Showing 6001 words to 9000 words out of 154131 words
Chapter 3 - Masarautar Alhamra Complete Hausa Novels By Asmeetah Writer.txt
so ta cire konkonto a zuciyar mai ɗinki sai ta ce da ita,
"Ina so zanyi kyautarsu ne, zan aika wa wani zai fara aiki a wannan masarautar domin an gama masa interview..."
Jinjina kai mai ɗinkin tayi tana murmushi sai yanzu ta gamsu..
AYAT ta cigaba da tsara ma'aikatanta gaba ɗaya, tana neman kayan dabaru ɗaya bayan ɗaya.
Ta ƙira mai gyaran kai ta ce,
"Ina so a koya mun yadda ake haɗa rawani domin na ga yanda Jaruman Fada ke yi..."
Mai Gyaran kai ya yi mamaki amma bai yi tambaya ba saboda Gimbiyar ba a tambayarta abinda take son yi...
Hakan kuwa ma'aikacin ya koya mata a jikin wani gunki a cikin part ɗinta..
Bayan ya gama naɗawa a kan gunkin sai ta buƙaci ya bar shi a kan gunkin kawai..
Bayan ya tafi sai ta zaro ɗaurin rawanin a kan gunkin yanda bazai warware ba domin ba ƙaramin naɗi akayi ba....just zata rinƙa ɗorawa ne akanta ba tare da ya warware ba....
Daga baya ta sa aka kawo mata mai kula da takalman jarumai..
Ta ce da shi.
"A kawo min takalmin jarumai guda ɗaya... domin na lura suna da inganci, ma'aikacina nashi ya daɗe da lalacewa amma bai samu an bashi wani ba har yanzu..."
Mai kula da takalma ya ce, "Gimbiya ai duk wani jami'in fada da ya lalata takalminsa to siya wani yake da kuɗin aljihunsa idan aka bashi na farko kyauta..."
Gimbiya ta ce, "har nawa ne kuɗin?.."
Ya ce, "ai gimbiya kuɗin da yawa, zai kai 150k..."
Tayi murmushi sannan ta ce, "amma sarki ya san da hakan?.."
Ya sunkuyar da kai a ɗan tsorace ya ce, "Gimbiya wannan ne sana'ar mu a cikin fadar nan, ko wani jami'in da yake kula da abubuwa to kafin ya bada sai ya karɓi kuɗi...."
Gimbiya ta ce, "amma ku kuka siyo abubuwan da kuke sayarwa ko Masarauta ce ta bada ?.."
"Masarauta ne Gimbiya kuma sarki bai sani ba..."
"Cin hanci kenam? Masarauta ta bada abu akan duk wanda nashi ya lalace a bashi ya cigaba da amfani da wani amma ku kuke sayar musu, baku da jari amma kunada riba, to ku sani duk abin da kuke yi zan aikawa sarki..."
A take mutumin ya durƙusa yana roƙon gimbiya...
Gimbiya ta ce, "shin albashin da ake baku duk wata baya isar ku ne?.."
Cikin kuka ya ce, "wallahi wadatacce kuɗi ake bamu sosai, amma zamu daina karɓan kuɗin kowa, a gafarce mu..."
Gimbiya Ayat ta jinjina kai sannan ta ce, "kada na sake ji to, kuma ka je ka kawo mun takalma sawu biyu..."
A ruɗe ya miƙe yana faɗin. "Insha allahu za'a kawo a yanzu..."
Ayat tayi tunanin takalmin ma'aikacinta ma ya lalace shiyasa yanzu ta buƙaci sawu biyu, na ta da kuma nashi..."
Ba da jumawa ba, ya kawo mata "Sample" na takalmin maza...
Ta karɓa tana bashi umarnin akan ya samo mata belt na ɗamara..
Nan ya je ya samo mata.
Bai san cewa, tana tara dukkan kayayyaki ne a sirri don ta kammala shirin rikidewarta ba!
Yanzu sauran gyara murya..
Wannan shine mafi wahala kuma mafi haɗari a cikin shirinta.
