Showing 111001 words to 114000 words out of 154131 words
Chapter 38 - Masarautar Alhamra Complete Hausa Novels By Asmeetah Writer.txt
Ayat...
Zuciyarta ta kusa fitowa daga ƙirjinta..
"Na shiga uku! Wanene za a kira a matsayina?" ta yi maganar zuci..
Lokacin da aka duba asusun gimbiyoyi aka ga kowa ya halarta banda ita, sai ga wata baƙar mota ta silalo ta fake..
Ƙirarin Gimbiya Ayat ne ya fara amo..
_"Tauraruwar Gabas! Farar wata dake haska sahara. Asalin Larabawa, ɗiyar gidan mutunci. Ayat, wadda fuskarta ke rufe da kwarjini da labule. Barka da isowa, sarauniyar zuciyar sarki!"_
Inuwa ya zabura, ya nufi fadar cikin sauri, Master Ibrahim ya biyo bayansa cikin mamaki. Suna isa ƙofar fadar, Inuwa ya ga wata mace ta fito daga motar, siffarta, tsayinta, da kayanta duka IRIN NA AYAT NE! Fuskar mace dake rufe da mayafi ta sa Inuwa daskarewa...
"Wannan wacece? Wacece wannan dake wasa da raina?" Inuwa ya tambayi kansa cikin tsoro da matuƙar mamaki. Master Ibrahim ya kalle shi, "Lafiya Inuwa?" Inuwa ya gyara muryarsa,
"Lafiya Master, kawai kwarjinin gimbiyoyin ne ya ba ni mamaki."
Sarki ya kalli gimbiyoyinsa guda huɗu dake zaune, ciki har da Ayat ta bogi. Ya gyara zama, muryarsa ta daka cikin fadar..
"Na ƙira ku ne don in bayyana muku wani sabon sauyi. Kun girma, kuma lokaci ya yi da zan muku aure. Amma sabanin al'adar gidajen sarauta, na yanke shawarar kowaccenku ta faɗi wanda take so..."
Yayin da Ayat ta bogi ta juyo da idanunta masu kama da na Ayat ta gaske, ta kalli inda Inuwa yake tsaye acan nesa da su. Ta yi wani ɗan gajeren murmushi dake bayyana ta cikin mayafin fuskarta..
Zayana ce ta ce,
"Wani irin mijin aure bayan ba ma fita ko ina?..."
Sarki ya sanar musu cewa..
"To ni zan nema muku da kaina..."
Zaku cigaba da tsare har lokacin auren ku...
Ya sanar dasu cewa zai tura saƙo ga ko wani sarakunan yanki mabanbanta, da su nemawa ƴaƴansu maza auren gimbiyoyinsa...
Kaf gimbiyoyin jin haka, babu wanda ya nuna farin ciki a cikinsu,
Bayan sarki ya bayyana nufinsa na yi musu aure da ’ya’yan sarakuna, fadar ta yi tsit. Zayana, wadda ko a gaban sarki ba ta tsoron magana, ta gyara zama, fuskarta cike da nuna rashin amincewa...
"Abul, kayi haƙuri ka cire ni a wannan batun," Zayana ta faɗa cikin muryar isa..
"Domin ni akwai wanda nake jira. Da zarar ya bayyana zan yi aure, wato uban yarinyata Mimi."
Nan take fuskar sarki ta canza kalar, idanunsa suka yi jajur. Maganar Mimi da asalin mahaifinta babban rauni ne ga masarautar Alhamra, domin babban abin kunya ne da Zayana ta janyo masa. Amma ko a jikinta, domin ta san sarki ba zai iya kashe ta ba...
Sarki ya daka wata tsawa wadda ta girgiza dandalin fadar...
"Ya isa haka! Babu wata gimbiya da ta isa ta bijire wa umarni na. Maganar wancan mutumin ta ƙare tun ranar da kika janyo wa wannan masarautar abin kunya. Dukkan ku, ku koma sashen ku! Nan da kwanaki kaɗan zan aike da saƙo ga dukkan sarakunan yanki."
