Showing 66001 words to 69000 words out of 154131 words
Chapter 23 - Masarautar Alhamra Complete Hausa Novels By Asmeetah Writer.txt
mai aiki, wadda kana ganinta kasan sabuwar zuwa ce, ta matso da sauri tana rawar jiki.
“G-Gimbiya, a yau an kawo ruwan Passion Fruit ne, saboda an ce lemun orange ɗin ya ƙare a kitchen.”
Maayah ta ajiye cokalin ta a hankali, sa'an nan ta ɗaga kai ta kalli sabuwar mai aikin. Ta yi mata kallo tun daga kanta har zuwa takalmin ta...
“Kin san cewa a cikin Fadar Alhamra, Maayah ba ta shan ruwan Passion Fruit? Kuma kin san cewa lemun orange bai taɓa ƙarewa ba? Yanzu haka, ki tashi ki kawo min sabon ruwan lemun. Idan kuma ba ki same shi ba, to ki je ki samo wanda zai kawo min a cikin minti biyar, sannan ki cire kayan jikinki ki bar mun site...”
Muryar Gimbiya Maayah ba ta da zafi amma ta fi ƙarfin wuta. Nan take, sabuwar mai aikin ta fashe da kuka, ta durƙusa tana roƙon afuwa...
“Gimbiya, dan Allah, ki yi haƙuri. Na yi kuskure. Zan tafi in samo.”
“Too late,” Maayah ta yi tsaki. Ta kalli ɗayan mai aikin, wadda ta fi ta sanin komai...
“Maimaita wa wannan sabuwar dokokinmu! Ba na son ganin ta a cikin fada ta. Cire mata uniform ɗin ta. Kuma Mama Liyatu ta kawo min ruwan lemu.”
Mama Liyatu ta shigo da sauri, tana sanye da doguwar riga mai kyau...
“Gimbiya ta, dan Allah ki yi haƙuri, abinci yayi daɗi fa. Ki bar ta. Zan kawo miki ruwan.”
Mama Liyatu ta san yadda za ta tausasa ran Gimbiya kafin ta fusata...
Maayah ta yi sigh mai nauyi... “Fine. But babu wanda zai iya damuna a cikin gida na.”
Mama Liyatu ta yi murmushi, amma cikin tsoro take faɗin.
“An gane, Gimbiya. Duk abin da kika ce shi za a yi.”
Ta juya, ta yi nuni ga masu aiki biyu da su raka sabuwar mai aikin...
Bayan ɗan mintuna sai ga wani jami’in tsaro na fadar sarki ya shigo domin isar da saƙo.
Ya gaishe da Maayah dake zaune a kan teburin cin abinci, sannan ya ce,
"Sarki ya aiko ni, yana son ganin gimbiyarsa Maayah..."
Maayah ta ɗaure fuska tare da yamutsa ta cikin isa ta ce,
"Kaje kace masa Maayah makaranta zata je, sai ta dawo."
Kafin Maayah ta sake furta wani abun, har jami'in tsaron ya juya ya fita domin isar da saƙon...
Kamar dama jira yake ta faɗi abin da zai sosa ran sarki, domin tun ba yau ba ake sanar da sarki cewa Maayah ta ɓaci da wulakanci da girman kai tamkar Zayana, amma sarki ya ƙi yarda...
Ganin jami’in tsaron ya tafi ne ya sa Maayah faɗin,
"Daga cewa makaranta zan je shikenan sai ya tafi? Faɗa kawai nayi, amma ba wai naƙi zuwa bane..." Ta ƙarisa maganar kamar mai fargabar abun da zai je ya dawo...
Mama Liyatu ta ce,
"To tinda hakane, kawai ki tashi kije ƙiran sarki. Idan ya ganki da uniform ɗinki, zai fi sallamarki da wuri, ya fi dai baki je gaba ɗaya ba."
