Showing 81001 words to 84000 words out of 154131 words

Chapter 28 - Masarautar Alhamra Complete Hausa Novels By Asmeetah Writer.txt

ba tare da shautin da yake fita ba kamar na marasa aji, sai dai murmushin nishaɗi..

​“Basir kuma? Subhanallah! Hahahaha!” Ta riƙe fuskarta, tana murmushi da nishaɗi!

“Tamowa! Hahaha!”

​Mutumin ya yi mamaki, shi ma bai san cewa wannan roƙo na tausayi zai zama barkwanci ba...

​Maayah ta tsaya, tana dariya cikin class. Ta nuna shi da yatsa...

“Kai ne! Mama Liyatu, wannan mutumin ya yi nasara! An sanya ni farin ciki da tamowa da Basir! Wannan shine nishaɗi na gaskiya!”

​Ta umarta cikin nishaɗi..
“A ba shi kyauta mai tsoka! Motar alfarma, gida mai kyau, da kuma Kuɗi masu yawa! Sannan a ba shi likitan basir da ya dace! Amma sauran, duk su sha bulala 50 kowa!”

​Gimbiya Maayah ta samu dariyarta a kan mugunta da kuma tausayi..

Mama Liyatu ta matso kusa da ita ta furta..

"Gimbiyata, sauran a musu sassauci mana, bulala hamsin yayi yawa kuma basu san da wannan hukuncin ba..na san ki da tausayi, a musu adalci..."

Gimbiya Maayah ta sassauta murya ta ce,

"Sauran ma, a basu dubu ɗari-ɗari saboda son taimaka mun nayi dariya..."

Mama Liyatu tayi murmushi domin wani sa'in gimbiya Maayah nada sauƙin kai...

Hakan kuwa akayi..

Bayan nan
Gimbiya Maayah ta zauna, amma nishaɗin ya mutu kamar wutar da iska ta hura.... Ba ta wuce minti biyu ba, sai ta miƙe, fuskarta ta koma taurinta na dā...

“Mama Liyatu, na gaji! Wannan Party ya ishe ni. Ina buƙatar hutawa!”

Mama Liyatu ta durƙusa da sauri. “An gama, Gimbiya. Za a yi yadda kika ce.”

Maayah ta kalli falon taron, wanda har yanzu akwai baƙi masu gata da kayan ciye-ciye masu tsada...

“Mama Liyatu! Ina nufin kowa ya watse yanzu! Ba na buƙatar ganin kowa a cikin Fada na! Wannan taro ya ƙare! Ku watsar da komai, ko da kuwa nawa ne kuɗin da aka kashe a kan wannan abincin marasa amfani!”

Mama Liyatu ta yi sauri ta tura Bodyguards da masu aiki don su fitar da kowa...

Cikin lokaci ƙanƙani, an watse taron! An kashe fitilu, an rufe ƙofa, kuma duk abincin Ƙasaita da aka kawo ya zama datti!..

Gimbiya Maayah ta shiga ɗakinta, baƙin ciki da gajiya sun koma mata.....


✨✨✨

Ayat ta shigo ɗakin baccinta cike da fara'a, ɗauke da manyan kulolin abinci na alfarma waɗanda aka girka na musamman..

"Lokacin cin abinci!"
ta faɗa cikin sanyin murya tana kallon Reems...

Yau ta ƙuduri aniyar cin abincin dare tare da abokinta kuliya. Ta ajiye tiren abincin, sannan ta juya zuwa sashen sutura don ta cire manyan kayan gimbiyancinta ta sanya lallausan kayan bacci domin ta saki jikinta...

Yayin da Ayat ta ba da baya, King Diamond a siffar kuliya ya daki hancinsa da wani irin kamshin kifi mai daɗi... Tun da yake a duniyar mutane, bai taba jin yunwa irin ta yau ba. Cikin hanzari, ya yi amfani da kafafunsa ya dinga bubbuɗe kulolin abincin. Ganin irin daɗin kifin da aka sarrafa, ya kasa jurewa...

Ya fara ci, sai da ya cinye kula na ɗaya tass.... Ya koma kan kula ta biyu, nan ma ya cinye tass, bai rage ko loma daya ba!..

Ayat ta nufo wurin abincin tana gyara gashinta, amma tana isa, ta tarar da kulolin wayam! Ta zaro ido, numfashinta ya kusa tsayawa...

"Wayyo! Duk ka cinye abincin? So kake na kwana da yunwa?"

Ta faɗa cikin murya mai cike da shagwaɓa...