Gimbiya ta kalli fim ɗin da ta gani sau 3 tana nazarin yadda mace take rage murya ta zama ta namiji. Sai ta fara gwaji a gaban madubi a cikin shurun daren part ɗinta...
"Assalamu alaikum..." ta furta too Weakly. Ta girgiza kai...
"Alaikumus salam..." muryarta ta yi tsayi High-pitched. Ta sake girgiza kai.
Sai ta ɗan saki numfashi mai zurfi, ta ɗan yi ƙasa kaɗan da muryarta, tana dannewa...
"Alaikumus salam..." Wannan lokacin murya ta yi laushin mace, amma kuma yayi kamar na namiji mai natsuwa da Izzah..
Ta yi murmushi ta kaɗa kai. Da wannan zan iya ratsa ko'ina... ba wanda zai gane.
Haka ta yi ta atisaye kusan rabin dare har sai da muryar ta ta kama tsarin da take so...
✨✨✨
Washegari kuma tana koyon tafiyar namiji...
Haka take ta fafatawa a cikin bedroom ɗinta..
Da farko, tafiyarta, tafiyar mace ce sosai ƙugunta na rawa, ƙafa tana sauƙa da salo irin na Sarauta.
Ta tsaya, ta rage, ta daidaita, ta danna ƙafarta ƙasa da ƙarfi.
Ta saita ƙafar daidai yanda baya ɗan tashi, tana banƙare ƙirji, jiki a sake....
Ta fara tafiya kamar takun raƙumi..
Nan ta sauƙe ajiyar zuciya domin ba ƙaramin gajiya tayi ba..
Sai kuma ta ɗauko kayan jaruman fada ta saka a jikinta tana gwada tafiyar da kayan har zuwa ƙasin falonta...
Ƴan bayinta suna kallo suna mamakin ganinta a haka, suka ce
"Gimbiya me kike yi haka?"
Bata ce komai ba face,
"Ina gwajin salon tafiya ne kawai."
Sun bar ta, suna tunanin wata yar wasan kwaikwayo ce ta taso mata..
Amma ita a zuciyarta tana maganar ciki, "dole na yi kamar maza... ina buƙatar in ratsa ƙofa babu zargi..."
Ta ƙara komawa can saman bedroom da kalar tafiyar maza...A wannan ranar kwana tayi tana atisayen tafiyar maza..
Ta gama shirin atisayenta. Yanzu abinda ya rage mata shine yanda zata sa a kawo mata kayan Concealer na yanda zata saka gashin baki da gemu..
Nan ta ƙira wani ma'aikacinta wanda ya kawo mata finafinai ta sanar masa, cewa.
"Ina so ka kawo mun design na gashin baki da gemu da kuma saje domin ina son gwajin sabon salon fim da na kalla..."
Ma'aikacin ya yarda da hakan domin Gimbiya ba ta taɓa tambayar abu mai kama da haka ba. Sun ɗauka sabuwar sha'awa ce kawai...
Amma ita a zuciyarta ta gama tattara komai, kayan maza, rawani, belt, takalma, riga, murya, tafiya, gashin baki, gemu... duk sun cika shirin ta.
Cikin dare Gimbiya Ayat ta tsaya a gaban madubi. Hannunta na ɗan rawa, zuciyarta na bugawa fiye da yadda ta taɓa ji a rayuwarta. Ta shimfiɗa kayan jaruman maza a gabanta..
"Zan iya... dole na iya," ta furta a hankali, tana ƙarfafa zuciyarta.
Ta fara da faɗaɗden belt na matsin ƙirji mai matuƙar Ƙarfi. Ta ɗaure ƙirjinta da belt mai faɗi, domin ta rage nauyin nonuwanta da kuma gyara surar ta zuwa madaidaicin namiji.
Sai da ta yi ƙasa da numfashi, tana jin matsa da zafi mai yawa. Zafin ya yi yawa har hawaye suka taru a idonta..
"Da haka maza ke ji?" Ta yi murmushin wahala da azaba...