Maayah ta kalli Mama Liyatu cikin isa ta ce,
"Mama Liyatu, ni fa ba a bani shawara ballantana umarni. Abin da naga ya dace shi zan yi."
Mama Liyatu ta yi shiru, ba ta sake cewa uffan ba..
Maayah ta ƙara da cewa,
"Ya je ya sanar ɗin tinda shi munafuki ne, bai jira na gama magana ba ya tafi. To makarantar zan je, na ga ko kashe ni za a yi!"
Ta ci gaba da cin abincinta cikin kwanciyar hankali, babu ruwanta da kukan yarinyar da aka kora ba tare da wani dalili na kirki ba....
Cikin minti biyar, direbanta wanda shima yake sanye da uniform ya iso ya tsaya a gabanta...
"Gimbiya, motar tana nan a shirye. Makarantar za a tafi yanzu?"
"Yes. Amma ba zamu bi hanyar da talakawa ke bi ba a yau. Zamu bi ta hanyar Presidential Gate, ina so naga yadda take a yau."...
Direban ya sunkuyar da kai,
"Kamar yadda kika ce, Gimbiya."
Maayah ta tashi, ta zuba ido ga Mama Liyatu ta ce,
"A cikin mako mai zuwa Mama Liyatu, ina so ki shirya min gagarumin party.... Zan gayyaci 'ya'yan ministoci da 'yan kasuwa masu kuɗi... Ba na son ganin talaka a cikin fadar Maayah..
Ki tabbatar an kammala komai kafin na dawo daga makaranta."
Ta fita tana takun alfarma da kasaita, dakarun tsaron ta guda biyu suna biye da ita....
Motar Lexus mai sheƙi ta ɗauke ta ta bar bangaren nata...
Kafin Maayah ta bar bangarenta, har jami'in tsaron ya isa gaban sarki ya sanar da shi yadda suka yi...
Tafida dake zaune a gefe ya cika da mamaki ya ce,
"Maayah ce ta ce haka?"
Jami'in tsaron ya tabbatar masa. Sarki Nourdeen yana zaune a kan karagar sa cikin siffarsa ta Zaki, bai ce komai ba...
Suna zaune
Kwatsam, sai wasu jami'an tsaro suka sanar cewa,
"Ga motocin Gimbiya Maayah nan zasu wuce makaranta."
A lokacin ne Sarki ya miƙe tsaye cikin kwarjini. Shi da kansa ya nufi wajen fada zai fita.
Wasu fadawa cikin girmamawa suka ce,
"Mai Martaba, ka bamu izini mu dakatar da su, ba sai ka fita ba."
Sarki ya ɗaga musu hannu alamar su kyale shi...
Yana fita, daidai lokacin da motocin Maayah suka raba titin gate ɗin fita, sarki ya saki wata irin uban tsawa mai firgitarwa cikin muryar Zaki mai cike da daji...
"MAAAYAAAHH!!!"
Wata irin girgiza motar su ta yi har sai da ta ɗan ɗagu daga ƙasa...
Direban ya danna burki da kansa, motocin suka tsaya cak! Saura kaɗan motar da Maayah take ciki ta kife. A cikin motar, Maayah ta yi sumar zaune saboda tsananin firgici...
Kaf jami'an tsaro, fadawa, bodyguards, da dakarun sojoji babu wanda bai tsorata ba, wasu ma har neman guduwa suke yi..
Fadawan dake kusa da sarki ma kowa ya ruɗe, har sai da wani ya saki fitsari a jikinsa saboda tsananin firgici....
Kukan birkin motocin ya haifar da wata baƙin hayaƙi mai yawa a harabar Gate...
A cikin motar Lexus ɗin, Maayah ta daskare, idanunta sun fito waje, numfashinta ya tsaya na mintuna biyar.. Ba ta taɓa jin muryar mahaifinta cikin wannan yanayin ba. Jikinta ya fara rawa, izzar da take ji yanzu ta narke ta koma tsoro tsagwaronsa...
