Showing 60001 words to 63000 words out of 133773 words

Chapter 21 - HASKE BIYU ( YAR JARIDA ) BY MEERAH.txt

Meerah   

28 Nov 2024

9705

da lokacin ka da ka ba mu "
Murmushi kadan doctor ya yi ya na fadin " no ni ne da Godiya "
" To doctor sai ayiwa ma su kallon mu sallama "
Juya wa doctor ya yi ya kali camera ya na yin sallama
Amsa mishi sallamar shi Safa ta yi kafin ta daura da cewa " Duka duka a nan mu ka kawo karshen shirin na mu na Abokiyar hirar ku , Tare da ni Doctor Sadeeq mu ke cewa mu hadu da ku a sati na gaba na barku lafya "
Ta na gama fadar haka mai kula da camera ya daga murya ya na fadin " Cut ! "
Da ga haka kuma duk mutanan wajen su ka shiga yin tapi , murmushi Safa dai ta yi kafin ta sauko da ga saman plateau din ba ta bi ta kan su ta bar wajen da sauri ko Doctor Sadeeq ba ta tsaya yi ma sai an jima ba
Kai tsaye waiting room ta nufa , bakin ta dauke da sallama ta shigo wajen
Nan ta ga Amar da Nabil su na zaune su na kallon Tv da ke gaban su , ashe duk abun da su ka tatauna su na kallon su directly
Kallon Safa Amar ya yi kafin ya ce " Har kun gama ? "
Murmushi kawai ta yi mishi ta na gyada mishi kai
Mikewa tsaye ya yi ya mika wa Nabil hannu ya na fadin " My friend , see you next time "
Riko hannun shi Nabil ya yi su ka yi musbaha ya ce mishi sai ya dawo , da ga nan Safa ta yi mishi sallama ita ma sannan su ka bar wajen ita da Amar
[10/09 Γ  20:04] MEERAH πŸͺ·πŸ©·:






πŸ’«πŸ₯€ HASKE BIYU πŸ₯€πŸ’«
( YAR JARIDA )







( A heart touching love story & destiny )


















STORY & WRITTEN BY : MEERAH πŸ•Š










Marubuciyar littafin


TAURIN ZUCIYA πŸ’–πŸ’πŸŒΊ: FREE BOOK

❀⚘ EXILED PRINCE ⚘❀ : PAID BOOK







DOMIN SAMUN WANNAN LITTAFIN DA GA FARKO , ZA KU IYA JOING MY WHATSAPP CHANEL


πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡


https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i



TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMENTS SECTION


πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡


https://chat.whatsapp.com/IrsjzfoHUHBJzdgRtskPcY




ZA KU IY SAMUN WANNAN PAGE A WATTPAD TA HANYAR WANNAN LINK


πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡


https://www.wattpad.com/1475830151?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=bennybite












BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM


















PAGE 19 πŸ₯€ ❀




















Ba su tsaya neman kowa ba su ka bar building din a tare dama Daukar ce kawai ke kawo Safa wajen duk wani abu da ya dace Mutalab ya ce ya dauki nauyin shi ita daukar da kuma guest din ta kawai su ke bukata in wata ya yi kuma su biya ta duk da ita Safa ba dan kudin ba ta ke yi musu aikin su ne dai ba su sani ba


Bayan sun shiga motar su su ka bar wajen su ka hau titi
Safa ta kali Amar ta tambaye shi ina za su je ne yanzu
Ba tare da ya kale ta ba ya ce " Gidan wani uncle di na , tun jiya ya kamata na je amma na bari mu taho tare zan so ya gan ki " ya kai karshen ya na juyawa ya kale ta


Dan karamin murmushi ta yi ta na kauda kan ta gefe
" ka san inda gidan ya ke ne ? " Safa ta tambaye shi ba tare da ta juyo da kallon ta ba


" eh na sani " ya ba ta amsa a takaice
Slowly ta juyo ta kaleshi ta ce " Why ba ku taho tare da Assad ba "


Dan karamin murmushin geffen fuska ya yi kafin ya ce " bai san da zaman Assad ba , Asali ma a tunanin su ni kadai ne ba Twins ba "


" how? Ban gane ba ka na nufin a tunanin su Assad ya mutu ko ya " Safa ta fada ta na dan lekon face din shi


