina na farko a garin mu wato Zamfara, daga nan ne abubuwa suka mike har aka samar da NAHUCHE GROUP OF HOTELS a manyan jihohi na wannan kasa tamu mai albarka. Na taba aure, inada yaro".
Abdulhadi Tahier yayi murmushi yace "masu sauraro zasu so su samu karin haske akan kalmar "na taba aure" domin kalma ce mai harshen damo, har yanzu da auren ko babu?"
Wani kasaitaccen murmushi ya saki, wani abu ya soki zuciyar sa, a lokacin da bafullatanar fuskarta ta gilma masa kamar walkiya, "ta yaya zai mantata da lokutan kwanaki bakwai?" A hankali kuma cikin karayar murya na tasowar wani tsohon miki yace.
"Duk yadda anka fassara ta, daidai ne!".

Abdulhadi Tahier bai ja tambayar da nisa ba don ya fahimci ya gama amsa ta. Sai ya dauko maqasudin tattaunawar, wanda shine abinda suke so matasa su amfana da shi.
"Ko menene sirrin da ke karkashin nasarori da habakar 'Nahuche Hotels' akan sauran gidajen saukar baki da muke dasu a kasar Najeriya?"
Bai bata lokaci ba ya amsa.
"Excellent Service Delivery!"
"Shin ina ne NAHUCHE? Domin banda Zamfarawa, ba kowa ya san garin 'Nahuche' da ake kiran ka da ita ba, wadda har ta boye asalin sunanka na yanka? A yanzun ana maganar kasarmu Najeriya ne in general da babu babban birnin da baka da Hotel, kana da masu kallon ka as a role-model suke kuma son jin wasu daga boyayyun sirrikan rayuwar ka".
"Nahuche karamin kauye ne a karamar hukumar Bungudu. Ainahin garin Nahuche gari ne dadadde, garin ne da mutanen garin hausawa ne. Mutanen garin bakake ne sid.
A wata shekara garin ya hadu da musibar hare-hare daga wasu garuruwan. An addabi garin da yaqi har suka rasa yadda za suyi. Ana cikin wannan halin ha%??jlin, sai wani shahararren mayaqi Ya zo daga Katsina, cikin kabilar Rumawa. Rumawa kuma ka san fulani ne kyawawan gaske.
Wannan shahararren mayakin tafiya ta biyo da shi ta cikin garin Nahuche, sai Kekun Nahuche (sunan ainihin sarautar Nahuche kenan) Ya roki wannan mayakin da ya taimaka masu kan hare-haren da su ke fama da su. Har yayyi mashi alkawarin idan har yacci wannan yaqin to zai bashshi rabin kassar shi da kuma sarautar Uban Dawakin Nahuche.
Aka yi yaqi, kuma aka samu cin nasara, shi kuma Kekun Nahuche bai manta da alkawarin da ya dauka ba, ya ba wannan mutumin sarautar Uban Dawaki (saboda ko da yazo a kan Doki yazo) ya kuma bashi rabin kasar shi Nahuche, shi kuma ya koma Katsina ya zo da iyalin shi suka ci gaba da zaman lafiya da mutanen garin, da Keku da Uban Dawaki sune ainahin sarautun da ke Nahuche kuma kowanne na mulki individually.
Har yanzu akwai rabe-rabe akan sunan wannan Bakatsinen amma mafi yawanci sun ce sunan shi Juli (sunan fulani ne). Juli ya sa %??ia 'yan shi sun yi makaranta, ciki har da kakanninmu, my grandfather (Bilyamin Nahuche) yana daga cikin dattijan wannan gari".
"Madallah da wannan kyakkyawan bayani na tarihi akan garin Nahuche, a karshe wane sako gare ka ga matasa masu burin zama manyan (business figures) irin ka a Najeriya?
Wannan karon da murmushi ya amsa.
"Su duba organizational theory of business, kafin kafa kowanne irin kasuwanci. Gaskiya, rangwame da rikon amana shine sirrin nasarar kasuwanci, kada a raina riba komai kankantarta. A zama kullum cikin tunanin sababbin hanyoyin habaka kasuwanci a zamanance (technological innovation). Abu na karshe shine mai cin muguwar riba, baya taba nasara a kasuwanci kuma dukiyar sa bata albarka".