Sarki Nourdeen ya taka zuwa tsakiyar hanyar, takunsa na girgiza ƙasa... Fuskarsa ta Zaki mai cike da gashi tana wani irin haske na ban tsoro, idanunsa ja wur kamar garwashin wuta...
Ya tsaya gaban motar Maayah, kowa na wajen ya ɗuka, wasu sun kifa fuskarsu a ƙasa don kar su kalli fuskar Zakin...
"FITO!!!" Ya sake daka wata tsawar, wadda ta sa gilashin motar Maayah fara tsagewa...
Ƙofa ta buɗe a hankali. Maayah ta fito, cikin takun tsoro da firgita, ƙafafunta sun kasa ɗaukar nauyinta... Ta zube a ƙasa gaban mahaifinta, uniform ɗinta ya ɓaci da ƙura...
"Barka da safiya... Abul," ta faɗa cikin murya mai rawa, kanta a ƙasa...
Sarki ya matso kusa da ita, inuwar fuskarsa ta Zaki ta mamaye duk jikinta. Ya sunkuyo da kansa daidai kunnenta, tana iya jin zafin numfashinsa da kaurin kishirwar jini da ke tashi daga gare shi...
"Izzah tana da iyaka, Maayah," in ji Sarki, muryarsa tana fitowa daga can ƙasan makogwaro kamar gurnani...
"Kina tunanin don na ba ki damar fita school, hakan yana nufin kin fi ƙarfin umarnina? Jami'in tsaro na ya zo gare ki, amma kika ce sai kin ga dama? Shin kin manta cewa ni ne na gina wannan masarautar da jinina da kuma wannan fuskar tawa?"
Maayah ta fashe da kuka, "Don Allah Abul... kayi haƙuri. Ba nufina ke nan ba."
Sarki ya ɗago kansa, ya kalli dakarun tsaron da ke kewayen motar.
"Daga yau, an soke fitar Maayah makaranta na tsawon wata guda. Za ta zauna a ɓangarenta, kuma kowane malami zai zo har gida ya koyar da ita kamar sauran..."
Ya kalli direban da bodyguards ɗin,
"Ku mayar da ita ɓangarenta. Idan na sake jin ta nuna isa ga wanda na aiko, to zan tabbatar ta san cewa ni Zaki ne, ita kuma 'yar dabba ce a gabana!"
Sarki ya juya ya bar wajen, takunsa yana barin gurbin ƙafa a kan kwalta. Fadawa suka fara rarrafe suna mara masa baya, yayin da Maayah ta rage a durƙushe a tsakiyar titi, tana kuka mai ban tausayi, duk izzarta ta koma kaskanci a gaban kowa...
Bayan kora da aka yi wa Maayah, an mayar da ita bangarenta karkashin tsauraran matakan tsaro...
Tana zaune a ɗakinta, ta kalli kayan makarantar da aka hana ta saka, ta watsar da su gefe guda cikin fushi da takaici...
Washegari da safe...
Malami ya zo har gida domin koya mata, amma Maayah ta ƙi fitowa daga ɗaki. Tana jin kanta ya ragu, musamman yadda yanzu sauran ƴan uwanta za su riƙa yi mata kallon wadda aka hukunta...
"Mama Liyatu!" Ta ƙira da karfi...
Mama Liyatu ta shigo jiki na rawa. "Gimbiya, gani."
"Ki sanar da malamin nan ya tafi. Ba zan fito ba. Kuma ki tabbata babu wanda ya sake ambata sunana a gidan nan yau, idan ba haka ba zan sa a yanke harshen duk wanda ya yi hakan."...
Duk da Sarki ya hukunta ta, Maayah tana kokarin dawo da ragowar izzarta akan talakawa da masu aiki...
Amma a zuciyarta, tana tsoron ranar da za ta sake haɗa ido da mahaifinta mai fuskar Zaki...
