Showing 48001 words to 51000 words out of 138779 words
Chapter 17 - El-mustapha Complete Hausa Novels By Fertymerh Xarah.docx
da hijab a duk lokacin da xasu shigo.
Bata da rawar kai duk sanda xasu shigo sai ta gaidasu kuma kome suka ce bata masu gardama illah ta gyada kanta wannan dalilin ya saka kurma jin tausayin jiddah a karo na farko a rayuwarsa daya taba tausayin wata halitta.
Ya xuqi sigari yana kallon jiddah,
Tunda uwata ta haifeni ban taba tausayin kowa ba sai ke, saboda sanyin ki da haqurin ki na lura ke Sam baki da hayaniya, sabanin wasu mata da muke kawo wa nan, daga masu tsiwa sai yan iska ni kuma tattakasu nake, na sa belt na xane shegu idan kuma yarinya ta matsamin na dauke ta da alburushi wanda ya kawo ta yamin maganar banxa na kashe shi haka nake kurma game da kissa.
Jiddah ta sunkuyar da kanta tana share kwallah,
Saboda cikin da ke jikinki xan tausayamaki, na dauko maki tsohuwa a cikin gari xata kula dake kullum na maidata dan baxata xauna dake ba, idan kina jin fitsari ko kashi ki daina rarrafawa ita xata kula da komai, waccan shegiyar matar da ta bamu ajiyar ki itace xata biyata dan ubanta, ta biyamu ta biya wannan tsohuwar tace yau xata xo ta kawo kudin, in kuma qarya take min wlhy cikin ta xan farke har cikin gidan mijin nata, yama kika ce sunanki.
Hauwa ta bashi amsa kanta a sunkuye dan bata qaunar ganinsa ko kadan.
'Yauwa sunan uwar babana ce amma ana ce mata kuluwa dan haka kuluwa xan riqa kiranki dan ni bana girmama kowa a rayuwata, uwata Ma kai tsaye nake kiranta da Ladidi, ya juya ya fice yana tangadinsa na maye, jiddah tabi bayansa da kallo tana sharar kwallah.
Baa jima ba taji uwani a gidan, tana jin su suna kururuwa sunga kudi.
Ina kika sami kudin bayan kince baki dasu,
'Na mijina ne na dauko jiya bayan ya fita😀
Kinyi qoqari, saura na waccan tsohuwar dana gaya maki tana kula da kuluwa, dubu dari biyu ne kudin ta.
Uwani ta bata fuska, batayi magana ba saboda tsoron kurma tasan tsab xai iya dukanta a gurin idan ta musa, sai tace idan xata dawo xata xo dasu.
Suka bude kudin suna dubawa suna jin dadi.
Ina so naga anti jiddah, da hannu suka nuna mata dakin da take.
Jiddah ta rumtse idanuwanta, babu abinda ta tsana a duniyar nan kamar ta dora idanunta a fuskar uwani, ta tsane ta bata son ta ko kadan, to me uwanin taxo tayi a gurinta.
Ayyah anti jiddah haka kika dawo cewar uwani bayan ta shigo dakin.
Kiyi haqurin son mijinki ne ya sakani, kuma gashi har yanxu yaqi ya bani lokacinsa da kulawarsa, bashi da wata damuwa sai ta jiddah, ni kam ya xanyi ne a rayuwata ya soni ki gayamin anti jiddah me kika masa ko kin hada da boka ne.
Shiru jiddah batayi magana ba kuma bata bude idanuwanta ba, uwani ta dafe kanta da goshinta, el'mustapha ya raina min wayo yana hada matsayina da banan, saboda na bigi aryan ya gaya masa ya kecewa duk na sake dukansu banan ta dauki mataki akai, to idan na kashe su ban san wani mataki xaa dauka ba musamman Ma idan na kashe jiddah.
Nan ma jiddah ko motsi batayi ba da uwani xata gane da taja komatsan qafafunta ta tafi ta bar jiddah.
