Showing 81001 words to 84000 words out of 138779 words
Chapter 28 - El-mustapha Complete Hausa Novels By Fertymerh Xarah.docx
wannan qoqon ta debo abin a yatsa, ita Ma yarinyar ta diba kowacce ta sunkuya suna shafawa a qasan su.
Lokaci daya suka dago suna kallon juna idanunsu a waje saboda wani radadi da suka ji......
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
50
Da gudu kowacce su ta nufi toilet neman ruwa.
Hargowar da suke ya dakatar da uwani daga kukan da take, ta kashe kunne sosai tana sauraren su,
A hankali ta tashi ta nufi dakin basa nan suna toilet, tayi shiru tana tunanin ko ihun me suke haka? Qilama iskan cin ne suke, yan iska.
Sadaf sadaf ta shiga dakin, hanyar toilet din ta nufa, qofar a bude take ta leqa taga me suke yi haka ne,
Abinda ta gani ya saka ta xare ido hade da dawowa baya da sauri tana kallon qoqon da ta sakawa yaji.
Gabanta ya tsananta bugawa ta san mai hana suci ubanta yau sai Allah,
Ta dora hannuwanta duka biyu aka sai ga hawaye shar na bin kumatunta,
'Na shiga uku ni uwani, Allah na tuba ka yafe min ka ceceni,
Ta fita daga dakin da sauri, harabar gidan ta nufa tana kallon gate din gidan,
Ta rasa yanda ake bude wannan gate, ga katangar mai tsayi ballantana ta haura.
Dabara ta fado mata, xata sami mabuya ta buya idan sunxo fita da mota ta fita ta gudu, ta koma cikin gidan da sauri dakin nasu ta nufa har lokacin basu fito ba.
Ta kyalkyace da dariya tana jin wani farin ciki a xuciyarta yanxu, ta qara leqawa tana kallonsu yanda suka bada muhimmanci wajen wanken abin da ruwa, ta dora hannunta a baki tana dariya🤭,
Jakar hajiya Mariya ta bude batare da tunanin komai ba ta dibi kudi bata san ko nawa bane, jikinta na rawa ta fice daga dakin, can harabar gidan ta nufa ta boye bayan wata flower tana jiran fitowarsu, yau kam xata bar garin sai inda hajiyarta, sai murna take.
Sun dauki kusan rabin awa aciki kafin su fito kowane fuskarsa ba annuri tunanin budurwar sharrin hajiya ne ko dama da saninta, sai ta soma hada kayanta tana maida kayanta a jiki.
Kallonta hajiya tayi sheqeqe,
Tace me kike yi haka Hadixa, ba dai tafiya xakiyi ba.
Batayi magana ba ta dauki jakarta da gyalenta, hajiya ta riqo ta da sauri,
Kiyi haquri wallahi ba laifina bane, ni kaina bansan da abin haka yake ba, kuma ko da safe da naje gurin ki na saka shi lfy lau ba wannan abin, ban san menene aka saka ba, banma san wanda ya saka ba, amma kiyi haquri ki tsaya har gobe kinji.
Ko na tsaya ba abinda xan iya maki, gurin xafi yake min sosai, ina so naje gida na duba kaina,
Haba hadixa yanxu ya kike so nayi, xo ni nasan yanda xan maki ya daina xafi, nima nawa ai xafin yake amma na haqura.
Bata saurare ta ba ta fice da sauri saboda xafin da take ji, tana son taje gida ta baje gurin a iskan fanka, idan tace tayi hakan gaban hajiya baxata barta ba da jarabarta.
Fitowarta duk akan idon uwani dake labe, tayi mamakin yanda ta bude gate din kai tsaye, dama dai ban iya bane, tana ficewa uwani ta biyo bayanta da gudu ta bar gidan har tana bankade hadixa a hanya, bata damu ba ko waiwaye burinta taga ta fice daga unguwar gabaki daya.