Kowace gimbiya ta tashi tana sosa ƙeya, Maayah da Yumna sun tafi cikin sanyin jiki, yayin da Zayana ta fice tana huci.
Ayat ta bogi ta miƙe cikin nutsuwa, tana taku ɗaya bayan ɗaya kamar yadda Ayat ta gaske take yi..
Inuwa dake tsaye kusa da Master Ibrahim, idonsa ya bushe, yana kallon yadda wannan matar take tafiya.
Inuwa ya kasa haƙuri, ya raɗa wa Master Ibrahim..
"Master, me suka tattauna a ciki? Ina ganin gimbiyoyin duka fuskokinsu babu annuri."
Master Ibrahim ya ja numfashi, "Sarki ne ya yanke shawarar ba da aurensu ga ’ya’yan sarakuna. Inuwa, kaga wannan gimbiyar dake ƙarshe? Ita ce Gimbiya Ayat. Mutane suna cewa tana da sanyi, amma tana da kwarjini a tare da ita domin kusan ta fi su..."
Inuwa ya kusan suman tsaye, "Idan sarki ya ba da aurena, wa za a kai gidan miji? Ni ko wannan matar?" Ya yi maganar zuci cikin matuƙar tashin hankali.
Suna fita daga fadar, Inuwa ya ga Ayat ta bogi tana shirin shiga motarta. Inuwa ya yi maza ya nemi izini wurin Master Ibrahim akan zai je ya duba wani abu a sashen tsaro, amma a gaskiya bin motar zai yi..
Yana isa kusa da motar, Ayat ta bogi ta zuro da kanta ta window, ta kalli Inuwa shi kuma yana cikin kakin PA.. Ta yi masa wani kallo mai zurfi, sannan ta raɗa..
"Kada ka ji tsoro, Inuwa.... Inuwa baya iya rayuwa ba tare da jikin da yake ba shi inuwar ba."
Ta ɗaga masa hannu, direban ya tada mota suka bar wurin. Inuwa ya daskare a tsaye. Wannan muryar... ya sani sarai ba muryar mace ba ce ta gaske ba..
Kowace gimbiya ta koma sashenta da damuwa..
Zayana tana huci tana shirin kiran mahaifiyarta don sanar mata da wannan auren...domin tasan ba ta sani ba..
Maayah kuwa tana kuka domin ta fi son karatu da makarantar da take zuwa fiye da zaman gidan miji...kuma ba ta jin a ransa zata rayu da ko wani namiji in ba Inuwa ba, ga damuwar Uncle Jalal da ya sako ta a gaba, yasa duk ta zubar da ƙimarta a gaban aji, a yanzu tana ɗaukan kanta ne a matsayin mutum-mutumi....
Yumna kuwa duk da tana matuƙar ƙaunar malamin da yake zuwa koyar da ita ba tare da ya sani ba amma tana addu'ar Allah ya ba ta mijin da zai so ta don Allah....
Shi kuma Inuwa, yana tsaye a tsakiyar fili, ya rasa inda zai dosa.
Ba tare da ɓata lokaci ba ta isa sashensa na gimbiya cikin sassarfa, zuciyarsa na bugawa tamkar za ta fito...
Ya lallaɓa ta ƙofar sirri ya shiga ɗakinsa na ciki, inda ya tarar da waccan siffar tana zaune a gaban madubi, tana gyara mayafin fuskarta...
Inuwa ya watsa wa wannan siffar kallo mai cike da tsoro da tambayoyi...
"Wacece ke? Kuma waye ya ba ki izinin shiga siffata?"
Waccan Ayat ta bogi ta tashi tsaye a hankali. Takun ta, kamshinta, har ma da kalar idonta duka na Ayat ne.. Ta matso kusa da shi, sannan ta yi wata dariya mai sanyi, muryar King Diamond ta fito fili..