"To ni yanzu me zan ci? Idan na sake komawa neman wani abincin, za su fara zargin me nake yi da abinci mai yawa haka, ni da ko rabi kula bana iya cinyewa!"...

Ganin Reems yana kokarin nufar wata karamar kula dake dauke da ferfesun kifi mai yaji, Ayat ta yi sauri ta janye kular...

"Wannan ma ba za a bar min ba?" ta faɗa tana turo baki...

Reems ya lallaɓa ya koma gefe ya kwanta kamar wanda aka zalunta...

Ganin haka, zuciyar Ayat ta karaya...

"Laaa... kar ka yi fushi My Reems... ga madara bari na baka."

Ta zuba masa madara mai ɗumi a kwanon azurfa, nan ma tass ya shanye gaba daya...

"Allah, ka cika ci da yawa! Zamanka sai a lambu!"

ta furta tana dariya da kuma mita...

Ta ɗauki ferfesun kifin ta kai loma ɗaya a baki, amma sai ta ga Reems ya zuba mata idanunsa na zinare, yana kallon lomar da take kaiwa...

"Na shiga uku! Wannan ma ba za ka bar min ba?"

Ta numfasa, sannan ta ce,
"To shikenan, bari na gani ko kana sona, za ka bar min wannan?" Ta ajiye masa kular...

Ai kuwa, King Diamond bai ko yi wata-wata ba, ya lankwame ragowar kifin nan tass!...
Ayat ta saki baki tana kallonsa, sannan ta fara kukan shagwaɓa tana shure-shure...

"Mugun kuliya!"

Ta miƙe ta nufi firij ɗinta, ta ɗauko fruits ta zauna can nesa da shi, ta fara cin apple ɗinta cikin ɓacin rai, tana kau da kai don kada ta kalle shi ta ji tausayinsa har ta ba shi ragowar...

King Diamond ya zauna yana lashe bakinsa, yana kallon yadda take cin apple ɗinta cikin fushi... A ransa ya ce,

"Ayat, da kinsan irin daɗi da nake ji na cewa yau kin zama uwar gida dake ciyar da ni, da tabbas ba zaki yi fushi ba."...


Ayat tana zaune a kan kujera can nesa da gadon, tana cin apple ɗinta cikin fushi, tana tauna shi da ƙarfi kamar tana tauna Reems ne....

Tana jujjuya ƙwayar idanunta, tana kau da kai duk sanda ta ji motsin kuliyar. Ta ƙuduri aniyar ba za ta kula shi ba har sai gari ya waye, domin kuwa ya kwashe mata duk abincin da take takama da shi...

King Diamond, dake cikin siffar kuliya, ya lura cewa wannan karon fushin na gaske ne. Ya san cewa idan bai yi dabara ba, Ayat ba za ta ba shi damar kwanciya kusa da ita ba yau....Ya miƙe a hankali, yana takunsa na kuliya mai sanyi, ya fara lallabawa har zuwa ƙafafunta...

Ya fara goga kansa a jikin lallausar fatar ƙafarta, yana fito da wani siririn sauti na kuliya mai ban tausayi...


Ayat ta ji sanyin gashin Reems a fatarta, ta yi ƙoƙarin janye ƙafarta tana mita...

"Ka tafi can! Mugun mai ci da yawa kawai. Ka cinye min shinkafa, ka cinye min tuwon shinkafa, ka cinye min kifi, ka cinye min ferfesun kifi, sannan ka shanye.. madara, yanzu kuma me kake nema? Apple ɗin ma so kake ka cinye?"

Duk da maganganun da take yi, ta kasa jure yadda Reems ya ɗaga kansa yana kallonta da idanunsa masu sheƙi, kamar yana roƙon gafara. Ya yi tsalle ya dawo kan cinyarta, ya fara goga hancinsa a hannunta dake riƙe da apple.

Ganin yadda ya dage wajen ba ta haƙuri, sai Ayat ta fara murmushi, har dariya ta fara subuce mata....

"Allah ya shirye ka Reems, ba ka da dama! To shi ke nan, tunda ka zama mai neman afuwa, bari na raba maka wannan."

Ta gutsuri ɗan ƙaramin guntun apple ta sanya masa a baki...

King Diamond ya karɓa ya fara taunawa, duk da cewa ba shi ne abin da yake so ba, amma taɓa shi da take yi da kuma murmushinta ya fi masa kowane irin abinci daɗi. Ayat ta rungume shi, tana shafa bayansa..

"Ka ga yadda kake da kyan gani? Idan ka daina wannan kwaɗayin, zan fi kowa daɗin zama da kai."