Samarin nan banda ihu ba abinda suke yi lokacin da shirin ya kare, muryar shi kadai tsuma samarin Zamfara take yi, kaunar da suke mishi ba 'yar kadan bace. Da a ce shi mai bin ra'ayin wasu ne ba ra'ayin rikau ba, da ya dade da shiga siyasa "........Allah ya taimaki Nahuche.......Allah ka bar mana Nahuche......." kawai suke ambato cikin hargowa. Daidai lokacin da motar baka wuluk kirar PORSCHE ta sulmiyo ta shigo layin kamar yadda suka yi tsammani. Suke kuma dakon jira.
Dan sardidin matashi da shi. Habibu Nahuche. Yau ma kamar kullum ya fito yana takun nan nasa majestically, cikin farin danyen Voyel mara nauyi dan shafal, dinkin jikin sa (very simple) wanda aka yi shi dan siriri da farin zare, sai da ya baiwa kowannen su hannu daya bayan daya babu gazawa cikin far'a da sakin fuska, sannan ya kawo ihsanin da ya saba yi musu a dunkule yayi musu, addu'a iri-iri Habibu ya sha ta, bai tsaya sosai ba ya wuce kai tsaye zuwa cikin gidan iyayen sa.
Mahaifin Habibu Alhaji Mustapha Bilyamin Nahuche tsohon dan siyasa ne wanda ya rike manyan mukaman siyasa a jihar Zamfara a lokacin rayuwar sa, yayi dan majalisar dattijai mai wakiltar Zamfara ta kudu, yayi sanatan Zamfara ta kudu, yayi shugaban karamar hukumar su wato Bungudu wadda garin Nahuche ke karkashin ta. Ya rasu ya bar matar aure daya da 'ya'ya biyu mace da namiji.
Itace aunty Badiyya Nahuche, wadda ke aure a garin Kaduna, tanada yara hudu, sannan shi Habib, dake binta, daga kansu Allah bai kara baiwa Haj Kaltume haihuwa ba.
Da sallama ya shiga falon Hajiyarsa, tana kishingide akan tumtum, ta kunna rediyo tana sauraron hirar da ake yi da shi. Shigowar sa tayi daidai da karewar shirin. Ta kashe rediyon tana mai shimfida masa karamin center carpet, bakin ta dauke da murmushi, fadi take.
"Habibu bazaka bari ka kwanta ka huta zuwa gobe sannan ka shigo ba? Ka taho tun daga Lagos? Ka san dai tunda samarin nan suka ganka ba bari zasu yi ka huta ba".
Murmushi yayi yana zama akan shimfidar data yi masa, idanun sa cike da kewar ta, da ganin su zaka san akwai shaquwa da kauna ta musamman bayan ta iyaye da Allah ya riga ya assasa, cikin nutsuwa irin tasa ya sunkuya ya gaisheta, sannan yace "bana taba gajiya dasu Hajiyar mu. They are part of me (su rabin jiki na ne), nima shekarun baya ai kamar su din nake; matashi mai buri. Ina Abdallah?"
Hajiya Kaltume ta nisa, sannan ta ce "Badiyya ta tafi dashi Kaduna hutu, amma gobe insha Allah nace a kawo shi don ku gaisa, kafin ka tafi Makurdi din da ka ce zaka wuce daga nan.
Anya Habibu ina amfanin a dinga yamadidi da kai a kafafen yada labarai ana fadin baka da aure sai kace wani dan siyasa? Shin ita ta kara tuna ka a duka wadannan shekarun nan ko bata san inda kake ba da dan ta? In tana da niyyar cigaba da rayuwa da kai ai da tuni ta nemeka. Tunda na tabbata ta san inda ka ke. Kai ne baka san inda take ba. Kai din a yanzu kuma fitacce ne kuma sananne a kasar Najeriya, bai yuwuwa ace bata san da wanzuwar ka ba koda a kafafen yada labarai ne. Idan har tana da muradin sake rayuwa da kai.
Mata na duniya babu irin wadanda iyayen su basa kawo min, babu 'yar wanda bazaka aura ba Habibu, ka hakura da yarinyar nan...... ka hakura da ita bisa umarni na!".
Hajiya Kaltume bata ankara da cewa hawaye ne ke zuba daga idon sa ba.....sai da ta kai karshen maganar ta. A fili ta furta
"Yaa Salamu sallim!"
Domin al'amarin Habib da uwar dan sa yafi karfin tunanin ta.
A duk lokacin da ta takura masa da zancen aure karshenta kenan, yayi mata hawaye. Don bai da abin cewa. Shin wacece wannan uwar Abdallah haka? Kuma me ta taka da har ta mallake zuciyar namijin duniya irin dan ta Habibu Nahuche???
****








ABUJA, NAJERIYA
(Cikin Gidajen Likitoci na National Hospital
9:30 am).