Bayan ta ɗaure, ta saka wandonsu na maza wanda ya yi mata nauyi, ya yi mata tsawo, sai ta ɗaura Belt ɗin ɗamara kamar yadda ta gani a fim..
Sannan sai gashin baki da ɗan gemu da ta ƙirƙiro. Ta mamanna su da ruwan gam, ta ƙara musu tinti da ƙananan launin ruwan ƙasa da take amfani da shi a eyebrows ɗinta. A hankali ta manna zuciyarta na bugawa..
"Na fara zama wani daban," ta furta...
Ta miƙe yadda maza ke miƙewa da ƙarfi. Ba tare da ta ɗaga ƙafa sosai ba, sannan ta daidaita jujjuya kugun dake ta matse su sosai. Salon ta ya canza zuwa na ɗan daudu..
Ta ɗaga ƙafa kaɗan. Ta yi tafiya a ƙetare cikin ɗakin. Sai ta sake dawowa.
"Ya kaji? Kamar namiji?" Ta yi tambayar da ba wanda zai amsa.
Ta yi tari don buɗe makogwaro. Ta sauƙe numfashi ƙasa..
"Ee... kai... Kawo dukkan tawagar nan zuwa ƙofar Masarauta," Ta yi ƙoƙarin yin muryar maza...
Wani dariya ya kuɓuce mata...dariyar mace.
"No! Muryar mace ce!"
Ta ƙoƙarta. Ta sake gwadawa. Sai ta yi ƙasa da murya..
"...ka... kawo tawagar nan..."
Cikin daren nan take ta maimaitawa, har sai da muryarta ta fara tsuke wa kamar namiji maai shekaru 18–20..
Ta janyo rawanin da ta ɓoye. Ta ɗora shi a kai. Ya rufe mata gashin kanta wanda ya daɗa nuna Izzah.
Ta tsaya. Madubi ya nuna wani Sabon Mutum..
A gaban madubi wani saurayi tsaye mai shekaru 20 ne, siriri, mai ɗan gashi a ƙasa da baki da kwantaccen saje..
Zuciyarta ne ya yi wani irin tsalle cikin bugawa, dũkan da har ta ji a kunne..
"Na zama wani... amma ba zan iya janye wannan ba," ta faɗa cikin murya mai zurfi..
Da sassafe, bayan bayinta sun tabbatar da tana cikin ƙoshin lafiya, duk ta sanar da su cewa.
"Yau bana buƙatar ganin kowa. Duk wacce ta shigo yanda nake hutawa sai ta fiskanci ukuba."
Duk sun jinjina kai tare da bin umarninta..
A wannan lokacin ne da ta san an yi mata ƙofa ta Aminci, ta kulle ɗakinta yanda za'ayi tunanin tana ciki. Ta bi hanyarta ta sirri ba tare da kowa ya ganta ba ta fice... A cikin lambun da take fita ta fice..
Haka take tafiya a hanyar masarautar da ta miƙe zuwa can yankin babban fertility ɗin Masarautar...
(Center of the Kingdom)..
```DAN ALLAH KUYI MUN ADALCI🙏 KAMAR YANDA NA BAKU LOKACI NA DON NA FARANTA MUKU, KU MA KUYI ƘOƘARIN SANYA NI CIKIN FARIN CIKI 🙏🙏🙏```
```LIKES ƊINKU SHINE ALBASHIN MARUBUCI```
👍 Like
🔁 Share
💬 Comment
*👑 MASARAUTAR ALHAMRA 👑*
_🪄 Gidan Mulki, Iko da Sirrin Zuciya 🪄_
✍🏽 By ASMEETAH WRITER
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
```JARUMAI WRITERS TEAM```
⚠️ SANARWA⚠️
Wannan littafi dukiyata ce a matsayina na marubuciya.
⚖️ Ba a yarda wani ko wata ya:
kwafa
gyara
sauya
ko amfani da wani sashe na wannan labari
ba tare da izini na kai tsaye ba.
Duk wanda ya saɓa, alhaki yana kansa..