Ta koma kan gado tare da shi, tana jin wani irin natsuwa. Ta manta da duk wani damuwa. A wannan daren, ita da Reems ne kawai a duniyarsu ta daban. Ta kwanta tare da shi, tana raɗa masa a kunne..

"Wani lokacin ina jin kamar kana fahimtar kowace magana da nake yi, Reems.... Shin kai wanene ne a asali?"

King Diamond ya lumshe ido, yana jin ɗumin jikinta. A ransa ya ce,

"Ina fatan ranar da zan amsa miki wannan tambayar, Ayat, ba za ta zama ranar da za ki guje ni ba."....

*Likes ɗinku shine albashin marubuci*

👍 Like
🔁 Share
💬 Comment


*👑 MASARAUTAR ALHAMRA 👑*

_🪄 Gidan Mulki, Iko da Sirrin Zuciya 🪄_

✍🏽 By ASMEETAH WRITER
~Hasken Jajirtattu~


💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️

```JARUMAI WRITERS TEAM```

▶️ DON BIYO DAGA FARKO 👇
🔗 WhatsApp Channel:
https://whatsapp.com/channel/0029VbBCNlqJUM2RQwWncg43

📚 ArewaPen:
https://arewapen.com/u/asmeetahwriter

📖 Wattpad:
https://www.wattpad.com/user/asmeetahwriter

📲 Contact:
09065443871

📅 FARA TURA BOOK:
🔥 01 — 01 — 2026 🔥

📘 BOOK ONE
```MATAKIN FARKO```

CHAPTER 2️⃣4️⃣

*بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ*



Yayin da Ayat ta lula duniyar bacci, King Diamond ya fito daga siffar kuliya ya koma asalin sa. Ya zauna kusa da ita, yana shafa lallausan gashinta cikin wata irin kulawa mai ratsa jiki. Wani irin ƙauna yake ji yana ratsa kowace jijiyar jikinsa, ƙaunar da ba shi da mizanin aunata. Ya kalli kyakkyawar fuskarta, ya kasa jurewa, ya kwanta a gefenta a matsayinsa na mutum, baccin natsuwa ya kwashe shi shima...

Ayat mace ce mai yawan juyi a bacci. Cikin daren, ta fara neman inda take jin ɗumi. Ba tare da ta sani ba, ta haye saman King Diamond...
Can ta ɗora ƙafafunta a kan ƙirjinsa, bayan awanni ta yi pillow da cikin sa.... In the last night ta hau kansa gaba ɗaya ta ƙanƙame shi sosai kamar tana tsoron kar ya gudu, tana jin wani irin ɗumi dake sanya mata natsuwa. Shi ma Diamond, saboda gajiyar kwanakin nan, bai ji daddaɗan nauyin da ta ɗora masa ba, suka ci gaba da sharar baccinsu...

Yau ƙaddara ta so hakan, domin dukkaninsu sun makara har aka idar da sallar asuba a masarautar. Hasken gari ya fara ratsa ɗakin... King Diamond ya fara buɗe idanunsa, ya ji jikinsa ya yi nauyi. Yana kallon ƙasansa, sai ya tarar da Ayat ta mayar shi dokinta, ta rungume shi sosai....

Wani murmushin gefen baki ya yi, yana magana a ransa..

"Ta riƙe ni sosai, ta yaya zan janye ta ba tare da ta farka ba?" Ya san muddin ta buɗe ido ta ganshi a haka, babu abin da zai cece shi daga takobinta...

Cikin dabara da takatsantsan, King Diamond ya sa hannayensa ya ɗaga hannunta da ƙafafunta a hankali, ya juyar da ita zuwa gefe...
Sai Yaraffff! ta faɗa a kan gadon. Sakamakon hakan, Ayat ta fara motsawa, tana shirin buɗe idanunta domin ta tsinci kanta a wani sabon yanayi...

Cikin kifawar ido, ya yi amfani da ikonsa, ya ɓace a matsayin mutum ya koma siffar kuliya a gefenta, daidai lokacin da ta buɗe idanunta tana miƙa...

Ayat ta buɗe idanunta, ta ga gari ya waye sosai. Ta ji jikinta yana mata wani irin ɗumi daban, kuma tana jin tamkar ta yi matashi da wani abu faffaɗa.. Ta kalli Reems dake kwance a gefenta yana kallonta kamar yanzu ya tashi...

"Ya salam! Reems, mun makara!" ta furta tare da miƙe wa. Ta fara tunanin juyin da ta yi a daren, tana mamakin me ya sa take jin tamkar akwai mutum a kusa da ita...

"Wannan juyin nawa kam, ko gado ne ya ruguje ba zan sani ba," ta faɗa tana dariyar ciki..