"Na gaya miki, Inuwa ba ya rayuwa idan babu jikin da yake ba shi inuwar... Idan ban bayyana a fadar nan ba, da yanzu Master Ibrahim da Sarki suna nan suna neman inda Gimbiya Ayat take..."
Ayat cikin kakin Inuwa ta zauna a ƙasa cikin sanyin jiki...
"Diamond, me kake shirin yi? Sarki ya ce zai ba da aurenmu. Idan ya kawo miji, wa zai aura? Kai ko ni?"
Diamond wanda yake cikin siffar Ayat, ya sunkuyo ya kalle ta...
"Ke za ki ci gaba da zama Inuwa, ki gina ƙarfi da ikon da kike buƙata don gyara masarautar nan. Ni kuma zan riƙa zama Gimbiya Ayat a duk lokacin da bukatar hakan ta taso... Game da maganar aure kuma... babu wanda ya isa ya aure ki muddin ina raye...
Ayat ta rufe fuskarta da hannayenta...
"Wannan hauka ne! Idan aka gano mu, kisa ne hukuncinmu."
Diamond ya yi murmushin raini...
"Kisa? Ni ne mutum na farko da aka taba kashewa amma ban mutu ba, Ayat. Ki kwantar da hankalinki..."
Bayan ɗakin ya yi shiru, Diamond ya saki siffar Ayat, hayaki ya rabe, ya koma asalin sa na King Diamond. Dogon namiji, kyakkyawa mai kwarjini, wanda kallo ɗaya zaka masa kasan ba mutumin banza ba ne...
Ayat ta miƙe tana kallon sa, kirjin ta na bugawa. Ganin yadda ya sadaukar da kansa ya shiga siffar mace don kawai ya kare mutuncinta a gaban Sarki, ya taɓa zuciyarta sosai. Ba tare da tunanin komai ba, ta fada kirjin sa, ta kankame shi tana kuka mai karfi...
Diamond ya rungume ta, ya dora habar sa a kanta, yana shakar kamshinta wanda ya dade yana mafarkinsa...
"Kiyi shiru Ayat," ya rada mata cikin murya mai daɗi..
"Babu wanda ya isa ya raɓe ki da sunan soyayya muddin ina raye. Ko Sarki ya aiko da sarakuna dubu, ke tawa ce, kuma ni naki ne. Ke ce zuciyata..."
Ta ɗago kanta tana share hawaye, ta kalle shi sama da ƙasa sannan ta fara bugun kirjin sa da kananan hannayen ta cikin sigar wasa da shagwaba...
"Ka samu matsala, Diamond! Taya mutum da aljani zasu yi aure? Allah ya kiyaye na auri aljani... cab! Ni mutum nake so, ba wani wanda yake narke wa ya zama hayaƙi ba," ta fada tana kukan dake gauraye da shagwaba...
Diamond ya tsaya yana kallon ta, wani irin murmushi ya subuce masa. Ya daga kafada irin na mutanen da suka san abin da suke yi...
"Aljani ko mutum, ni dai na san ke tawa ce. Idan lokacin ya yi, zaki gane cewa ba kowanne hayaƙi ba ne yake ƙonewa... wasu hayakin suna bayar da inuwa ne..."
Diamond ya koma gefe ya zauna a bakin gadon ta, ya miƙa mata hannu...
"Maganar wasiƙun Sarki kuma, ki kwantar da hankalinki. Ko ya tura su, ba za su taba isa inda aka dosa ba ga sunanki. Zan tabbatar an aurar da sauran, amma ke Ayat, zaki kasance cikin masarautar nan har sai ranar da zan zo daukarki a matsayin Sarauniyata..."
