Showing 90001 words to 93000 words out of 138779 words

Chapter 31 - El-mustapha Complete Hausa Novels By Fertymerh Xarah.docx

09 Oct 2025

2006

kuma tsab dan sanda mai babban muqami Irina xai iya kamashi.

Dr merah yace duk wata baraxana ta dan sanda bata tsorata ni ballantana tayi tasiri a kaina inada mulkin da xan saka..... El'mustapha ya katse sa,

Aure na, matsalata, matata ba damuwar ka bane is my personal issue da bana son kowa ya saka kanshi aciki.

Ni kuma dole xan saka kaina aciki an you have to listen, labarin da kabani jiddah tana yin komai ne saboda kai da soyayyar da take Ma, kuma dalilin ka ta shiga wannan halin da take ciki, but why kake son auren mai aikin gidan ka can you imagine, har yaushe ka sake mata wannan fuskar, yaushe ka fara sonta, mace mai kyau da aji, mace mai mulki da sarauta kamar ni bata isheni kallo ba saboda ina ganin na aje wadda ta fiye min ita fiye da komai nawa, nima matata ta wahala dani na gayama, har muka haihu ban taba furta mata kalmar so ba cos a lokacin ban gane miye so ba sai bayan tafiyar ta, na gayama yanda ta wahala da yanda tayi rainon sultan da yanda family suka juyamin baya dalilinta, I told you everything about me an Afiya, wahalar da mukayi da juna baxai saka na iya cin amanarta da kowace mace ba ballantana yar aiki thought ba haramun bane amma Sam bai dace ba tun da ita ce ta raineta, ita Ma yarinyar taci amanar jiddah, ka wahala da jiddah, jiddah ta wahala da kai,

Ita Mace komai girmanta yar rarrashi ce da tarairaya, (care and concern) abinda take so kenan daga namijin da take so, wallahi jiddah tana sonka, dubi idanunta ba Komai aciki sai xallar soyayyar ka, kaima kana son jiddah ni shaida ne, but why El'mustapha?

El'mustapha yaja numfashi yana kallonsa,

Yace Wallahi bana son Banan kuma bani da niyar qara aure a xuciya ta da wata mace ballantana banan, baxan boye Ma ba before na fara jin feelings akan yarinyar tun jiddah nada lafiyarta bawai bayan ta nakasa ba, ban taba sanin jiddah tayi wa yarinyar miji ba sai bayan jiddah ta kwanta asibiti sunxo duba jiddah tare dashi.

A lokacin da jiddah fa gayamin banji haushi sosai ba tunda ban riga na kamu da son ta ba, kuma tun daga lokacin bana mata wani kallon bayan qanwa, ta wahala da yarana ta wahala da jiddah, tayi wa yarana riqon da ko mama ke da rayuwa a yau shi xata yi masu bayan ido na, just tell me Merah wanda ya kula da yaranka ya xauna dasu fitsarin su da kashin su xaka iya wulaqantashi? Idan har na dauki banan a matsayin qanwata saboda me baxan sakar mata fuska ba, dole sai ana soyayya ake sakin fuska, ballantana jiddah bata taba kamani da yarinyar nan ba, kawai xargi take wallahi ban taba tsayuwa da banan da sunan soyayya ba, is either akan yarana or gidana da matata, amma ban san xuciyar yarinyar ba tunda jiddah tace wai banan tana sona, ni ban san da wannan ba kuma ban taba lura ba saboda ban damu da ita ba.

'Na yarda da kai el'mustapha shiyasa na gayawa jiddah bana xaton xaka iya cin amanarta, yanxu na fahimci laifin daga ita banan din ne, tana so ta rusa maku farin ciki da xaman lafiya, idan har jiddah tayi mata miji kuma ta amsa a tana sonsa saboda me xata so mijin uwar rainonta?

Mata kenan... El'mustapha ya fada yana jan tsaki, ya lumshe idonsa cikin takaici.

Banan kin gama hada kayan naki kuwa? Cewar yusrah tana kallon ta,

'Na gama anty ta fada a sanyaye, jikinta duk yayi sanyi jiya ko barci bata samu tayi ba saboda damuwa xata je ta daina ganin sanyin idaniyar ta.

A fakaice ta share hawayen fuskarta, tun bata kai wannan lokacin ba take son el'mustapha tana dawainiya dashi a xuciyarta, ta haqura dashi ta karbi Islam a matsayin mijin auren ta saboda a lokacin tana ganin el'mustapha yafi qarfinta kuma uwani baxata taba yarda a aure ta ba.

Soyayyar el'mustapha ta dawo xuciyarta lokacin da ya fara sakar mata fuska saboda tana kula da yaransa wanda hakan ya qara mata qaimi wajen kulawa dasu sosai ganin bashi da wani abu da yake so kamar su da matarsa.