Ta kashe rediyon a hankali, zuciyar ta na wani irinragaita, tana daga cikin wadanda suka fara aikawa BBC sakon appreciation din su ga wannan shiri na musamman. Abubuwa masu yawa da suka gabata a birnin Cologne din Jamani shekaru GOMA a baya na gilma mata. Wannan ita ce kaddarar su, da har gobe ba wanda ya san ta. Kuma kaddarar data hana ta AURE shekaru goma bayan rabuwar su. Kaddarar data maida rayuwar ta duhu didim; farin ciki bai kara gudana a cikin ta ba; "Kaddarar auren kwana bakwai".
Ta dauki hoton karamin kyakkyawan yaron mai kama da ubansa a komai tana kallo, hawaye na sauka akan fararen sumul-sumul din kundukukinta. Ta san yanzu ya girma, watakila aji hudu na firamare. Cikin kowanne hali dai ta san zai kula da shi. Damuwar ta ba akan kulawar da zai samu bane domin hakika Habib Nahuche zai kula da dan sa har fiye da yadda yake kula da Hotels din sa. Damuwar ta akan yadda har gobe ta kasa kallon kowanne namiji da idanun sigar aure, kowa ya zo sai ta ga bai kai shi ba, ko farcen kafar sa bai kama ba, koda kuwa ya fi shi komai na rayuwa.
Duk da cewa ta san shi ne kawai a matsayin dalibin jami'ar Cologne ba'a matsayin sa na yanzun ba (mamallakin Nahuche Hotels) amma tana bibiye da duk wani fadi-tashin sa na rayuwa daga ranar da ya yi kidnapping Dan su. Dalilin bibiyar ne bata sani ba har yau, tunda ita tace bata son sa. Farin jini kam har bata san irin nata ba, manema ba irin wadanda Allah bai bata ba, kuma burin Dada shine tayi aure tun kafin Allah ya dau ranta, amma har gobe ta kasa kallon kan sauran maza da gashi sai dan mutanen Nahuche. The one that took away her pride na diya mace. Wanda ta tabbatar zuwa yanzu ya manta da ita, a irin shuhurar da Allah yayi masa cikin shekaru goma kacal da rabuwar su.
Bata san hawaye take ba. Sai da ta ji dandanon gishiri a bakin ta. Hawayen da ta tabbatar bazata daina zubar dasu ba har zuwa karshen rayuwar ta. Idan har rayuwa bata koma yadda take a baya ba; with him by her side.
"Auren Wucin Gadi". "Auren kwanaki bakwai kacal". Wadanda abubuwan da suka wakana cikin su sun fi tsayin na shekaru bakwai. Wanda ya samar da kaddarar Dan da ke a tsakani, Dan da silar zuwan sa duniya ne yayi connecting komai, ya hada zukata ya kuma raba su cikin kwanaki bakwai. Jami'ar Cologne din Jamus ita ce tushe, mafari, ginshiki na dukkan walagigin rayuwar data samu kanta. Plus rashin cikakken gata da ya baibayeta a lokacin.
Shekaru goma a baya, suka soma tariyo kansu a idanun ta, tamkar a majigi.
*****



NA HUCE.....IS NOT FOR FREE.
IT'S N1000 VIA;

3094856450.
SUMAYYAH KABARA
FIRST BANK

SHAIDAR BIYA
07030137870
SUMAYYAH ABDULKADIR TAKORI 07030137870


*NA HUCE!*
(PAID BOOK)

(FARKON LABARIN)
SHEKARU GOMA A BAYA


Daga cikin bututun maganar cikin jirgin Boeing745 wanda ya tashi zuwa kasar Jamus a yau daga filin jirgin saman Murtala Mohammed dake Lagos, bututun sadar da sako na gaggawa ya karade kunnen fasinjoji, "jirgi yana cikin hatsari, jirgin mu yana watangaririya, hazo ya lullube sararin samaniya gabadaya, direbobi sun rasa direction din su, a sabili da haka muke shawartar a sanya rigar hatsari, don komai na iya faruwa, sannan ta soma bayanin (how to escape a plane crash) cikin gaggawar magana.
Abinda ya gigita fasinjoji, ya firgita mata da yara, masu kuka na yi, masu salati na yi, bata san sanda ta kankame mutumin dake gefenta ba tana rusar kuka.

"Ina da gyatuma, da Allah da ni kadai ta dogara, dama sai da tace min kada in taho karatun nan, don ba lallai mu sake ganawa ba, don Allah don annabi ka taimaka min kada in mutu, in koma wajen Daada".

Za'a iya cewa shikadai ne bai razana a cikin jirgin ba, da ganin yarinyar ta gama tsurewa, kokari yake yasa mata rigar hadari amma ta bi ta cukuikuiye shi gabadaya.

Ta kankameshi kamar ta samu uwar ta. Duk da cikin tashin hankali suke sai da yaji wani iri a cikin jikin sa da ruhin sa. Da karfi ya yakice ta,

"Hey! Relax, are you not a Moslem? Kiyi addu'a, ki cika ni insa miki rigar kubuta daga hadarin jirgi". Ya soma ambaton "innalillahi wainna ilaihi raji'oun......" a fili har itama ta kama eventually.


Cikin ikon Allah ba'a yi minti talatin ba kuma komai ya daidaita. Hazo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login