Labarin abin da ya faru da Maayah ya isa kunnen Gimbiya Zayana...
Zayana tana zaune a nata sashen, wanda yake can nesa da kowa, cike da kamshin turaren na musamman...
Zayana tana kwance a kan wata gadon alfarma, tana wasa da wani kwarangwal ɗin zinare a hannunta...
Ɗaya daga cikin bayinta ta shigo tana sanar da ita abin da Sarki ya yi wa Maayah...
Zayana ta yi wata irin dariya mai sanyi, wacce take da amo kamar iska..
"Maayah yarinya ce. Tana tunanin izzah ita ce tafiya da bodyguards... Shi kuma sarki, yana tunanin fuskar Zakin nan tasa za ta tsoratar da kowa."..
Ta miƙe tsaye, tana taku cikin nutsuwa...
"Maayah ta yi kuskure da ta nuna rauni ta durƙusa...
Ni Zayana, babu ranar da zan durƙusa wa wannan fuskar ta Zakin. Idan ya yi kuskuren yi min tsawa, zan nuna masa cewa akwai abin da ya fi Zaki girma a daji...."
Ba zato ba tsammani, sai ga Sarki Nourdeen ya ƙariso sashen Zayana... Ya shigo ne da nufin ya gargade ta kamar yadda ya yi wa Maayah, domin ya ji labarin ita ma tana wuce gona da iri...
Sarki ya tsaya a ƙofar sashen nata, ya zuba mata wani irin kallo na kwarjini...
Amma Zayana ba ta ko tashi daga inda take ba, ba ta kuma sunkuyar da kai ba. Ta ƙura masa idanuwa waɗanda suka fara canza launi daga baki zuwa wani kalar ja mai duhu...
"Nourdeen,"
Zayana ta ƙira sunan mahaifinta kai tsaye ba tare da faɗin Sarki ko Abul ba....
"Kada ka kawo wannan gurnanin naka sashena. Ka riga ka sani, Ni na bambanta da sauran yaran gidann nan. Kada ka kuskura ka taɓa ikona."
Wani irin iska mai sanyi ya fara kaɗawa a ɗakin, har fitulun ɗakin suka fara disashewa...
Sarki Nourdeen, Zakin da kowa yake tsoro, ya ji jikinsa ya yi sanyi. Ya san cewa Zayana ba mutum ba ce kawai, tana ɗauke da wani abu da ya fi karfinsa...
Sarki ya ja numfashi, ya kawar da kansa. Ba tare da tsawatarwa ba ya ce,
"Zayana ki kiyaye. Iyakarki daban, tawa daban."
Sannan ya juya ya fita da sauri kafin ikon Zayana ya fito fili...
Zayana ta cigaba da zama, tana wasa da ƴar tsanar ƙwarangwal...
"Izzah ba hauka ba ne, Maayah. Izzah ita ce ka sanya kowa ya tsoraci ko da kallonka ne, har da wanda ya haife ka."..
Ta furta tana sakin murmushin gefen baki...
*SYDNEY*
A can nesa, a cikin wani babban bene mai kallon teku, Ruma tana zaune a kan kujerarta ta mulki...
Sanye take da tufa na alfarma, amma yatsunta suna sanye da wasu tsofaffin zobina. Babban cikinsu, wanda yake da wani baƙin dutse mai sheƙi, yana haskaka wani irin kore-kore...
Ruma ta murza zoben, tana rufe idanunta. Tana iya jin bugun zuciyar Zayana daga Alhamra...
Wannan zoben shi ne "remote control" na tausayin Zayana, muddin yana hannun Ruma, Zayana ba za ta taɓa sanin ma'anar jinƙai ba...
"Nourdeen," Ruma ta yi murmushin mugunta...