Sai safa da marwa take tsakiyar dakin cikin tunanin ko waye xai mata wannan danyen aikin.
Uwani ta fado mata a xuciya, lallai kuwa xanci ubanki a yau domin ke xan saukewa buqatata ko kina so ko bakya so,
Ta fita a fusacce tana kiran uwani, shiru baa amsa ba, ta soma duba wa ko ina tana kiran sunanta,
Wayam babu uwani ba alamarta, tana fitowa harabar gidan taci karo da gate din a bude.
Taja numfashi cikin jin haushi, rufe gate din tayi ta koma cikin gida tamkar xuciyarta xata fado saboda haushi da baqin ciki, Allah ya hada ta da uwani ko a hanyane.
Uwani na barin gidan a haukace ta shiga taxi sai tasha, duk da dattin dake jikinta bata damu ba, haka ta shiga motar ana hantarar ta da kyamarta ko a jikinta illa qara baje duwawu da tayi tana fadin
Mutum kudi ya biya na biya muka shigo motar, bata gidan uban kowa bace ballantana a fiddani, wanda ke jin wari ya saka hancinsa a window ina ruwana, ta cigaba da cin biredi ta da pure water batare da damuwa ba.
Da yawa kallon da suke mata a motar bata da hankali, in ba haka ba wane marar hankali xai fito haka ba mayafi ba takalmi kuma cikin datti, bugu da qari cin biredi da pure water cikin maxa.
Tana gama ci ta qulle sauran biredi ta rungume abinta a qirji tana fadin,
Duniyar nan bata da tabbas idan kayi sake ayi maka sakiya, nasan mutane da yawa acikin motar nan guntun biredi nan suke jira idan nayi sake a sace min na rasa wanda ya dauka yanda ake ta kallo na haka, gwanda na rungume abina idan na tashi barci na qarasa cinyewa.
Sai kallonta suke suna tausaya mata qila sabuwar hauka ce, amma da uwani tasan tunanin da suke kanta na cewa mahaukaciya ce da sai ta xage su tsab😂
Suna cikin tafiya barci ya dauke ta rungume da biredi ta, ta kwantowa wanda ke kusa da ita a kafada, sai matsawa yake cikin kyankyaminta yana ture ta, ta bude idanunta da suka soma ja tana kallonsa,
Saboda me kake ture ni, ina ruwanka da barcina, tukunna Ma miye damuwar ka dani banda baqin ciki barcin Ma baxaa bar mutum yayi ba.
Cikin mamaki yake kallonta yace saboda me baxan ture ki ba kina kwanta min a jiki,
Tace to na kudi na biya ba, ai ba bashi bane ko kyauta.
Kudin jikin nawa kika biya ko na mota.
Kudin mota na biya dan haka duk abinda ke cikin motar na biya ina da haqqi akansa, in banda baqin ciki na dauko barci Mai dadi saboda me xaa ture ni a katsemin barci, wlhy aka qara tada ni barci sai dai driver ya tsaya a dokar dajin nan ayi duk wadda xaa yi, taja tsaki hade da gyara kwanciyarta.
Kowa shiru yayi yana kallonta, wanda ke kusa da ita yana ji yana gani ta kwanto a kafadar sa tana barci harda dan minsharinta mai nuna alamar tana cikin gajiya,
Xaiyi magana na kusa da shi ya hanashi,
Yi haquri ka barta baka san haukar nata ko na duka bane,
Driver dake kallon su ta mirror yace,
Malam kayi haquri kabarta dan Allah kaima da ganin yanayin ta kasan abin bai ishe ta ba, karmu xo mujawa kanmu masifa cikin wannan dajin da ta ambata qilama akwai aljannu a tare da ita.
Haka ya haqura ya barta har suka iso,
Slippers ta siya ta sakawa qafafunta tana sauke numfashi sai kallon kallo ake tsakanin mutanen dake kallonta, napep ta shiga, bata dau wani dogon lokaci ba sai gata a qofar gate din su.