Ayat ta dan yi shiru, tana kallon fuskar sa da ta yi mata kwarjini. Akwai wani abu game da Diamond dake tunatar da ita Reems, amma tana ganin hakan ba zai taba yiwuwa ba tunda Reems mutum ne kuma tana tunanin ya daɗe da mutuwa...
"Yanzu ki huta," Diamond ya ce mata. "Gobe Inuwa yana da aiki babba a gaban sa. Sarki zai bukaci ganin PA ɗinsa... Ki zama jajirtacciya kamar yadda kika saba."
Ayat ta jinjina kai, tana jin wani irin kwanciyar hankali da ba ta taba ji ba tun bayan rasuwar mahaifiyarta. Tana jin cewa koda duniya zata juyo mata, tana da Aljani dake shirye ya yaƙi kowa don ita...
Ta buɗe baki cikin gaggawa kafin ya ɓace ta ce,
"Yauwa, ta ya kai shigo Masarautar nan alhalin a tsare yake?..."
Murmushi kawai Diamond yayi sannan ya ɓace ba tare da ya ba ta amsa ba....
*Likes ɗinku shine albashin marubuci*
👍 Like
🔁 Share
💬 Comment
*👑 MASARAUTAR ALHAMRA 👑*
_🪄 Gidan Mulki, Iko da Sirrin Zuciya 🪄_
✍🏽 By ASMEETAH WRITER
~Hasken Jajirtattu~
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
```JARUMAI WRITERS TEAM```
▶️ DON BIYO DAGA FARKO 👇
🔗 WhatsApp Channel:
https://whatsapp.com/channel/0029VbBCNlqJUM2RQwWncg43
📚 ArewaPen:
https://arewapen.com/u/asmeetahwriter
📖 Wattpad:
https://www.wattpad.com/user/asmeetahwriter
📲 Contact:
09065443871
📅 FARA TURA BOOK:
🔥 01 — 01 — 2026 🔥
📘 BOOK ONE
```MATAKIN FARKO```
CHAPTER 3️⃣1️⃣
*بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ*
A cikin wadannan kwanakin, Inuwa ya ƙara karfi a idon jami'ai. Ya fara gabatar da sabbin dokoki na sassauta wa fursunoni, wanda Master Ibrahim ya amince da su saboda hazaƙarsa. Inuwa ya zama kamar wani Yariman Ofis, domin kowa girmama shi yake yi...
Bayan kwana biyu da taron fada, Inuwa yana kokarin tantance wasu takardu a ofis, sai ga wata kuyanga daga sashen Gimbiya Maayah ta iso. Ta miƙa masa saƙo a boye..
_"Inuwa, ina bukatar ganinka yanzu a lambun dake bayan sashena. Rayuwata tana cikin hadari."_
Inuwa ya firgita, yana tunanin ko wani abu ne ya faru da Maayah, don haka ya nufi can da sauri.
Yana isa lambun, ya iske Maayah tsaye a bakin bishiyoyin flawa, fuskarta duk hawaye. Tana ganin sa, ba ta jira komai ba ta rugo da gudu ta faɗa jikinsa, ta kankame shi tana kuka mai cin zuciya..
Inuwa ya daskare! Jikinsa ya fara rawa, domin a matsayinsa na mace, bai saba da irin wannan kusancin da wata mace ba. Ya tsaya da hannayensa a sama, ya rasa inda zai sa su...
Da kyar, cikin dabara da karfi, Inuwa ya janye jikinsa daga nata, ya raba rungumar..
"Gimbiya, me ke faruwa? Kin san matsayina, kuma kin san idan aka gan mu a haka kisa ne hukuncina,"
Inuwa ya fada cikin muryar jami'ai dake rawa..
Maayah ta kalle shi da kyawawan idanunta wanda yake cike da hawaye.
"Inuwa, ba zan iya ba! Sarki yana shirin aurar da mu ga sarakunan da ba mu sani ba. Ni kuma zuciyata ta daɗe da ficewa daga kirjina ta koma gare ka."