Shiru ya yi bai ce mata komai ba
Sai da ya dan dauki lokaci kafin ya ce " zan ba ki labarin idan mun koma gida saboda ya na da tsayi "


Jinjina kan ta kawai Safa ta yi kafin ta juya ta sunkuyar da kan ta ta shiga latsa wayar ta


Sun dauki wajen five minutes a haka kafin ta ji ya danna horn
Ba ta dago kan ta ba har sai da gateman ya bude musu gate , Amar ya danna hancin motar cikin gidan ya nufi parking space ya yi parking ya kashe motar sannan ya sauko ya zagayo geffen Safa ya bude mata kofar ya na fadin " To madam sai a sauko "


Sai a lokacin ta kashe wayar ta , ta meda ta cikin bag din ta , sannan ta sa kafa ta sauko , Amar ya meda kofar ya rufe ya na ce mata su tafi


Dum Safa ta ji gaban ta ya fadi ganin gidan da su ke ciki har sai da ta yi sumar tsaye


Ganin yadda ta yi tsaye waje guda ya sa Amar kamo hannun ta ya ja ta su ka nufi kofar shigowa parlourn
Sai da su ka iso bakin kofar sannan ya saki hannun ta ya yi knocking
Bai kai ga yin na biyu ba a ka bude mishi door din


Ya na shirin shiga wayar shi ta fara ringing
Komawa gefe ya yi ya ce ma Safa ta shiga ya na zuwa


Jinjina mishi kai ta yi ta na hadiye wasu yawu sannan ta daga kafa kamar wadda a ka zarewa lakar jiki ta shiga parlourn ta na sallama , ta yi sa'a ko Daddy ba ya nan shi da Sami da khalifa , amma duk matan gidan su na nan Twinkle kuma ta na bedroom din ta , yan matan ne kawai a parlourn kowa ce na kallon Tv allamun shirin ya yi musu duka


Noor na ganin ta ta tashi da gudu ta rungume ta ta na fadin " oyoyo Safa na "


Dan tsaki RaΓ―ssa ta ja ta na kauda kan ta gefe
" zauna bari na je na kira momy " Noor ta fada ta na sakin Safa ta Haye stair da gudu
Ita dai Safa shiru ta yi ta na tsaye waje guda kamar bakuwar gidan


Noor na barin wajen Fadila ta wurga ma Safa wani mugun kallo ta na fadin " ke me ya kawo ki gidan nan ? "


Ba ta gama rufe bakin ta ba RaΓ―ssa ta daura da cewa " Ta zo abun da ta saba yi mana , nan fa ba gidan talafin marayu ba ne , kin yi batan hanya "


A tare duk su ka bushe da dariya dai'dai lokacin da Amar ya turo kofar parlourn ya shigo ya na sallama kai a sunkuye ya na duba wayar shi


RaΓ―ssa na ganin shi ta mike tsaye slowly , dama jiya Daddy ya fada mata yau doctor Amar zai zo gidan har pic din shi sai da ya turo mata , shi ya sa ta na ganin shi ta saki baki dan fa ya tafi da duk imanin ta


Shi kuma sai da ya karaso geffen Safa ya tsaya sannan ya dago kai ya na meda wayar shi cikin aljihu


Kallon mutanan parlourn ya yi ya saki wani cool murmushi ya ce " Hi guys How are you ? "


Cike da zumudi Fadila ce mishi " Lafya lau ya ka ke ? An zo lafya ? "


" oh Sorry ba na jin haoussa " ya fada da turanci


Dan zaro idanu Fadila ta yi ta na juyawa ta kali RaΓ―ssa ta juya ta kali Amar


Ta na shirin magana ta ga RaΓ―ssa ta karaso gaban Amar ta na fadin " Sannu ka da zuwa bismillah zauna mana "


Daga mata hannu ya yi sannan ya juya ya kali Safa ya ce " I'm sorry baby ina ga komawa za mu yi , uncle ne ya kire ni , ya ce ba ya gida sai dai gobe mu dawo "


A tare Farida da Fadila su ka kali juna su na zaro idanu su ka ce " baby ? " a tare


Ba su gama rufe bakin su ba , Safa ta juya da sauri za ta bar wajen
Ta yi taku biyu ta jiyo Muryar TWINKLE ta na fadin " Safa ? "