Murmushi tayi cikin jin dadi, I miss home, Allah yasa kada abba yamin baqin ciki ya koro ni ya fiye fushi da riqo, taja tsaki tana bude gate din gidan.
Ta shiga tana kallon mai gadin nasu, tsaki taja ta dauke kanta tasa kai tana tafiya,
Ke... Ke... Ke ina xuwa haka, waye ke, wa kike nema ne,
Kerere take kallonsa,
Tace nida gidan ubana kake tambayar ina xanje, chab,
Yace 'au ashe uwani ce ai sai da kika yi magana na gane ke, ke kuma haka duniyar taxo maki da nata salon,
Kadai iya bakin ka, ina nan ba canxawa nayi ba, nadama kawai nayi, ta fice fuuuuuu
*
Awa biyu kacal suka rage daga cikin awannin da likita ya dibawa jiddah, kuma har lokacin bata farfado ba.
Gabaki daya hankalin su a tashe yake, bama kamar hajiya tayi kuka sosai kamar ranta,
'Anty yusrah duk ta jigata saboda fitinar jaririyar, madarar da ake bata taqi karba, an goyata taqi barci sai kuka,
Da kyar el'mustapha ya kalle su, wai baxa kuje gida haka bane, tun daxu nake maku mgn.
Muje gida muyi me el'mustapha, hankalin mu baxai taba kwanciya ba, cewar yusrah.
Ya karbi jaririyar hannun banan yana kallon fuskarta tayi jawur sosai, wataqila akwai abinda ke damun yarinyar take wannan fitinar tun daxu, ya bawa yusrah yana fadin,
Sister ko xakije da ita inda dan gidanki ya duba ta, ina ganin bata da lfy fa,
Ta karbeta tana fadin, nima nayi tunanin haka, ko cikin ta ke ciwo.
Yayi shiru baiyi magana ba, yana kallo suka fice, yunwar cikin sa Ma ta ishesa amma bashi da kuxarin sakawa cikinsa komai banda ruwan lemu tun daxu.
Dakin da aka kwantar da jiddah ya nufa, xama yayi kusa da ita ya tsurawa fuskarta ido yana kallo,
Hannunsa ya saqala cikin nasa ya matse a hankali,
'ya kamata ki tashi haka jiddah, we are ol here for you, idan kika tafi kibar twins a gurin wa, with our new baby,
Ya xubawa agogo idanu, awa kadai ya rage, ya juya yana kallonta gabansa na tsananta bugawa,
Pls jiddah, ko kadan ne ki motsa, time is going, ki bari mu rayu tare da ya'yan mu cikin farin ciki as before,
Shigowar dr merah ta katse sa, suna hada ido el'mustapha ya dauke kansa gefe,
Dr merah bai kula sa ba, kai tsaye gurin jiddah ya nufa ya soma duba ta yana kallon time,
Shi kansa hankalinsa a tashe yake, amma meyasa bata farfado ba har wannan lokacin, ya soma dubata yana examine wasu abubuwa, duk dube dubensa ya kasa gano wata matsalar a tare da ita komai is normal.
Yayi shiru yana qara duba time, 30mnt ya rage, shi kansa el'mustapha wannan karon tashi yayi har lokacin hannunsa na riqe da nata.
Duk suka yi shiru an rasa mai magana a cikinsu illah idanu da suka xuba mata kowane cike da fargaba,
Pls jiddah... El'mustapha ya fada cikin rawar murya kamar xaiyi kuka, Dr merah ya kallesa tausayinsa yake ji,
Hajiya da banan suna tsaye ta window suna kallo binni binni suke sharar kwallah,
Sunkuyawa el'mustapha yayi dai dai kunnenta, Allah kadai yasan abinda yake fada a kunnen nata, yana jin sanda agogon dakin ya buga,
Ya tsaida hankalinsa da tunaninsa cak cikin faduwar gaba, a hankali ya dago yana kallon jiddah har lokacin bata motsa ba,
Ya maida kallonsa da sauri ga dr merah idanun sa cike da kwallah,
Can't believe jiddana is death, inaji a jikina bata mutu ba xata tashi, ka qara bata awa daya xata tashi,
Magana yake kamar xautacce yana fadin xata tashi, jiddah ki tashi pls, You promised to be with me, idan kika tafi ya kike so nayi rayuwa without you, ba uwa ba uba kuma ba jiddah, miye amfanin duniyar.