Tana xaune dasu da xuciya daya bata tabajin niyar cutar dasu ba, ba laifin ta bane laifin so ne da baya tunani ko shawara sai dai kawai ka jisa a tare da kai banda haka meyasa so xai mata haka, kuma meyasa jiddah xata bata amanar el'mustapha ta kula dashi bayan tasan ba mutuwa xatayi ba😭

Sanda suka xo asibitin ban kwana da jiddah xasu tafi tana baiwa jaririyar ta mamma, shigowar su ya saka ta janye yarinyar hajiya ta dauke ta tana fadin,

Jiddah bata sha komai na kirki ba, wannan halin naki bana sonsa ke kice bakya iya shayarwa cikin mutane,

Jiddah batayi magana ba suka soma gaisawa da su anty ikram, da kyar ta amsa gaisuwar banan tana qara daure fuskarta,

Suka mata sallama suka fita suna neman el'mustapha, ya rage dakin ita kadai da banan.

Jiran me kike yi anan kika min tsaye, ko el'mustapha din kike jira?

Banan ta dago tana kallonta xuciyarta na bugawa, jikinta ya dauki rawa shikenan ta shiga uku tunda har jiddah ta gano tana son mijinta,

Xatayi magana jiddah ta katse ta,

Kiyi gaggawar cire son el'mustapha a xuciyarki dan baxaki taba auren sa ba, baxaki taba samun sa ba, baxan iya korarki daga gidana ba saboda kin xauna dani da amana da yarana baya ga wannan wallahi Islam din Ma hana maki auren shi xanyi, tsab xan iya nema masa auren yar anty ikram domin itace dai dai da shi ke kije ki auri talaka dai dai dake.

Banan ta soma kuka, dan Allah kiyi haquri anti jiddah kada ki juyamin baya kada ki canxa min fuska...

Baxaki taba ganin annurin fuskata ba har sai kin bar mijina, kuma hankalina baxai taba kwanciya dake ba har sai naga auren ki, saboda banan din dana sani a da ba itace a gabana ba wanna  xuciyarta cike take da cin amana da yaudara idan har xata iya auren mijin jiddah.

'Dan Allah anti jiddah kiyi haquri,

In haqura in maki me, in barki ki auri el'mustapha ko me, kifita daga dakin nan kar na maki illah, kuma kar na qara ganin ki cikin gidana, ki koma can ciki da masu aiki inda kika saba xama, ya'yana ma kada ki qara kula su tunda dasu kike fakewa kina cin amanata, da su kike ganin el'mustapha kina jin dadi, xaki fita ne ko sai na rotse maki kai...

Ta juya da sauri tana kuka kicibis sukayi karo da El'mustapha, ya matsa gefe da sauri,  tafi ta tana waiwayen sa shikenan ta rasa shi har abada...

Jiddah tace ki kallesa a yanxu da nake kwance, watarana kika qara masa wannan kallon idanun xan cire gabaki daya, gani nan bari nan keda shi har abada.

El'mustapha na tsaye yayi shiru ya xuba mata idanuwa, wallahi har a xuciyar shi ya kasa yarda wannan jiddar sa ce tun daga jiya xuwa yau kwata kwata ta canxa ta dawo mai xafi da fushi, bai taba sanin tana da fada haka ba,

Ta juyo suna hada ido ta soma harararsa tamkar idanunta xasu xubo qasa, taja dogon tsaki cikin fushi hade da juya masa baya.

Ko dai jiddah tayi gamo ne, yaushe jiddah xata iya kallonsa ido da ido haka ta hararesa,

Bai yi magana ba sai ya juya da xumar xaije ya rakasu ikram airport, tana jin alamar xai fita ta juyo,

Ina kuma xaka je?

Kome take mamaki take basa,

Yace xanje na raka su anty ikram airport,

Tace aa xakaje dai ka raka banan kake fakewa da anty ikram, ka xauna ba inda xaka je.

Yace ok tor banan xanje rakawa xaki hana ni ne,

Ta yunqura ta tashi da sauri, qafar da aka mata aiki take yunqurin saukowa da ita,

Hankalinsa ya tashi ya nufe ta da sauri ya riqe qafar yana kallonta cike da haushi,

Kina da hankali, keda akace baa so kiyi dogon motsi har kike neman saukowa, kije ina jiddah.

Tace muje raka banan tunda xataje ta barka,

Wai meke damun ki jiddah, meyasa kika dawo kamar wacce bata da hankali,

Tace eh naji bani da hankali indai akan kane baxan taba hankali ba, dalla Malam sake min qafa kuma wlhy ba inda xaka je, xaka je rakiyar anty ikram saboda ku kalli juna kuji dadi barin Ma ita shegiyar dana ga tafi xaqewa wurin kallon ka...

Ganin in baiyi da gaske ba jiddah xata iya bata aikin da aka mata a qafa aiki ya dawo sabo, sai ya kwantar da murya cikin rarrashi duk da bacin rai da yake ji.

Yace shikenan naji baxan je ba, yi haquri ki kwanta jiddah saboda aikin qafarki,

Ta kwanta ba musu hade da dauke kanta gefe,ya gyara xaman qafar kamar yanda take kana yayi tsaye yana kallon jiddah kafin ya nemi guri ya xauna yana kallon ikon  Allah.