Ta miƙe tsaye tana murza idanunta, tana jin wani irin ɗumi na musamman dake yawo a jikinta. Ta kalli gadon ta ga yadda ya hargitse, alamar ta yi juyi sosai....
Lokacin da ta kalli madubi tana shirin gyara gashinta, sai idonta ya sarƙe da wani abu dake kwance a kan kafaɗar rigarta ta bacci..

Ta sa hannu ta ɗauko shi. Dogon gashi ne guda ɗaya, fari sol kamar hasken wata, kuma yana sheƙi mai ban mamaki...

Ta zaro ido, ta matso da gashin kusa da idonta..

"Wannan kuma daga ina yake?" ta tambayi kanta..

Ta kalli kanta a madubi, gashin kanta baƙi ne wulk, ba shi da ko saƙar fari. Ta juyo ta kalli kuliyar...

"Reems, wannan gashin naka ne?" Ta matsa kusa da kuliyar ta duba gashin jikinsa. Duk da cewa kuliyar fara ce, amma gashin jikinta ɗan gajere ne kuma mai laushi, ba shi da tsayin da zai kai wannan gashin da take riƙe da shi a hannu..

"Wannan gashin na mutum ne, kuma mutum mai farin gashi!.."

Nan take zuciyarta ta harba. Hoton mutumin nan da ta gani a bakin kogi ya dawo mata...

"Mai Farin Gashi!" ta furta a hankali. Wani irin fargaba da tsoro suka baibaye ta...

"Shin ina nufin mutumin nan yana shigo min ɗaki ne yayin da nake bacci? Amma ta yaya? Masarautar nan fa tana da kariya!"

Ta fara duba ko'ina a ɗakin, tana bincike ƙarƙashin gado da bayan labule, tana jin kamar ana kallonta...

King Diamond, wanda ke cikin siffar kuliya, ya daskare a wurin da yake kwance. Zuciyarsa ta buga ganin ta tsinci wannan gashin nasa. Ya san cewa yau ya tafka babban kuskure. Yana kallon yadda Ayat take bincike cikin fargaba, yana jin tausayinta kuma yana jin tsoron abin da zai faru idan ta gano gaskiyar...

Ta sake dawowa kan gadon, ta zauna kusa da Reems...

"Reems, akwai abin da ka sani wanda ni ban sani ba? Me ya sa nake jin tamkar ba ni kaɗai nake a ɗakin nan ba?"..

Ta matse gashin a hannunta, sannan ta miƙe ta nufi wurin tufafinta...

"Yau dole na je na ga babban malamin tsafi na masarauta... Dole na san ko akwai wata inuwa dake biye da ni, domin wannan gashin ba na duniyar nan ba ne."..

Ta shige banɗaki da gaggawa, yayin da King Diamond ya sauƙe wani nannauyan numfashi. Ya san muddin ta kai wannan gashin wurin malamin tsafi, asirinsa na matsayin kuliya zai iya bayyana..

Ayat ta kammala shiryawa cikin kayan gimbiyanci, jikinta na fitar da daddaɗan ƙamshin mayukan alfarma. Ta nufo gadon da niyyar ɗaukar Reems, amma sai ta tarar da gurbinsa wayam. Ta ɗaga blanket, ta duba ƙarƙashin gado, ta bincika kowane lungu amma kuliya ba ta nan...

Cikin matsananciyar fargaba, ta juya kan madubin don ɗaukar gashin nan dake hannunta, nan ma ta iske ba komai!
Hankalinta ya tashi fiye da kowane lokaci...

"Reems! Reems ina ka shiga ne? Don Allah ka fito!"

Ta fara hawaye lokaci guda, zuciyarta na gaya mata cewa ɓacewar Reems babban rashi ne da ba za ta iya jurewa ba.

Tsabar ruɗani ya sa Ayat ta manta da sanya mayafin da take rufe fuskarta da shi. Ta buɗe ƙofa ta fito, gashinta baƙi wul ya bazu a bayanta, fuskarta tana sheƙi tamkar hasken farin wata...
Tana sauƙa falon ƙasa, ma'aikata da bayin da suka saba ganinta a rufe suka daskare...

Saratu da take ganinta kullum ma ta kasa motsi. Kyawun Ayat ya wuce misali, fara ce sol, idanunta masu kalar zinare suna fitar da hawaye... Kyawunta ya zama tamkar nurul-ayn, wani kwarjini ne dake sanya kowa sunkuyar da kai da daskarewa tsabar kallo. Ba su ma iya tambayarta ina za ta ba, sai kawai suka ba ta hanya tana gudu tana ƙiran sunan kuliyarta...