Duk da haka ga zannuwa na kawo maki guda biyu ki qara saboda wannan dake jikinki sunyi datti ga tsamin dauda hala bakya wanka ne.
Jiddah ta bude idanuwanta a hankali tana kallon xannuwan da uwani ta miqo mata, hannu tasa kamar xata karbi xannuwan sai ta fisgo uwani qiris ta fadawa jikinta, ta fadi gurin, takaicin jiddah babu wani abu ko makami a dakin da xata illata uwani, ina Ma qafarta daya nada lafiya ta miqe sosai yanda xataji dadin dukan uwani da kyau.
Ta shaqo wuyan uwani kamar iya qarfinta tana buga kanta a qasa, uwani ta soma ihu tana neman taimako, shigowar su goga ya saka jiddah sakin uwani dan bata qaunar wani daga cikinsu ya taba ta da sunan xai kwaci uwani a hannunta, ta soma kuka.
Uwani ta tashi tana huci, kallabinta a hannu ta gyara rigarta tana kallon jiddah,
Kin jawa kanki anan xaki tabbata ko nasa su kashe min ke, kuma wlhy sai na rama a gurin ya'yan ki.
Ta fice a fusacce goga yabi bayanta dama shi kadai yaxo idan ta kurma ne su kashe kansu ko a jikinsa.
Banan dauke da arham a jikinta, bai da lafiya sosai xaxxabi ke damunsa, dawowar su daga asibiti kenan tare da el'mustapha.
Kallonta yayi cikin tausayawa yanda take bata lokacinta gurin kula da yaran ta xama kamar jiddah a gurin su abinda uwani ce ya kamata tayi, kuma iyayensu ba yanda basu so karban yaran ba el'mustapha ya hana yafi so yaransa suna hannun sa.
Allah xai saka maki banan, bani da bakin da xan gode maki amma Allah kadai yasan abinda ke xuciyata game da kulawarki ga yarana, sai kuma yayi shiru yana sharar kwallah.
Ki gayamin abinda kike so daga gare ni insha Allah xan maki shi ko menene.
Banan ta dago tana kallonsa, tausayinsa ya qara mamaye xuciyarta, yanda el'mustapha ya dawo abin tausayi ne ga duk wanda ya sanshi a baya,
Taji ina ma xata kasance dashi da ta dawo masa farin cikin da ya rasa a baya, da ta maye masa gurbin jiddah, amma Sam baxata iya hakan ba ta riga ta sanarwa jiddah ta amince da Islam kuma koda ace jiddah bata raye tabbas sai ta cika mata burinta na auren Islam domin yanxu sun soma dai dai tuwa.
Ba komai ina yine saboda Allah da qaunar mahaifiyarsu, dawainiyar da kukayi dani tun ina yarinya ya isa nima na dauki dawaniyar yaran ku.
Allah ya saka maki da alheri, ki qara kulamin dasu ki masu duk abinda suke so kuma ki kare min su kada ki bari suma a cutar min da su.
Ya tashi ya fice daga gidan, arham ya soma amai sosai ta ajiye shi ta fice da sauri da xumar ta dauko abinda xata gyara wurin.
Sai ga uwani ta shigo gidan tana huci, ba xato ta taka amai ta dubi arham din batare da tunanin komai ba ta dauke fuskarsa da Mari dai dai lokacin banan ta shigo dauke da tsumma da Cup na ruwa a hannunta.
Banan ta saki Cup din da tsumma ta sha gaban uwani dake qoqarin shigewa dakin ta, arham sai kuka yake yana kiran mummy.
Me yayi maki kika dake sa Uwani?
Kallon ta take da mamaki,
Yau kuma Uwani xaki kirani babu anti lallai yarinyar nan saboda na daki yarana kike tambayata ko wadda ta haifesu bata isa tamin wannan isar akan su ba.
Uwani me arham yayi maki kika mare sa, shi nake tambayar ki,
Uwani taja da baya ganin ganin banan din na shigowa cikin ta kamar xata dake ta,
Saboda xai yi amai anan tsakiyar falo naxo na taka, kuma ke me ya hana tuntuni kixo ki kwashe.