"Kana tunanin ka raba ni da ɗiyata? Ka riƙe gangar jikinta, amma ni ina riƙe da ruhinta da tausayinta. Duk sanda kake tunanin kai Zaki ne, ka sani cewa ɗiyarka tana da ikon murƙushe maka kwarangwal ɗin jikinka."
✨✨
A Masarautar Alhamra..
A daidai lokacin da Ruma ta murza zoben a Sydney, sai aka ga idanun Zayana sun ƙara yin ja wur a Alhamra. Wani irin kukan tsuntsu na daji ya tashi daga samfurin kwarangwal ɗin da ke hannunta...
_______________Maayah, wadda ke cikin damuwar hukuncin da aka yi mata, ta kasa daurewa. Ta yanke shawarar zuwa sashen Zayana, ko da yake tana tsoronta, tana tunanin ko za ta samu hanyar fita daga halin da take ciki...
Maayah ta isa ƙofar sashen Zayana, amma tun kafin ta shiga, wani sanyi ya ziyarci ƙashin bayanta..
Ta tura ƙofar a hankali, ta ga Zayana a tsaye, fuskarta babu ko ɗigo na ɗan'adamtaka...
"Me ya kawo ki nan, Maayah?"
Zayana ta tambaya, muryarta tana amo kamar tana magana ne daga cikin kabari.
"Kin zo ne ki yi kuka domin sarki ya nuna miki cewa ke ɗaliba ce kawai?"
Maayah ta haɗiye miyau, ta tsaya cikin izzarta ta ce,
"Ba kuka na zo yi ba. Na zo ne mu haɗa kai. Abul yana neman ya raina mu gaba ɗaya. Idan ya fara da ni, ke ce ta gaba."...
Zayana ta fashe da wata dariyar shakiyanci, ta taka har gaban Maayah...
Ta matsa da fuskarta kusa da ta Maayah har suna jin numfashin juna...
"Ba mu duka ba, Maayah... Ke aka raina. Ni, babu wanda ya isa ya gaya min yaushe zan fita ko yaushe zan zauna..... Ki fita daga sashena kafin na sa ki manta sunanki."..
Maayah ta ji tsoro ya fara ratsa ta, ta juya za ta fita, sai Zayana ta ƙira sunanta..
"Kuma ki gaya wa ma'aikaciyarki Liyatu, kada ta sake barin ƙafarta ta taka wannan sashen nawa. Domin bana buƙatar ko wani ƙazami, ke ma na raina tsabtar ki balle ita...."
Ba ƙaramin ƙuluwa Maayah tayi ba, haka ta share ta koma sashenta cikin fushi, tana huci...
Bayi da hadimai kowa ya rarrabe saboda yadda ta koro kowa da tsawa daga part ɗinta... Ta zauna a kan doguwar kujerarta ta alharir, tana kallon silin ɗakin nata...
"Meye ya kaini?"
Ta faɗa a fili cikin takaici...
"Meye ya kaini wurin Zayana? Don tana da wani sirrin kwarjini da kowa ke tsoro? Ni Maayah ce! Ni ce wadda kowa a International Elite School ke tsoro. Idan Abul ya hukunta ni yau, ba yana nufin na zama raunanniya ba."...
Ta cika da takaicin yadda ta nuna rauninta har ta tafi neman haɗin kai...
A gun Maayah, neman taimako ma kaskanci ne. Ta yanke shawarar cewa daga yau, ko da za ta dawwama a sashenta, ba za ta taɓa nuna wa kowa ba, musamman Zayana, cewa tana cikin ƙunci ba...
Ta ƙira Mama Liyatu...
"Mama Liyatu! Ki shirya min abinci mafi tsada, kuma ki ɗauko min sabon littafin nan na Royal Dynasties... Ina son na nuna wa duniya cewa ko a kulle nake, ni ce sarauniya."
Ita kuwa Zayana, tana nan zaune a daƙin da ko iska ba ta ratsawa sai da izininta. Ta san cewa Maayah ta tafi ne cike da takaici, kuma hakan daɗi yake mata...