▶️ DON BIYO DAGA FARKO 👇
🔗 WhatsApp Channel:
https://whatsapp.com/channel/0029VbBCNlqJUM2RQwWncg43
📚 ArewaPen:
https://arewapen.com/u/asmeetahwriter
📖 Wattpad:
https://www.wattpad.com/user/asmeetahwriter
📲 Contact:
09065443871
📅 FARA TURA BOOK:
🔥 01 — 01 — 2026 🔥
📘 BOOK ONE
```MATAKIN FARKO```
CHAPTER 3️⃣
*بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ*
Bayyanowar ta cikin babbar masarauta...
Tana haɗuwa da tawagar ɗaiɗaya amma babu wanda yayi tunanin Gimbiya ce. Tana ƙoƙarin wurin daidaita tafiyarta kamar namiji, domin tana ganin yanda sauran suke yi.
Sai ga wani tsararren mota cikin Masarauta ya tsaya a gefenta. Kirjinta ya yi wani irin bugawa sosai, ta ɗauka an ganota ne. Sai ta ga ɗaya daga cikin Security ne mai jan mota, ya ce da ita.
"Ya! Mutumin hau na rage maka hanya zuwa can Center ɗin Masarautar mana..."
Ayat ta shiga cikin gaggawa, amma jikinta yana ɗan nuna gajiyawa irin bata saba ba saboda matsin ƙirji.
Security ya kuma cewa.
"Kana daga cikin tawagar da zasu fita ne?"
Ayat tana fargaban magana saboda kar ya ganota ta murya duk da tayi training. Tayi shiru.
Security ya ce, cikin ɗan tsawa.
"Kai ɗan rainin wayo, ina magana kana mun shiru, in ban jefar da kai ba!"
Ayat anan ta tsorata, ta daidaita muryar ta mai sanyi.
"Amm... Dani za'a fita..."
Security ya ce
"Yadai naji muryarka haka, kodai mura kake?"
Haka suka kasance har suka isa Center of the Kingdom. Ayat tana ta wara idanuwa tana ganin tsararrun abubuwan da suke cikin Masarautar nan. Tana tunanin daman haka Masarautar nan take da girman gaske?
Dai-dai lokacin da suka isa, yanda wasu tawagar suke shirin fita daga Masarautar.
Ayat ta sauƙa tana zazzaro ido cike da bege. Ta shiga cikin tawagar da suke ƙoƙarin fita outside ɗin Masarauta.
Suna fita daga cikin Masarautar, ta yi wani irin ajiyar zuciya mai tsayi wanda ya fito daga tsakiyar zuciyarta.
Iskar waje ne ya buge ta a fuska!
Iskar da ta daɗe tana mafarkin ji, shekaru ashirin da biyar tana zaton yanda duniyar waje take. Hawaye ne ya gangaro daga idonta...
"Duniya... ga ni."...
Ta furta cikin ƙarƙashin maƙoshinta..
AYAT tana ta fargaba yanda kayan suka matse ta da kuma tsoron ko wata dabara zata warware. Bayan ta tsallake gwaji na farko na mai motar tsaro, ta sulale ta bar cikin tawagar tsaron, ta tafi yawonta a ɓoye.
A ɓoye ta ɗauki dokin ɗaya daga ciki, ta zagaya bayan Alhamra wurin da babu wanda ke zuwa. Anan ta tarar da wani kogi mai kyau da wurin gudanar ruwa mai zurfi. Wurin yana da rata sosai da cikin garin. Ba kowa sai kukan tsuntsaye da natsuwar ruwa.
Zama tayi tana shan iskar wurin domin wurin ba ƙaramin burgeta yayi ba. Har yanzu tana sanye da shigar mazanta. Ta zauna a bakin kogin, ƙafafunta cikin ruwa mai sanyi.
Can sai ta ji wani abu ya faɗo ta bayanta!
A zabure ta miƙe cikin tsoro mai tsanani tana ƙara! Cikin muryar mace tamkar ba namiji ba, firgici ya sa ainihin muryarta ta dawo!.