Oh saboda kin taka aman sa kika mare sa, yaron da ko lfy baida, to idan aman ya taba jikin ki kuma ya xakiyi.
Uwani tace kamar ya tana kallonta, banan ta riqo hannunta uwani ta soma kiciniyar kwacewa sai suka soma dambe a falon, arham ya rude musamman da yaga ankai uwani qasa, ta soma kururuwa tana kiran mutanen gidan taimako.
Banan ta cusa kallabinta a bakin uwani ta rufe yanda kowa baxai ji ba,
Yau duk uban da xaki kira yaxo ai na dake ki dama ina ciki dake, ina ganin take taken ki akan yarannan ba kya tausayin su, kinsha duka na ina kyaleki yau duk xan fashe, ki kira qaumi ko hajja duk basu isa su hana na dake ki ba,
Batare da tunanin komai ba ta goga fuskar uwani a cikin amai, yanxu sai ki mutu ko kuma idan kin tashi kada kibarshi da rayuwarsa....
Kai kai kai me nake gani haka cewar el'mustapha bayan ya nufi inda suke da sauri, ya dauke banan daga jikin uwani sai huci take kamar Serdia a filin dambe.
Uwani ta tashi tana cire kallabin bakin ta ta nufi banan da niyar kai mata duka el'mustapha ya hana,
Me ya faru ne,
Saboda arham yayi amai ta taka shine ta mare sa bayan ta san kuma bai da lafiya, yanxu da na sa mata aman a fuska nake son ganin matakin da xata dauka akaina ko akansa.
El'mustapha ya dauki arham dake kuka yana kallon fuskarsa, ya kalli uwani yanda tayi wani xuru alamar ta daku a gurin banan, ga aman duk ya bata jikinta.
Murmushi yayi har a ransa yaji dadi, Sam ya lura banan bata da haquri kamar jiddah,
Xo ki gyara falon banan, kije kiyi wanka ki huta ni xan kula da shi kinji, sannu da qoqari Allah yayi maki albarka.
Ya dubi arham,
Is ok yaro na no need to cry again, baka ga anty banan ta rama maka dukan ba ai ko ba komai mutum yasha aman ka You have to be proud of it, kuma ba wanda ya isa ya taba ka, idan kuma mutum ya qara gigin taba min kai ko aryan xai sha mamaki kuwa, ya fice.
Wanka yayi wa yaron, ya bashi magani bayan ya sha tea, ya kwantar dashi inda aryan ke barci tun daxu bai san wainar da ake toyawa ba.
Dakin uwani ya nufa lokacin ta fito wanka daga toilet kenan tana tunanin qila sai ta hada banan da kurma, itace matsalarta a yanxu.
Kallonta el'mustapha yayi qasa da sama,
Kudin da kika dauka dakina naxo kibani abuna?
Gabanta ya fadi, kamar ta saki kashi a gurin yanda cikinta ya murda,
Tace ni ban dauki kudin ka ba, ni da baa xuwa dakin ka.
Ki gayamin gsky me kika yi da kudin da kika dauka a dakina, just tell me uwani, tun da nake xaune da jiddah bata taba min sata ba, cikin wannan bangare babu mai shigowa acikin maaikatan gidannan sai banan kuma nasan baxata dauki kudi na dan bata taba xuwa ko falona ba ballantana daki na, ina kika kai kudin.
Jikinta ya dauki rawa ta fara rantse rantse tana hawaye ita bata dauka ba an mata sharri ne dan ko aljannunta basu sata.
'Naji shikenan baki dauka ba, kuma duk wanda ya dauka asirin sa na gab da tonuwa har da mai sa hannu a batan jiddah very soon xan gane.