Ta sake kamowa hannunsa, "Inuwa, tun ranar da na fara ganinka, nake jin wani abu daban. Ni ba na son kowa, ba na son sarauta, kai kadai nake so. Dan Allah ka ce wani abu!"
Ayat dake cikin kakin Inuwa ta ji kamar ƙasa ta tsage ta hadiye ta. Tana jin tausayin Maayah, amma tana jin wani irin kishi na daban domin ita ma tana da nata ra'ayin akan kanta... Ta san cewa wannan soyayyar ba za ta taɓa yiwuwa ba..
"Gimbiya Maayah," Inuwa ya ƙira yana kau da kai. "Ni bawa ne, ke kuma gimbiya ce. Haka kuma, akwai abubuwa da yawa game da ni da ba ki sani ba. Wannan soyayyar... haɗari ce gare ki."
Maayah ta ƙara sautin kukan ta...
"Babu wani haɗari da ya wuce a raba ni da kai... Idan har ba za ka aure ni ba, gara na mutu kafin ranar da wasikun sarki zasu bar fadar nan!"
Ta ƙara matso kusa da shi tana nuna ƙirjinta...
"Inuwa, na kamu da matsananciyar ƙaunarka. Idan har ba za ka ce kana so na ba, ko kuma ba za mu kasance tare ba, to gara rayuwata ta ƙare a nan."
Inuwa ya ji wani irin nauyi a ransa. Tausayin Maayah ya kama shi, musamman ganin yadda take kuka kamar ranta zai fita. Ya tsaya yana kallonta, ya rasa ta ina zai fara gaya mata cewa wannan burin nata ba zai taɓa cika ba, kuma ba zai iya son ta yadda take so ba..
Maayah ta ci gaba da kukan ta, tana roƙonsa, tana jiran ya ce wani abu da zai kwantar mata da hankali kafin lokacin wasiƙun Sarki ya yi...
Inuwa ya ja numfashi mai nauyi, idanunsa suka sarƙe cikin na Maayah dake zubar da hawaye. Ganin yadda gimbiyar ta duƙa gwiwowinta a ƙasa tana kuka, ya sa ya ji cewa idan bai faɗi wani abu ba yanzu, za ta iya aikata abin da zai tona asirinsu duka..
Hakan ya sa ya sunkuyo, ya kama kafadunta ya ɗago da ita a hankali.
Inuwa ya saita muryarsa ta yadda za ta ratsa zuciyar Maayah, ya dube ta cikin natsuwa...
"Gimbiya Maayah, ya isa haka. Share hawayenki," ya faɗa cikin muryar lallashi...
"Na ji duk abin da kika faɗa, kuma ba zan zura ido in ga an kai ki gidan da ba kya so ba. Ki kwantar da hankalinki, ba za a tura wasiƙar aurenki ba."
Maayah ta tsagaita kukan, ta kalli Inuwa cike da faduwar gaba da bege..
"Inuwa, da gaske kake? Za ka iya hana Sarki?"
Inuwa ya ɗaga kai, koda yake a ransa ya san cewa yana yin wannan alkawarin ne domin ya kare kansa daga wannan auren, amma ya nuna wa Maayah cewa domin ita ne..
"Ke kanki kin sani ni ne PA na Master Ibrahim. Ni ne zan karɓi wasiƙun nan, kuma ni ne zan miƙa su ga ƴan aike. Zan yi dabarar da zan bi in tabbatar da cewa takardar aurenki ba ta bar masarautar nan ba. Amma ki yi min alkawari guda ɗaya..."
Maayah ta share fuskarta da sauri, "Komai ka ce zan yi, Inuwa!"
"Kada ki sake nuna wa kowa damuwarki. Ki koma sashenki, ki zama kamar ba abin da ya faru. Idan Sarki ko kowa ya ga kina murna ko kina cikin natsuwa, ba za su yi zargin komai ba. Ki bar min sauran aikin, zan yi duk yadda zan yi in ga na dakatar da wannan auren."