Har lokacin bata motsa ba,
Dr merah ya riqo kafadarsa cikin sanyin jiki ya hada shi da jikinsa, rarrashinsa yake cikin kalamai masu sanyi,
Jiddah has gone kuma baxata taba dawowa ba, inda taje ya fiye mata nan duniyar da duk abinda ke cikinta, kuma kowane mai rai sai yaje inda taje.
Yaja hannunsa suka fito yana waiwayen jiddah shi kam ya kasa gasgasta jiddah ta tafi, baiji hakan a jikinsa ba gani yake xata tashi su cigaba da rayuwa cikin farin ciki.
A hankali ta bude idanuwanta, tana Jan numfashi da kyar,
Dishi dishi take gani kafin idanun su fara waye wa tana kallon dakin da take kwance, a hankali ta juya ta window ta tsinkayo wucewar el'mustapha yana kuka riqe a hannun Dr merah,
Me ya saka el'mustapha kuka? Ta tambayi kanta, ta qara bude idanunta idan ba mafarki take ba hajiya take gani tana kuka, meya same su?
Ta shafi cikin ta wayam, sai a lokacin ta tuna ashe ta haihu, da kyar ta juyar da kanta tana kallon qafarta yanda aka wani daure ta cikin qarfuna tayi mata wani uban nauyi.
'Alhamdulillah ta fada a hankali, koda babu qafar nagode da rayuwar da Allah ya bani na cigaba da rayuwa cikin ya'ya na da mijina.
Ta lumshe idanunta a hankali tana hawaye...
Follow an vote pls🙏🏻
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
51
Sallama take ba kakkautawa kamar wace aka ma dole.
Abba na xaune a falo yana jinta, muryarta kawai da yaji sai da gabansa na fadi, baisan me ya dawo da ita gidan ba.
Yayi shiru yana cigaba da Jan carbinsa batare da ya kula ta ba,
Ta gaji da sallamar taji baa amsa ba taja dogon tsaki, sai ta fada falon kai tsaye tana qunquni, taxo gidan ubanta ana ji tana sallama an kyale ta saboda ana baqin cikin dawowar ta.
Tana ganin abba ta xube qasa, sai gaidashi take tana washe baki,
Kallo daya yayi mata ya dauke kansa, baiyi mamakin yanda yaga ta dawo ba yama so tafi hakan lalacewa yanda xata gane duniya ba komai bace, daga yanayinta ya gane Sam har yanxu batasan rayuwa ba, bata horu ba idan har wannan shegen bakin nata bai mutu ba.
Nayi sallama baa amsa ba, naxo ina gaisuwa an kyaleni, Allah yasa dai bayan rabuwar mu abba ba matsala ya samu a kunnuwan sa ba, ta matsa kadan tana kallonsa hade da yi masa nuni da hannu irin na kurame tana tambayar yana jin ta.
Abinda yaxo ransa uwani ta sami tabin hankali, no wander ya ganta hakan, sai yaji wani iri a jikinsa ko ba komai alhakinta na kansu.
Ke....! Ya daka mata tsawa ganin tana qoqarin tabashi da wannan dattin jikinta,
'au ashe Ma yana ji, ta xauna tana tunxure baki, mutum wata da watanni baya gida kuma ya dawo baxaa tarbesa ba,
Tashi ki bar min gidana cewar abba,
Ta dago tana kallonsa da sauri baki a bude,
'Abba ina kake so naje idan na bar gidan,
'inda kika fito, ko kin manta na gayamaki ba ni ba ke, kije ki xauna da rayuwar da kika xabarwa kanki.
