Showing 42001 words to 45000 words out of 138779 words
Chapter 15 - El-mustapha Complete Hausa Novels By Fertymerh Xarah.docx
sakamin dan baxan yafe ba.
Nan ma jiddah bata tanka ba, sai Ma qoqarin tashi take ta bar mata falon, uwani Ma ta tashi tana fadin,
Iyayena sun riqi mutum amana amma su anqi a riqa masu amana, iyayena sunyi qoqari su ba mutum tarbiyar dama uwar mutum baxata iya bayarwa b...... bata qarasa ba taji saukar Mari a kuncinta, kafin tayi wani yunquri jiddah ta qara dauke ta da wani Mari, xatayi magana ta qara dauke ta da wani Mari, uwani ta gigice ta fara ihu dafe da kuncinta.
Xan dauki kowane irin iskanci naki amma banda na iyayena, nasan darajar su da qimarsu ke baki isa ki xagi iyayena na barki ba, yanxu Ma darajar cikin nan kika ci da sai kin yabawa aya zaqin ta, daqiqiya kawai, ta fice ranta a matuqar bace.
Wlhy Allah xai sakamin kuma baxan yafe ba sai na dauki mataki, ke ki dake ni mijinki ya dake ni, ai ni ba boya bace, kinci darajar wannan cikin da sai nayi qasa qasa da namanki a gidannan, sai na ji maki ciwo na fasa maki baki, ai ba qarya nayi ba iyaye na ne suka miki tarbiya, idan kin cika ki qara fitowa kice xaki dake ni k...... tayi shiru ganin jiddah ta fito, tana nufo ta, ta yunqura da gudu ta shige dakin ta hade da saka key, still uwani batayi shiru,
Ai ba tsoron ki nake ji tausayamaki nake saboda cikin jikinki, da sai na farfasa maki baki yau, sai na jimaki ciwo kin kwanta a asibiti, insa likita ya cire min wannan baqar xuciyar taki, kuma Allah xai sakamin.
Ta sauke numfashi, ta nufi mirror tana kallon fuskarta har tayi wani kumburi, taja dogon tsaki tana shafa fuska, akwai lokacin da xai xo nima xan rama inda baki da ikon dukana, ashe jiddah xata iya duka kenan, tana nufin kyaleni ne takeyi karma ta qara ragamin nima xan dage damtse infara dukanta ne, harda wani kirana daqiqiya har yanxu tana jin haushi saboda naqi karatu to baxanyi ba sai dai ki mutu, sum sum da ita kamar kifin ruwa mtsewwwww.
A ranar jiddah tana cikin bacin rai sosai, shi kansa el'mustapha yaga hakan,
Ko dai jikin ne jiddah?ta dauke kanta gefe batare da tayi magana ba, ya xauna yana kallonta cikin seriousness,
Talk to me jiddah, what's wrong?
Ba komai ta fada a hankali tana kallon,
Akwai komai, from your face nagani, indai ba nine akace nayi wani abin ba,
Idan kaine wannan xaman da kayi a gabana xan rufe ka da duka ne,
Dana ji dadi jiddana ta bige ni, nasan nayi mata laifi ne ta hukuntani da hakan.
Shiru batayi magana ba, babu walwala a fuskarta,
Idan bani bane waye, please tell me...
Uwani ce ta bashi amsa kamar xatayi kuka,
Me uwani tayi?
Iskancin ya tashi kaina ya koma kan iyayena da basu a duniyar ma, I can't take it anymore el'mustapha,
Yaja numfashi yana kallonta, uwani.. Uwani... Uwani... Am tired of her jiddah duk laifin kine, meyasa tunda uwani ke maki rashin mutunci baki daukar mataki, yanxu ta bata maki rai kinxo kin xauna kina fushi kina kuka an you know your condition meke nan,
Tana min gorin iyayenta sun min tarbiya, ita meyasa batayi amfani da tarbiyar da suka mata ba, ta tashi tana fadin idan ban daki uwani ba baxan sami nutsuwa a xuciyata ba.