A tunaninta, Maayah ba ta kai matsayin da za su haɗa kai ba,
ita Maayah tana izzah ne don tana da kyau da masoya, amma ita Zayana izzarta tana cikin jininta ne...
✨✨✨
Sarki Nourdeen yana zaune a babban falonsa, fuskarsa ta Zaki tana kallon hoton Ruma Mahaifiyar Zayana dake jikin bango. Ya daɗe yana kallon hoton, yana tunanin halayyar Zayana...
"Izzar Ruma ce take yawo a jikin Zayana," ya faɗa a ransa...
"Ba wani abu bane illa gado. Yadda Ruma take kallon kowa kamar kaskantacce, haka Zayana take. Ba zan taɓa mantawa da yadda Ruma ta tafi ta bar min wannan ragamar ba."
Sarki bai kawo a ransa cewa akwai wani tsafin zobe a Sydney da ke juya Zayana ba...
Ga shi, ganin cewa Zayana ba ta yi wa kowa tsawa ko yawo a fili kamar Maayah, sai ya fi jin kwarjininta....
A wurin Sarki, Zayana ita ce True Reflection ta mahaifiyarta, mace mai mulki da taurin kai...
👍 Like
🔁 Share
💬 Comment
*👑 MASARAUTAR ALHAMRA 👑*
_🪄 Gidan Mulki, Iko da Sirrin Zuciya 🪄_
✍🏽 By ASMEETAH WRITER
~Hasken Jajirtattu~
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
```JARUMAI WRITERS TEAM```
▶️ DON BIYO DAGA FARKO 👇
🔗 WhatsApp Channel:
https://whatsapp.com/channel/0029VbBCNlqJUM2RQwWncg43
📚 ArewaPen:
https://arewapen.com/u/asmeetahwriter
📖 Wattpad:
https://www.wattpad.com/user/asmeetahwriter
📲 Contact:
09065443871
📅 FARA TURA BOOK:
🔥 01 — 01 — 2026 🔥
📘 BOOK ONE
```MATAKIN FARKO```
CHAPTER 2️⃣1️⃣
*بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ*
King Diamond yana zaune a tsakiyar gadon Ayat, yana shaƙar ƙamshin turaren oud dake tashi daga jikin filon baccinta..
Fuskarsa dake ɗauke da annuri da kwarjini tana haskaka cikin duhun ɗakin. Ya kalli kansa a madubin da Ayat ta gama amfani da shi, ya ga yadda sumarsa fara sol ta dace da lallausan zanen gadon..
"Reems..." ya furta a hankali, yana jin daɗin yadda sunan ya dawo masa da rayuwa ta sanadin Ayat. Duk da raunukan dake jikinsa, sumbar da ta yi masa a goshi ta zama tamkar maganin da ya fi kowane maganin tsafi ƙarfi....
A can ƙasa a babban falon cin abinci, Ayat tana zaune ita kaɗai, an jera mata kalar abinci daban-daban na alfarma... Saratu tana tsaye a gefe tana yi mata hidima, amma hankalin Ayat baya kan abincin...
Tana tunanin Reems dake sama....kuliyar da ta yi amanna da ita...
"Saratu," Ayat ta ƙira muryarta a dake..
"Na'am ranta ya daɗe," Saratu ta amsa cikin ladabi..
"Ina son ki haɗa min wani abincin a ƙaramin kwanon zinare, ki kawo min shi... Kuma ina son madara mai ɗumi."
Saratu ta ɗan yi mamaki,
"Gimbiya, ko har yanzu yunwar ba ta ƙare ba ne?"
Ayat ta watsa mata kallo ɗaya ta cikin mayafinta, wanda ya sa Saratu ta sunkuyar da kai da sauri...
"Kiyi yadda na ce."
Da ta kammala cin abinci, Ayat ta ɗauki farantin da