Kije na sake ki saki daya saki biyu, dan babu kyau yin uku ne da nayi maki mai gaba daya, na aure kine saboda jiddah babu jiddah a tare dani babu amfanin xamana tare da ke, ba kyason yara na ban son ki, kuma baxaki bar gidannan ba xaki xauna ne har sai ranar dana ga jiddah, har yanxu ke nake xargi kuma ina bincike akan ki, ya juya ya fice yana so yaje yayi tracing layin jiddah agani waye ya kirata urgent, abinda ya kamata yayi tuntuni amma saboda tashin hankali da damuwa baiyi wannan tunanin ba.
Pherty... ✍🏻
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
37
Ya fito harabar gidan yana kallon securities,
Kada kubari uwani ta fita a gidannan, idan kuka yi wannan saken a yau wlhy ran ku xai yi matuqar baci fiye da kuskuren da kuka yi a farko.
Ya isa ga motar sa dai dai lokacin da wayar sa ta dauki qara, yana dubawa anty ikram ya gani, yayar sa.
Ya dauki wayar bayan ya kara a kunnensa,
'autan mama, kaxo asibiti jikin mama yayi tsanani sai sunan ka take kira.
Ya tsinke wayar batare da yayi magana ba, da sauri ya shiga motar ya bar gidan abinda ya mantar dashi xuwa mtn office kenan🤦🏻♀.
Uwani tun daxu tsaye take, ta kasa xama ta kasa gasgasta abinda kunnuwanta suke jiye mata, el'mustapha yayi mata saki biyu, aa bata yarda ba kunnuwanta basu jiye mata da kyau ba.
Jikinta ya dauki rawa, lokaci daya xaxxabi mai xafin gaske ya taso ya rufe ta, jikinta yayi xafi rau, da kyar ta isa bakin gado ta xauna, sai ga hawaye sharrr na bin kumatunta.
Ji take duniyar ta mata xafi, duniyar Ma gabaki daya juya mata take, wani duhu ya mamaye idanunta, duk wani motsi ko sauti bata jinsa a kunnuwanta, sai ta gigice ta fashe da kuka mai tsananin gaske kukan da bata taba irin sa ba,
Ta rasa el'mustapha har abada, ta rasa wannan abin da take matuqar so da qauna, ta rasa wannan abin da take gani tana gab da samuwar sa, ta rasa wannan abin da ta wulaqanta yar uwarta saboda shi, ta rasa wannan mutumin mai matuqar tsada da muhimmanci a rayuwarta, el'mustapha yayi mata nisan da har abada baxata taba samun sa ba, ba ita kadai ba har jiddah ta gama samun sa, idan ta rasa shi shima xai rasa jiddah, jiddah Ma xata rasa shi, kowa ya rasa, indai tana numfashi a doron qasa el'mustapha da jiddah baxasu taba kasancewa tare ba.
Idanunta suka yi jawur saboda kuka, da kyar ta janyo wayarta ta soma neman layin jamcy, kusan sau biyar tana kiran layin baya shiga, ta tashi da kyar ta xura doguwar riga, qaramin mayafi ta dora akan ta, key din motar ta kawai ta dauka ta fito da kyar tana layi saboda axababben ciwo da kanta keyi.
Horn tayi alamar a bude mata gate din, amma aka qi, tayi magana suka gayamata abinda el'mustapha yace, bata damu ba saboda yanda take jin jikinta, tana komawa dakin ta ta fadi ragwaf, xaxxabi mai xafin gaske ya rufe ta.
El'mustapha kuwa yana isa asibitin kai tsaye ICU ya nufa,
Gaba ki daya mama ta fita hayyacinta ba abinda ke fitowa bakinta sai el'mustapha, hannunta ya hada da nashi bayan ya tsugunna a qasan gadon da take kwance.
Magana take yi a hankali da kyar yake iya jiyo abinda take fada, da alama wasiya take bashi musamman akan yayyunsa da yan uwansa, ya rumtse idanunsa sai ga hawaye na xuba, jikinsa ya dauki rawa lokacin da yaji tana kalmar shahada, kafin wani lokaci numfashin ta ya ajiye.