El'mustapha ya sha gabanta da sauri,
Calm down jiddah, idan kika ce kiyi fada da uwani da wannan cikin ai xata ji maki ciwo, idan taci riba akan ki gobe kome xai hadaku qoqarin fada xatayi dake, respect yourself, tun a lokacin da tayi maki iskanci ya kamata ki dauki hukunci akai.
'Na mare ta sau uku, amma xuciyata batayi sanyi ba, ina jin haushin uwani a yau, I can do anything for her idan bata kiyayeni ba ko.....
'Ashe haka jiddana keda xafin xuciya I don't know, yau uwanin da ake tausayi ce aka Mara har sau uku, how I wish ina gurin ne na ganewa idanuna jiddah ta dauki hukunci da hannunta, ya riqota suka xauna.
Haqurin da kike bani akan uwani nima shi xan baki, wata uku ne xata bar miki miji harda gidan Ma, xata koma gidan iyayenta ta cigaba da xama dama saboda karatu take xaune a gidan kuma ta ajiye batayi kinga sai ta tattara komai nata ta bar mana gida.
'Naji kamar wata uku yaxo gobe, dana sani ban hada wannan auren ba, har yau na kasa gano inda uwani ta dosa akaina.
Is better ki gano jiddah ina so naji kin furta da bakinki uwani taci amanar ki, uwani bata sonki.
Tayi shiru kawai batare da tayi magana ba.
*
Tun daga lokacin suka soma wasan buya, uwani ko kadan bata so taga jiddah ko abinda xai hada ta da jiddah cos a tsorace take da ita tun lokacin da taga fushin jiddah, ashe haka jiddah take, shiru shiru kamar baxatayi fada ba ballantana ta kai ga duka.
Sai plan suke hadawa ita da kurma yanda xasu bullowa su sace jiddah.
Islam ke son banan, yasmeen ta fada tana kallon jiddah, tun ranar da kika aiko ta gidana ya ganta yake min maganarta.
Jiddah ta bayyana farin cikinta tana kallon yasmeen,
Kice banan tayi sa'a, amma yasan wacece banan din kuwa, bana son abinda xai xo ya cutar da yarinyar, marainiya ce bata da kowa a duniyar ni sai ni da kakarta, rayuwar Islam daban ce da banan, she is not dat wise irin yanda Islam ke so you know it, last month ta gama skul.
Tun da Islam yace yana son ta nasan da gaskiya yakeyi yana son ya, kuma kinga shine ya ganta yace yana so har ya matsamin lallai sai naxo na sanar dake, banan tana da kyau kuma yarinyace kamar shi so banga rashin dacewar su anan ba, sai idan kece ba kyaso jiddah.
Lol, saboda me xance baxan so dan'uwanki ba, kinsan yaran yanxu baa masu dole, kuma banda tabbacin tana da wanda take so ko kuma babu, xan tuntube ta yasmeen ki kwantar da hankalin ki insha Allah xata auri Islam nima ina mata sha'awa dashi.
Murmushi yasmeen tayi, ta kawar da xancen tana fadin jiya baban baby ya dawo daga dubai, ya kawo min kaya masu kyau na jaririrai.
Xan gayawa el'mustapha idan ya dawo, sai ki aiko da kayan ya gani duk da ya gama siyayyar kayan haihuwa tuntuni amma nasan idan sun masa kyau xai siye.
Insha Allah xan aiko, wannan cikin naki wai wata nawa ne?
Bakwai ne fa kin ganshi da girma barakallah.
Wlhy kuwa kuma girman ya taso lokaci daya, before ma baa gane kina da ciki, qila wasu biyun ne xasu xo again.
Murmushi kawai jiddah tayi tana fadin Allah dai ya raba lafiya.
Amin cewar yasmeen tana qoqarin barin gidan.
Kinji Islam ke son ki banan, am happy for you, yaron yana da kirki sosai.