Jin wannan maganar daga bakin Inuwa ya sanya Maayah jin kamar an sauke mata dutse a kanta. Ta yi murmushi cikin hawaye, ta so ta sake rugowa ta rungume shi, amma Inuwa ya yi saurin yin taku ɗaya baya...
"Yanzu ki tafi, Gimbiya. Kada a gan mu a nan."
Maayah ta gyada kai cikin farin ciki, ta juya tana tafiya tana waigensa, tana jin cewa yanzu ta samu jarumin da zai cece ta.
Inuwa ya tsaya yana kallon yadda take tafiya cikin farin ciki. Ya sauke wata nannauyar ajiyar zuciya, yana jin nauyin karyar da ya yi mata a kansa..
"Kiyi haƙuri Maayah," ya yi maganar zuci...
"Ba don ke nake wannan aikin ba, don kaina nake yi. Amma tunda hakan zai cece mu duka, zan yi iya ƙoƙarina..."
✨
Washegari, Inuwa yana cikin sashen Master Ibrahim yana nazarin wasu takardu, sai ga bawan Gimbiya Zayana ya sake bayyana... A wannan karon ma, katin gayyar ya fi na farko tsada, kuma akwai wani akwati ƙarami na zinare dake rakiya da katin..
"Ranka ya daɗe," bawan ya faɗa yana gaisuwa..
"Gimbiya Zayana tana nemanka yanzu a sashen fita na lambun ta na sirri. Tana son tattaunawa akan makomar masarautar nan."
Inuwa ya san cewa ƙin zuwa zai iya janyo masa zargi, don haka ya nufi sashen Zayana. Ya tarar da ita tana tsaye a cikin lambun ta, sanye da wata doguwar riga mai kalar ruwan gwal. Fuskarta yau tana nuna annuri, sai dai wani irin murmushi take na maƙirci...
"Inuwa, na san ranar na ɓata maka rai," Zayana ta fara magana cikin sanyin murya...
"Amma maganar da Sarki ya yi, ta sa na gane cewa kai ne kaɗai za ka iya taimaka min.. Kuma idan ka taimaka min, zan mayar da kai mafi kuɗi a duk dakarun Alhamra."
Inuwa ya tsaya, hannuwansa a baya, fuska babu annuri...
"Ina saurarenki, Gimbiya."
Zayana ta matso kusa, muryarta ƙasa-ƙasa..
"Ka san Sarki ya bayar da umarnin a tura saƙo ga sarakuna don neman aurenmu. Ni kuma ba zan taɓa auren wani sarki ba! Ina so ka yi amfani da matsayinka na PA, ka canza wasiƙar da za a tura wa Sarkin yankin da aka nufa da ni. Ka sa a rubuta cewa 'Zayana ba ta da lafiyar da za ta iya zama matar aure'. Ko kuma ka ɓatar da wasiƙar gaba ɗaya."
Inuwa ya ji zuciyarsa ta buga. Wannan dama ce ta kusa-da-kusa don ya san yadda zai ɓatar da tasa wasiƙar ma. Amma dole ya nuna taurin kai don kada Zayana ta yi zargin wani abu...
"Gimbiya, kin san hukuncin canza wasiƙar Sarki? Kisa ne," Inuwa ya faɗa..
Zayana ta yi dariya, ta buɗe wancan akwatin zinaren, cike yake da duwatsu masu daraja (diamonds) da zinare..
"Wannan na farko ne. Idan ka yi nasara, zan ba ka ninkin wannan. Kuma zan tsaya maka a gaban Master Ibrahim ya ƙara maka matsayi. Idan kuma ka ƙi..." Ta ɗaga kanta, idanunta suka yi shanye,
"...zan gaya wa kowa cewa ka shigo mun har ɗaki ba tare da izini ba, kana nemana da lalata...."
Inuwa