Tana fita harabar sashenta, jami'an dake tsaron wurin duka sumar tsaye suka yi. Ba su taɓa sanin cewa Gimbiya Ayat tana da wannan irin siffar ba. Suka bi ta da kallo, wasu ma har makaman hannunsu ya faɗi ƙasa ba tare da sun sani ba. Sun ɗauka wata halitta ce daga aljanna ta sauƙo cikin masarautar Alhamra...

Cikin kuka da ƙiran sunan Reems, Ayat ta nufi babban lambun dake cikin sashenta. Wuri ne mai cike da furanni jajaye da farare, masu ƙanshi da kyan gaske... Ta shiga duba bayan kowane fure da ƙarƙashin bishiyoyi, amma babu Reems babu alamunsa...

Wannan lambun dake sashenta ya kasance mafaka a gare ta, domin babu wanda yake da ikon shigowa ya takura mata a ciki. Ta duba ko'ina amma shiru, kukan da take yi ya ƙara tsananta...

Ganin ba ta ga Reems ba, ta durƙusa a tsakiyar lambun, ta haɗa kanta da gwiwa ta fashe da kuka mai ban tausayi...

"In har baka nan, to na sani na rasa ka kenan...me ya sa ka tafi a wannan lokacin?" ta furta cikin murya dake rawa...

Ta jima a haka, tana kuka na tsawon kusan minti talatin, tana jin tamkar rayuwarta ta rage amfani tunda ta rasa abokin hirarta kuma garkuwar zuciyarta...

Can sai ga kuliya ya bayyana a gabanta..

Muryar kuliyar dake fitar da wani siririn sauti ya sa Ayat ɗago kanta da sauri. Tana ganin Reems a gabanta, zuciyarta ta cika da farin ciki...

"Reems!" ta faɗa tare da miƙewa da sauri don ta rungume shi. Amma kafin hannunta ya kai gare shi, sai wani zazzafan haske ya bayyana, tare da wata guguwa mai ƙarfi da ta tada furannin lambun sama. Ayat ta sa hannu ta rufe fuskarta saboda ƙura da ƙarfin hasken da ya kusan makantar da ita.

Bayan hasken ya lufa, ta sauƙe hannunta a hankali, tana addu'ar kada abin da take zargi ya zama gaskiya... Idonta ne ya sauƙa akan abin da ya fi kowane tsoro.. Mutumin nan mai farin gashi!..

King Diamond ne tsaye a gabanta, yana mata wani kallo mai cike da mallaka da isa. Ayat ta zazzaro manyan idanunta, kyakkyawar fuskarta ta bayyana tsantsar firgici....Sai da ta ƙare shi da kallon sama da ƙasa, sannan ba tare da ta tsaya wata-wata ba, ta buɗe ƙaramin bakinta ta saki wani uban ihu ta juya da gudu, tana son barin lambun kafin zuciyarta ta buga...

Gudun Ayat bai kai ko ina ba, domin kafin ta ankara, King Diamond ya ɓace ya sake bayyana a gabanta...

Saboda ƙarfin gudun da take yi, ta kasa tsayawa, sai kawai ta faɗa kan faffaɗan ƙirjinsa dake da ɗumi. Firgicin taɓa shi ya sa ta yi baya da sauri tana shirin faɗuwa ƙasa, amma ya miƙa hannunsa mai ƙarfi ya cafko hannunta, ya tsayar da ita kyam a gabansa...

A wannan lokacin, King Diamond ya sauya siffarsa zuwa asalin siffar Sarkin Power Pool. Yana sanye da fararen kaya na alfarma masu ratsin zinare da gwal. Sumar kansa fara sol an tuƙe ta a tsakiyar kansa da wani ƙarfen gwal, fuskarsa tana fitar da wani haske mai ban mamaki sakamakon tsantsar farin jikinsa..

Duk yadda Ayat take da kyau, a wannan lokacin ta ji kwarjininsa ya kusan danne nata. Ya kura mata ido, yana kallon yadda fuskarta take sheƙi ba tare da mayafi ba, yayin da ita kuma take tsaye jiki na ɓari.

Duk da bugun zuciyarta da ya kusan kayar da ita, Ayat ta dake. Ta tsaya kyam tana kallon cikin idanunsa, hannunta dake cikin nasa yana rawa. Ta kasa magana, amma idanunta suna tambayarsa..

"Shin duk wannan lokacin, kai ne kuliya ta? Kuma kai ne ka ga duk abin da na ɓoye?" King Diamond ya matsa kusa da ita, numfashinsa yana dukan fuskarta, ya raɗa mata cikin muryar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login