Banan ta bata fuska tana kallon jiddah,
Waye shi anti jiddah ni ban san shi ba.
Qanin qawata ne yasmeen, sanda kika je gidan ya ganki yana so, nikam nace xan bashi banan saboda na yarda dashi nasan baxai cutar dake ba.
Banan ta dafe kanta, sai yanxu ta tuna shi, shine Ma ya maidota gida, tayi shiru batayi magana ba, ita dake son el'mustapha ya xatayi da Islam, wai samun guri inji wata xuciyar, masu aiki nawa ne suka sami irin gatan da ta samu saboda jin dadi xatace xata auri mai gidan, baxata iyama anti jiddah hakan ba.
Taji muryar jiddah na magana, idan kuma kinada wanda kike so ne to, baxan maki dole ba, duk wanda kike so dashi xaa yi, buri na ki auri wanda xai riqe ki amana kuma yasan darajar ki, kada ki biyewa xuciyarki ga samarinnan na yanxu masu qaryar banxa ki xauna kina ta jiran warabuka dan baki da tabbacin xasu fito neman auren ki ko baxasu fito ba, nidai baxan cutar dake ba ko na kaiki inda xaa cutar dake kinsani, kije kiyi tunani akai.
Ta sunkuyar da kanta feeling guilty idanunta suka ciko da hawaye,
Shikenan ta rasa el'mustapha har abada, mutumin da bai san tana yi ba, ita kadai ke haukanta kuma tasan baxai aure ta ba, koma xai aure ta baxata iya xaman kishi da jiddah ba, jiddah ta xama tamkar uwa agare ta yanxu dole kuma xata haqura da el'mustapha ta yaqi xuciyarta na ganin ta cire sonsa.
Ta yarda ta rasa el'mustapha har abada, xata cigaba da rayuwa babu el'mustapha sai xabin Allah, yeah tafi kowa sanin jiddah baxata cutar da rayuwarta ba,
Da gaske kenan da jiddah tace ta kama mai son ta wato Islam domin shi kadai ne yanxu wanda ke son ta, ta rabu da jiran tsammanin wato el'mustapha saboda shine baisan tanayi ba, dan haka ta rungumi mijin da duk Allah ya rubuta mata da hannu bibbiyu Kuma xatayi biyayya ga jiddah dan cimma rayuwa mai amfani a duniya da lahira.
Ta amince ta yarda Islam shine xabin Allah, ta soma siffantoshi a idanuwanta....
Tunanin me kike banan? Jiddah ta katse ta.
Ba komai anti jiddah na amince da duk mijin da kika xaba min, ni mai yi maki biyayyace.
Sosai jiddah taji dadi, banan kuwa ranar tasha kuka kamar me.
Bayan kwana biyu, twins sunje islamiya tare da banan, ba kowa a gidan sai jiddah kadai xaune a falo,
Wayar ta, ta soma ringing, tayi mamakin ganin call din uwani a lokacin, kamar baxata dauka ba sai kuma tayi receiving,
'Dan Allah anty jiddah kixo ki taimakeni, gani a hanya na kasa driving baxan iya dawowa gida ba saboda banda lfy dan Allah kixo ki taimakeni.
Kina wajen ina ne na aiko maki driver kinsan condition dina ai.
'Dan Allah karki aikoshi anty jiddah kixo da kanki kuma kada kixo da kowa saboda duka jikina ya lalace da jini, ashe ina da ciki ne ni ban sani ba, dan Allah kixo yanxu anti jiddah kada na mutu sai ta fashe da kuka.
Jiddah ta rude, yaushe uwani tayi ciki bata da labari, el'mustapha ya munafunceta yanda yake nuna mata babu komai tsakaninsa da uwani.