Ta tsuke baki hade da bata fuska, ta gyara xama tana fadi, abba ba tonon asiri ba gidan nan fa nawa ne, gado nane, saboda ni kadai kuka haifa, nayi haquri na barku ku xauna ne tunda kuna raye amma ko mutuwa kuka yi ai gida nane, gado na to meyasa kake korata cikin sa.
Kibari idan na mutu kixo kici gadon ya fada a fusacce yana tashi daga inda yake xaune, tana ganin haka ta tashi da sauri tana kallonsa jikinta na rawa,
Wai abba da gaske kake yi korata kake, ina xanje, wallahi nayi nadama kowa yasan na shiryu, dan Allah kayi haquri ka tausayamin ka barni, ta soma kiran hajiya..... Hajiya... Kixo ga auta ta dawo abba yana Kore maki ita, tana leqen hanyar dakin hajiya.
Get out please, butulu macuciya, duniya yanxu kika fara gani tukunna Ma baki ga komai ba, haqqin jiddah kadai ya isheki.
'Abba wallahi *NAYI NADAMA* baxan qara cutar da kowa ba, jamcy ce ta sakani abba dan Allah kayi haquri ta soma kuka iya gaskiyarta tana bashi haquri, fafur ya murje ido akan lallai sai ta bar gidan.
Ganin da gaske yake kuma yana gab da dukan ta ya saka ta juya tana kuka ta fito gidan, bakin gate ta rakube ta xauna tana rera kuka.
Nida gidana a hana min xama a ciki, wai mai gadi ma ya fini gata a gidan, ita hajiya saboda baqin ciki kada na xauna ko ta fito ta bashi haquri ya barni amma tana jina ta kyaleni, ta cigaba da kukan iya gaskiyarta.
Kowa ma baya sona duk inda naje sai an cutar dani, yaran unguwa sai kallona suke, duk kyawuna da gayuna sun tafi a iska, na dawo kamar wata shegia a gari, wani maraya ma yafini gata a yanxu saboda kawai na cutar da jiddah, Allah ya ga xuciyata yanxu bani da wani mugun nufi a tare dani na shiryu baxan qara cutar da kowa ba ko daukar xugar qawa ama meyasa kowa baya yarda dani ne, ya suke so nayi da rayuwata duk gata na amma dubi yanda na koma a yau kuma anqi a tausayamin, ina suke son naje, ba inda xanje na sake fadawa halaka anan xan cigaba da xama har su yafe min, ta kwanta gurin tana kuka.
Barci mai nauyi ya dauke ta a gurin,
Duk wanda yabi gurin sai ya kalle ta babu mai tunani cewa uwani ce wannan sai dai kallon mahaukaciya ce, yadda aka san uwani da tsabta, ga gayu ko banxa tana da kyankyami akan mutane amma ita ce yau a hakan.
Kiran sallar magrib ya fito da abba da saurin sa xaije masallaci, kicibis yayi karo da ita kwance a gurin, girgixa kansa kawai yayi ya tafi abinsa.
Iskan hadari ya tada ta daga barcin da take, ta qara takurewa guri daya,
'Wannan rayuwar bata min adalci ba idan gaskiya ake bi ai wahalar da nayi jiddah batayi irin sa ba kawai dai dan ta rasa qafafun ne amma ni dube ni kamar yar tasha har wadanda suka haifeni basa sona.
Ba inda xanje anan xan xauna saboda duk duniyar nan ba inda yafi min gidan ubana, koda ruwan nan da xai sauko xai kasheni baxan bar qofar gidannan ba.
'Abba bai dawo gidan ba sai bayan isha, tana ganinsa ta tashi da sauri tana kallonsa.
'Abba dan Allah