Ya bude idanunsa sosai yana kallonta, no he can't believe it, mama ta mutu yanxu a hannunsa, ya soma jijjigata a hankali yana kiran sunan ta.
Da kyar nurses suka fitar dashi dakin,
Idan el'mustapha dake namiji yayi kuka akan mutuwar mama, mu da muke mata mu ce me? Cewar anty ikram tana kallonsa bayan ta riqo hannunsa.
'Anty yusrah tace ba kuka xamuyi mata ba addua ce, kukan mu baxai amfanar da ita da komai ba, kuma ta roqa ko bayan ranta kada muyi mata kukan mutuwa.
'Anty ikram da kanta ta soma share masa hawayen, a yanda el'mustapha yake jin kansa tamkar qaramin yaro, yau ya rasa maman sa, yayi kukan mutuwa a karo na biyu bayan na baban sa, bai san wanene na uku a rayuwar sa ba.
'Anty ikram, mama has gone, shikenan babu uwa babu uba, shikenan baxan qara kwanciya a jikin mama ba, baxata qara min fada ko rarrashi na ba, mama baxata qara bani abinci a baki ba, mama baxata qara saka ni dariya ko share min hawaye ba,mama baxata qara shafa kaina ta samini albarka ba, tell me meyasa baxan yi kuka ba, meyasa baxan xubar da hawayen rashin uwa ba?
Daga anty ikram har anty yusrah kuka suke,
Inna lillahi wa Inna ilaihir raji'un, shine abin da mutane ke Nana tawa a xuciyar su a duk lokacin da suka ji mutuwar mahaifiyar AIG, Mace mai fara'a da karamci, kowa nata ne babu kyama ga talakawa haka kuma bata koyawa ya'yanta su kyamaci wani mutum a duniya ba duk yanda yake.
Bayan sadakar bakwai, abubuwa suka soma yiwa el'mustapha yawa, ya saka mama a xuciyarsa sosai yake mafarkinta, bashi da nutsuwa a koda yaushe sai nema mata gafarar ubangiji.
Anyi saa uwani tayi masa gaisuwar mutuwar cikin nadama da qasqantar da kai kamar mai roqon el'mustapha xai maidata.
*
Inna ige yau kam ina jin motsin abinda ke cikina, ina roqon Allah ha rayamin shi har xuwa lokacin da xan haifesa, cewar jiddah tana kallon tsohuwar da aka dauko domin kula da ita cikin murmushi tana shafar cikin.
Ai na gayamaki ina karban haihuwa a karkarar mu, kowa yasan ni ungoxuma ce, tun da nace kisha wannan gayen komai xai warware ai kinga kin sami sauqi.
Jiddah tayi murmushi tana kallonta, nagode Inna ige, kin taimakeni da yawa, kin nuna min so da kulawa babu kyama, ina Ma ina da abinda xan saka maki dashi a yanxu da na baki domin nuna godiyata akan ki.
Karki damu jiddah, da na kowa ne, amma xan tambaye ki, me kikayi aka kawo ki nan?
Hawaye suka taru idanun jiddah,
Banyi komai ba Inna, kishiyata yar uwata ta jefani a wannan halin saboda mijina, ba wannan ne damuwata ba kamar ciwon qafata, dubi yanda ta kumbura, ina tsoron wani abu ya same ni na kasa tafiya a rayuwata.
Inna lillahi, kishiya jiddah?
Jiddah ta maida kallonta ga cikinta tana murmushi, ta daga rigarta tana kallon yanda yake motsi, farin ciki fal a xuciyarta ta san komenene yana cikin qoshin lfy.
Hala shine cikin farko jiddah?
Jiddah ta dube ta tana girgixa kanta bayan ta rufe jikinta,
Ina da yara biyu maza tagwaye, na jima ban sami haihuwa ba kafin wannan, duk abinda ke ciki ina son sa ne saboda ya wahala, jiddah ta bata labarin komai, Inna tayi matuqar tausayawa jiddah harda kwallah tayi.
A yanda na tsani uwani