Ko wane hali uwanin take ciki, abin na buqatar sirri basai taje da wani namiji ba dan batasan halin da xata isko uwanin ba, amma ita kadai baxata iya taimaka mata ba, ta kira uwani a waya,
Kinsan ni kadai baxan iya taimaka maki ba uwani ko naxo da Inna ne,
Aa anti jiddah bana son kowa yasan halin dana ke ciki ballantana mai aiki, ga wata mata anan tare dani bataso tabar motar ta da yaranta a gurin ne da itace xata maidoni gida,
Kina wajen ina ne?
Da kyar uwani tayi mata bayani.
Jiddah ta dauki hijabin ta da key din motarta, batare da tunanin komai ba ta shiga motar ta.
Taxo fita ne wani security ya tsaidata,
Madam ke kadai xaki fita ne, oga yace kada abarki kije ko ina batare da ko daya daga cikin mu ba.
Tace karka damu, its urgent yanxu xan dawo, kafin yayi magana ta ja motar da qarfi ta fita daga gidan.
*
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
Dis page is for you my dear Maryam kaumi, one among d best, Hbd dear.
34
Tafiya tayi mai nisa, a xuciyarta tana tunani kome yaxo da uwani gurin.
Tun daga nesa ta hango motar uwani a gefen titi, ta rage gudun motar tana observing wani abu,
A waya uwani tace akwai wata mata tare da ita da ya'yanta, to ina suka shiga?
Tayi parking nesa da motar uwani, ta cikin glass din ta tsurawa motar uwani ido har ta hango kamar wasu maza a cikin motar, gabanta ya fadi, kada dai uwani ta kirata ne domin ta cutar da ita, dama bata kashe motar ba, ta soma qoqarin juyawa ta bar gurin, abinda bata sani ba tayoyin motar, qusoshin da aka xuba akan titin duk sun fuda motar, ta fito cikin motar da sauri tana kallon motar, sai a lokacin tsoro ya xiyarce ta mai tsanani musamman da ta gane plan ne aka hada mata, ta juya da sauri tana qoqarin gudu amma baxata iya ba saboda cikin da ke jikinta,
Kurma na ganin haka ya fito da gudu daga inda yake boye cikin grass, ba zato jiddah taji saukar duka a qafafunta wanda yayi sanadiyar faduwar ta gurin a sume.
Su uwani suka qaraso da saurinsu tare da wasu maxan abokan aikin kurma, kurma ya yarda qaton qarfen dake hannunsa wanda shine ya bugawa jiddah a qafafu.
Ai na gayamaki idan tayi qoqarin guduwa sai na harbe qafafunta ko na ciresu gabaki daya, inda na bige ta a qafar ina sa rai baxata qara tafiya ba ballantana tayi qoqarin guduwa.
Uwani ta xare idanu cikin tsoro, wayyo Allah anti jiddah baxata qara tafiya ba kake nufi, amma ai munyi magana da kai aciki ba cutarwa.
Saboda kada na cuce tane ya saka ban cire qafafun gabaki daya ba, kuma xan iya babu imani a xuciyata ko kadan ki tambayesu, nine na kashe mahaifina saboda ya kamani ina yiwa qanwata fyade, tunda na kashe mahaifina da hannuna uban kowa Ma xan iya kashewa kuma kowanene akace na kashe sai na kashe shi nake samun nutsuwa,
Uwani ta nufi inda jiddah ke kwance a sume, ta rungumota sosai a jikinta, taji wani tausayinta ya kamata wanda yake sanyata dana sani a yanxu, idan ita ce jiddah baxata taba mata haka ba.
Kurma ya dubi daya daga cikinsu,
Goga dauki matar nan saka mana ita a motar mu kada musa wasa axo a riske mu, ke kuma sati daya kacal na baki ki kawo min kudi na idan kika qi wallahi summa tallahi sai na kashe wannan matar kuma naxo har gidan na kashe ki sai dai nima a kasheni, bana wasa da kudina, ya juya ya fice sauran suka bi bayansa yayin da goga ya dauki jiddah yabi bayansu.
Jiki a sanyaye uwani ta tashi ta nufi motar ta, tana kallo suka sanya jiddah a motar su suka keta cikin dajin, gidansu yana can ciki sosai.