Cak ta tsaya ba tare da ta juyo ba ta na jin zuciyar ta na duka uku uku


Shi dai Amar tsaye ya yi ya na kallon matar nan , sai ya ga kamar Safa ce ya ke kallo kawai sai ya rasa yin wani kwakwaran motsi kawai ya tsaya ya na kallon su


Sai da TWINKLE ta karaso wajen su , sannan Safa ta juyo slowly
Da sauri TWINKLE ta rungume Safa ta na fadin " My Safa , na ji dadin ganin , i have really missed you "


Rungume ta ita ma Safa ta yi cikin sanyin murya ta ce " Good morning Mom ! "


Dan zaro idanu Amar ya yi ya na maimaita kalmar cikin zuciyar shi


Raba jikin su Safa da twinkle su ka yi , da sauri Safa ta juya ta na fadin " Good bye Mom "
Cak ta ji an riko hannun ta , da sauri Safa ta juyo ta ga Amar ne
Cikin raunin murya ta ce " Doctor please let's go "
Kallon Doctor Twinkle ta yi ta na shirin magana Noor ta riga ta cewa " My Safa tafiya za ki yi " ta kai karshen kamar za ta yi kuka


Slowly Safa ta juyo ta kali Noor ta yi mata murmushin karfin hali ta ce " i'm sorry My Noor ina dawowa ran Monday yanzu akwai inda zan je " ta kai karshen ta na kwace hannun ta da karfi da ga na Amar ta fice Parlourn da sauri


Da sauri Amar ya ce " Baby where are you going ? " ina har ta ficewar ta ta janyo door din da karfi


Dawo da kallon shi ya yi kan twinkle ya yi sannan ya ce " I'm sorry Mom....... "
Cikin nitsuwa TWINKLE ta katse shi da cewa " don't worry my son let's go home now " ta kai karshen ta na juyawa ta Haye stair


Ta na barin wajen Noor ta karaso gaban Amar ta na washe baki ta ce " hi , my name is Noor , ba zan tseda ku ba , kawai dan in ce maka ina matukar son aikin da ka ke yi , ni ma in na girma karatun doctor zan yi "


Maganar ba karamar dariya ta ba shi ba , amma sai ya danne ya saki wani cool murmushi ya mika ma ta hannu ya ce " Nice to meet you Miss Noor , an taba fada miki ki na da kyau kamar hasken wata "


Da sauri Noor ta sa hannu ta rufe fuskar ta ta na murmushi wai ita ta ji kunya


Murmushi mai dan sauti ya yi kafin ya ce " Don't be Shy like me , i'm coming back very soon , yanzu dai bari na je kar Madam ta bace min , bye " ya kai hannu ya na juyawa ya fice parlourn


Ya na fita Noor ta saki wata yar kara har da tsale kafin ta juya da gudu ta Haye stair


Ta na barin wajen Fadila ta ce " Toooo , wata sabua , Fifi kin ji abun da na ji Madam ? "


Yar karamar dariya Farida ta yi ta na kallon RaΓ―ssa ta ce " to je RaΓ―ssa kin ga samu kin ga rashi , dan da ga ganin allamu Safa ta malake zuciyar Doctor Amar , kin ji wai Madam " ta kai karshen ta na sake bushewa da dariya


Dan tsaki RaΓ―ssa ta yi kafin ta harare ta sama da kassa sannan ta nufi stair da gudu ta Haye , da kallo Fadila da Farida su ka raka ta har sai da ta Haye sannan su ka sake bushewa da dariya har da tapi


Bangaran Amar kuma bayan ya fito harabar gidan ya ga babu Safa ya yi tunanin ta na cikin motar amma sai ta ga ba ta nan
Da sauri ya shiga motar ya tada motar ya bar gidan da mugun gudu
Shi ya rasa ta ina ma zai fara duba ta , ya duba duk layin har karshen shi babu ita babu mai kama da ita


Da sauri ya ciro wayar shi ya fara duba localization din ta
Da sauri ya tada motar ya bar wajen
Sai da ya yi tafiya wajen ten minutes kafin ya iso cikin wani tsohon kongo
Da sauri ya yi parking din motar shi , ya sauko ko motar bai kashe ba ya shiga wajen da sauri
Cen ya hango ta zauna saman wasu brick na siminti ta na zaune ita kadai ta na dan rera waka ta na murmushi kamar mahaukaciya