Tana juya bayanta sai kawai ta ga wata farar tsuntsuwa kyakkyawa a kwance a ƙasa, an harbo ta daga sama.
A tsorace ta kama ƙirji tare da jin zafin matsin ƙirji da ƙugun cikin tsoro da tausayi. Ta nufe ta da gudu ta ɗauke ta. Can sai ga wasu matasa ‘yan farauta sun zo ɗaukan tsuntsuwar daman su suka harbe ta da mashi.
Ganin AYAT a shigar tsaro suturar maza ta fadar Alhamra yasa suka tsorata suka ce.
"Wayyo! Ɗaya ne daga cikin Security Fadar Alhamra! Mu gudu!"
Nan suka juya suka gudu cikin gaggawa.
AYAT ta sauƙe idanunta a kan tsuntsun. Ta zauna a bakin ruwa. Ta ciro Allura da Zare a jikin rawanin da ta ɗaura. Ta fara ɗinke wa tsuntsuwar wurin da aka cake ta da mashi cikin salonta. Tayi treatment ɗinsa sannan ta ba shi ruwa.
Tana ajiye tsuntsuwar, sai ta ga ta miƙe, amma bata iya yin sama sosai ba.
Itama ta miƙe tana binta da gudu. Ta ga tsuntsuwar ta sauƙa a saman wani tsararren bishiya yanda ƙoyayenta suke cikin raga-raga irin abin da suke koyaye akai har wasu sun kinkishe.
Ta sha mamaki sosai. Ita kaɗai ta fara murmushi tana jin daɗin ceton da tayi.
Tsuntsuwar tana kwance akan ƙoyayenta a ɗan sama da bishiyar kaɗan.
AYAT tana tsaye tana kallonta tare da shafa mata baya. Ta ce, cikin muryar maza mai tausayi..
"Ashe ke ɗin Uwa ce. Nagode Allah da yasa nake nan a wannan lokacin... Shin anan kike rayuwa? Kusa da kogin nan mai kyau? To kar ki damu, zan riƙa zuwa miki ziyara... kuma zan cigaba da kare rayuwarki...
Sunana AYAT, amma a shigar mazan nan sunana 'INUWA'. Wato Inuwarki, mai tare miki rana. Idan na ƙara dawowa zan ba ki takaitaccen tarihina mai cike da kaddara... Ki kula da kanki da yaran ki."
Daga nan ta rufe ta da wasu ganyaye yanda duk wanda yazo bazai san akwai halitta a wurin ba. Nan ta juya zata tafi.
Ganin yamma tayi, nan ta zaro ido a tsorace ta furta.
"Na shiga uku! Daidai wannan lokacin ake rufe Masarauta... kuma nasan ma'aikatana zasu nemeni daidai cin abincina. Wayyo banaso a samu matsala a rana ta Farko!"
Daga nan ta hau saman dokin ta fara gudu dashi, ta ratsa cikin city ta nufi Masarautar...
Ana shirin rufe babban gate sai ga ta, ta nufo da gudu tana tsayar da su da muryar maza mai ƙarfi.
Ɗaya daga cikin masu tsaron Get ne ya ce, cikin tsawa.
"Kai ɗan ƙwaƙur! Daga ina kake?"
Cikin muryar maza a ɗan tsorace, ta ce
"Man dokin ne ya ƙare..."
Duk suka kalli juna jin rainin hankali irin nasa.
"Wannan fa dokar sarki ka karya, don haka zamu je dakai can sai kayi masa wannan bayani..." a cewarsu.
Zaro ido tayi! Ta ji zuciyarta tayi mugun bugawa. Nan ta sauƙo a kan doki ta fara ba su haƙuri da muryar ta mai sanyi.
Ganin bazasu haƙura ba, yasa ta riƙo hannun wani daga ciki cikin fargaba. Duk ta ruɗe tana ba shi haƙuri.
Wanda ta riƙe wa hannu ne ya ji wani irin sanyi ya ratsa shi da ta taɓa hannunsa. Ya ji hannun laushi ya kuma ratsa jikinsa. Ya ɗan ruɗe jin hannun namiji mai sa shauƙi.