Wata xuciyar ta soma xuga ta, saboda me xata damu ai abin farin cikin tane jiddah ta xama nakasashiya baxata taba moruwa ba kuma el'mustapha baxai taba xama da ita a hakan ba, dole xai dawo mata tunda itace mai lafiya, baxata damu ba tunda har sun furta baxasu kashe taba idan ta kawo kudin, xatayi qoqari ta kawo saboda bata son a kashe jiddah tana so abarta da ranta yanda xata riqa ganinta da el'mustapha tana juyashi kamar yanda ake juya waina, ta saki murmushi,
Wani tunani tayi ta isa motar jiddah ta bude, wayar ta ta ciro, ta sami dutse tayi mata ratsa ratsa, ta cire sim din ta yarda har wayar ba kana ta shiga motar ta tabar gurin da sauri.
Tafiya sukayi mai nisa acikin dajin kafin su iso gidan nasu, gida mai kyau baxaka taba tunanin yan iska ke xaune a cikin sa.
Goga dauko wannan matar sharp sharp,
Goga ya dauki jiddah
Ya shiga da ita gidan, wani daki suka kaita suka kwantar da ita, kurma ya dauko qaton bucket cike da ruwa ya watsa mata batare da tausayi ba.
Har lokacin bata motsa ba, ya sake debowa ya watsa mata, ta saki ajiyar xuciya, numfashin ta na dawowa a hankali.
Abinda ya faru ke dawo mata akai, sanda kurma ya bigi qafarta wani irin radadi da axaba da taji tunda take a rayuwa bata taba jin irin sa ba, ta bude idanuwanta da sauri tana kallon dakin da take, ambaton Allah take a xuciyarta, ta soma qoqarin tashi amma me qafar ta riqe bata iya motsa ta ko kadan,
Meke nan? Ta maida dubanta ga qafar cikin rudani, meke faruwa, meyasa na kasa motsa kafar, meya sami qafar, innalillahi wa Inna ilaihir raji'un, ta saki wani kuka sosai gwani ban tausayi.
Jiddatulmusty 😒
Uwani tana xuwa gida ta shigewarta abinta kada Ma a xargeta akan batan jiddah,
Ita yanxu abinda ke damunta yanda xata sami million biyu, ta sani idan tayi wasa tsab kurma xai iya kashe su ita da jiddah, ta ciro wayarta ta kira jamcy,
Tayi ta ringing bata dauka ba, haka ta sake gwada kira, gab da xata tsinke ta dauka, abinda taji jamcy na furtawa a bakinta yayi tsananin rudata,
Uwani ina cikin wani hali, guy din dana biyo muka xo ashe yana dauke da cocaine, sun kama shi sun tafi dashi gani bansan inda xan nufa ba nima nemana suke.
Uwani ta tsinke wayar yayin da dakin ke juyawa da ita, har wani duhu take gani a idanuwanta.
Banan suna dawowa makaranta taje da yaran ta cire masu uniform na islamiya, ta shiryasu cikin kayan su na gida.
'kuje ku gaida momy kafin naxo, suka nufi sashen jiddah da gudu.
Mummy... Mummy we are back,
Dakin ta suka nufa bata nan, kitchen bata nan, toilet, har sashen el'mustapha suke bata nan suka sake komawa dakinta, aryan ya kwanta saman gadonta yana kuka,
Momy ta tafi ta barshi ita da daddy yau baxai ci abinci ba.
Arham bai damu ba, keken sa ya dauko ya soma yawo da ita a tsakiyar dakin yana wasa tare da bindiga a hannunsa na yara.
Uwani na jin kukan aryan ta qara lafewa tana xaginsa a xuciyarta, yau babu momy sai dai kaci ubanka, kaima daqiqi yanda mamanka ke cemin daqiqiya, kuma daqiqai ne wawaye kawai.
Tun da banan ta nufa falon take jin kukan aryan