Bai ce mata komai ba kawai ya sa hannayan shi biyu ya dauke ta cak kamar baby ya juya ya bar wajen da ita
Bai sauke ta ko ina ba sai cikin motar shi , sannan ya shiga shi ma ya bar wajen da gudu


Bai ce mata komai ba har sai da su ka karaso cikin garin Kaduna , ya iso bakin kofar gidan su ya yi parking din motar


Ba tare da ya kale ta ba ya ce " Ba zan yi miki dole ki fada min abun da ke damun ki , amma zan so ki san duk ranar da ki ka ji ki na bukatar abokin da zai taya ki kuka ki kira ni kawai "


Bai kai ga karasa maganar shi ba ya ji ta fado jikin shi ta rungume shi ta na sakin kuka mai cin rai
Bai yi kokarin hana ta ba , sai ma rungume ta da ya yi shi ba ya na dan bubuga bayan ta a hankali ya na fadin " ni fa ba irin wannan kukan ba na ke so , amma please ki daina ba na son ganin ki cikin wannan halin wlh ki na karaya min zuciya "


A hankali ta dago da ga jikin shi ta na rage sautin kukan ta , ta ce " me ya sa ka damu da ni haka wai , duk rayuwa ta bayan Family na babu wanda ya taba ce min ina karaya mishi zuciya da kuka na sai kai , asali ma bayan su kai kadai ne ka taba ganin kuka na "


Dan karamin murmushi ya yi ya na kai hannu ya ciro handkerchief ya fara goge mata hawayen ta ya na fadin " to ni ma ai yanzu familyn ki ne , dan haka duk lokacin da ki ka ji wani abu na damun ki , kawai ki kira ni mu tafi shan ice cream "


Yar karamar dariya ta yi ta na shirin magana ta ji saukar lips din shi saman forehead din ta ya yi mata kiss
" shikenan yanzu tashi ki je , ki wanke face din ki , ki yi sallat sai ki tardo ni gida ina jiran ki kin ji ? "


Gyada mishi kai kawai ta yi dan ya kashe mata bakin magana, da ga haka ta sauko da ga cikin motar ta shiga cikin gidan su
Shi ma saukowa ya yi da ga cikin motar ya nufi cikin gidan na su , kafin ya shiga sai da ya bawa daya da ga cikin Sojojin da ke tsaye bakin gate a kan ya sanyo motar cikin gida


Bayan ya shiga gidan kai tsaye part din su ya wuce
Bakin shi dauke da sallama ya shigo parlourn part din su
Nan ya isko Assad zaune saman sofa ya na aiki cikin laptop din shi
Geffen shi Amar ya karaso ya zauna ya na fadin " wai yaushe za ka fita da ga cikin gidan nan , kullum ka na ciki kamar amarya "


Ba tare da ya kale shi ba ya ce " da ga ina ka ke ? "
Dan kauda kan shi gefe Amar ya yi ya na dan karamin tsaki kafin ya ce " wai yaushe za ka daina samin ido ? "


Ajiye laptop din shi Assad ya yi ya juyo ya kali Amar ya ce " fada min gaskia , me ke tsakanin ka da yarinyar nan , na ga ku na yawwan fita kai da ita "


Dan karamin murmushi Amar ya yi kafin ya ce " Love ! " a takaice
Shiru Assad ya yi ya juya ya dauki laptop din shi ya ci gaba da aikin shi


Mike wa tsaye Amar ya yi ya nufi bedroom din su
Har zai shiga ya tsaya ba tare da ya juyo ba ya ce " Sasha ko na fada maka ba za ka iya gane abun da ke cikin zuciya ta ba , saboda ba ka san wannan abun ba "


Cikin nitsuwa Assad ya katse shi da cewa " na sani , kar ka manta zuciyoyin mu a tare su ke bugu , duk wani yanayi da ka ke ciki ina jin shi a jiki na , na san ka na son yarinyar nan , ba kuma zan tseda ka ba wajen ganin ka samu soyayyar ta ba , I just don't want her to end up fucking your heart , ba zan iya jure haka ba "


Slowly Amar ya juyo ya kali Assad , har yanzu dai ya na faman latsa laptop din shi


Dan karamin murmushi Amar ya yi kafin ya juya ya shiga bedroom din su


Ya na shiga Assad ya dago kai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login