Security ya tambaye shi cewa, "Meye sunanka domin ban taɓa ganinka a cikin wannan masarautar ba."
A ruɗe ta ce.
"Musa... Kabiru... Iliyasu... Shafi'u..."
Security ya ce "Kai bana son hauka fa! Anya kai ba ɗan Daudu bane?"
Ta daidaita muryar ta, ta furta sunan da ta sanar wa tsuntsuwa....
"Inuwa.... Inuwa sunana..."
Ɗaya daga ciki ya ce.
"Wannan daga gani ba abinda ya iya domin ɗan daudun cikin mu ne, ga murya a ranrangwaɗe..."
Ɗaya daga ciki ya ɗaga ƙafa ya canƙe ta a wurin mazauninta yana faɗin
"Wuce ka bamu wuri dallah!"
Nan ta fara Tangal-Tangal zata faɗi. Da ƙyar ta daure ta wuce da ɗan gudu–gudu...
Su na masa dariya, har sun sa masa suna 'Ɗan Ƙwaƙur'.
AYAT wato Inuwa kai tsaye ta nufi part ɗinta a babban yankin masarautar. Hanya ɗaya kawai take so ta sulale ta koma part ɗinta tun kafin a ankara da bata nan. Tasan akwai matsala domin dole yanzu za'a buƙaci ta fito akan ta ci abinci.
A hanyarta, wani babba daga cikin Security ya dakatar da ita da cewa.
"Kai! Sauƙo nan..."
Ayat ta sauƙa cikin rikicin zuciya da gajiya. Security cikin nuna isa irin na Shugaba mai role, ya ce
"Uhmm! Wannan Littafin za ka kai wa Gimbiya MAAYAH! Ta buƙaci a kai mata ne."
Cikin ajiyar zuciya na tsoron an tsallake wani haɗarin da kuma sabon tsoro lokaci guda, Inuwa ya karɓa. Ya hau dokin, yana nazarin ina ne part ɗin MAAYAH? Domin tun da take bata taɓa zuwa ba. Sai dai idan lokacin haɗuwa yayi a haɗu a babban fadar sarki.
Haɗiyar yawu tayi domin iya part ɗin ƙanwarta Firdos ta sani kawai.
Tana cikin tafiya, ta tarar da wata mata baiwa ita ma Ma'aikaciya ce. Ta tambaye ta da muryar maza mai sanyi
"Amm, shin ko kin san ina ne part ɗin Maayah?"
Matar ta zabura tana zaro ido ta ce, "Maaaa me?"
A ɗan ruɗe yace "Ohh Gimbiya Maayah..."
Matar ta ce "Ohh yanzu naji batu, amma kai baƙo ne ko? To haramun ne ka ƙira sunan Gimbiyar Sarki kai tsaye ba tare da girmamawa ba." Daga nan ta kwatanta masa..
Inuwa ya ƙara gaba ya sha mamaki ganin tsaruwar part ɗin Maayah. Tsaruwar da ya nuna tsananin alatu da kuma tasirin mahaifiyarta 'Yar Hindu. Da farko masu tsaron part ɗin ne suka tare shi. Ya musu bayanin saƙo ya kawo mata.
Ɗaya ne ya miƙo hannu akan zai kai mata..
Inuwa ya ce "No! Sirri ne! Ni aka buƙaci na kai mata da hannuna."
Jin ya ambaci sirri da umarnin sarki yasa suka barshi ya shiga. Har sai da ya tsallake gate biyar kafin ya isa Center na part ɗin. Nan ya fara ganin mata masu dawainiya da ita sunata zirga-zirga.
Ya shiga babban falon. Wani irin sanyi ne ya ratsa shi. Ga ƙamshi kala-kala na turaren hindu ko wanne fita yake.
Ganin ba kowa a falon, kowa yana ta zirga-zirgan aiki, hakan ya ba shi daman haurawa can saman ɗakin yanda yake da tabbacin anan take. Sai da ya