Anyi da yawa yau ba qorafi🤦🏻‍♀

Follow an vote...

EL'MUSTAPHA

Haske Writers Association

Home of experts and perfect writers

Fertymerh Xarah💞

54

   Shiru dakin yayi, kowane da saqe saqen xuciyarsa.

Hajiya tayi sallama ta shigo da jaririyar a hannunta tana kuka, a tunanin ta jiddah barci take yanda taga ta lumshe idanuwanta.

Yarinyar nan sai kuka take tun daxu, dama jiddah ba wani abin kirki ta bata ta sha ba,

El'mustapha ya karbe ta, hajiya ta juya ta bar dakin, tsurawa yarinyar idanu yayi, shi kadai yasan tunanin me yake yi,

Ya dago yana kallon jiddah dai dai lokacin ta bude idanuwanta suka hada ido, turo baki tayi ta harare sa tana dauke kanta gefe,

Yace gata ki bata tasha, tayi masa banxa kamar bata ji ba, ya taso da jaririyar yana miqa mata,

Just feed the baby jiddah don't involve her  cikin baqin halin da kika kwaso tsakanin jiya da yau.

Ta bude idanu tana kallonsa, why should I feed her? Inaji kaima kana da shi a qirjinka, ka bata ta sha kada ta dauki baqin halin da na kwaso.

Wai meke damunki ne jiddah, har akwai ranar da xaki iya min rashin kunya, idan nace xanyi auren akwai wanda ya isa ya hana ne, ni ba mijin mace hudu bane ko anyi ni ne saboda jiddah kadai, ko kin manta sanda kike roqona akan nayi aure, You even cry for that, idan har xaki iya tilastamin auren wata yanxu banga abinda xai daga hankalin ki na kishi ba, gida nane I have the right nayi duk abinda nake so kuma nasa duk macen dana ga dama,kiyi abinda duk xakiyi.

Idan har kana tunanin ban isa na hana maka auren ba kaje kayi ni kuma xan nuna maka gida ba nawa bane amma na fika iko dashi dan ba shegiyar da xata xauna a wannan gidan wallahi sai dai na qona shi duka........ Kuka yaci qarfinta, Inna lillahi wa Inna ilaihir raji'un ta fada a hankali cikin kuka, bata taba tunanin akwai ranar da xata iya maidawa el'mustapha magana ba ballantana ta kai ta da yana fada tana fada,

Cike da bacin rai ya miqa mata baby, feed her jiddah.

Nace baxan bada ba, nawa ne ko shima xaa min iko akan shine, ka bata ta sha ko ka kaiwa banan din ta shayar da ita.

Xaiyi magana wayar sa ta dauki qara, yana ganin anty ikram ya dauka da sauri, jiddah ta kafe shi da idanu.

Autan mama yarinyar nan banan tace bata da lafiya na taba jikin nata naji xafi sosai shine nace ko a dawo da ita ne a duba ta tun da duk asibiti ce,

Ya dubi jiddah yanda ta kafe shi da idanu kusan Ma kamar tana jiyo abinda ikram din ke fada, ya tsinci kansa da tsoron jiddah,

Yace aa basai kun dawo ba idan kun sauka taje asibiti amma bari yanxu xan x....

Kaje ina?yaji muryar jiddah baisan sanda ya katse wayar yana kallon taba,

Xanje na duba yarinyar mutane...

Wallahi baxaka je ba, kaje ka duba yarinyar mutane You are not even ashamed of saying that, sai kace akan ka take bani ce na dauke ta aiki ba, wai me kake nufi el'mustapha?

Ke xan ma wannan tambayar jiddah, me kike nufi, sam wannan abin da kika dauko bai dace dake ba.

Baxai taba dacewa dani ba idan har baka cire wannan yarinyar a xuciyarka ba,

Don't you understand, so nawa xan gayamaki bana son yarinyar, ko sai na rubuta a goshina  na nunawa duniya bana son banan, saboda yarinyar nan kike min rashin kunya, telling me any word da yaxo bakin ki, abinda baki taba min ba shi kike min a yanxu, shikenan ki cigaba and don't feed the baby sai me, sai aka ce maki baxata rayu ba, mtsewwwww ya fice da yarinyar a hannunsa, ta bisa da kallo tana sharar kwallah,

Wayarsa da ya ajiye a saman gadon ta dauka  ta shiga neman layin anty ikram amma sam baya shiga, Allah yasa Ma jirgin ya tashi, lallai Ma banan, yarinyar nan da gaske take yi kenan, ai ana barin halas dan kunya amma sam banan bata wannan tunanin, dole xata tashi tsaye kan banan.

Gaba ki daya yinin ranar tayi shine cikin kadaici da kewar el'mustapha tun da ya fita bai sake dawowa ba, abinci ma kasa ci tayi, bata da wannan kuxarin, xuciyarta ta kasu kashi biyu na farko tunanin inda el'mustapha yaje ya barta abinda bai taba yi mata ba, na biyu matakin da xata dauka akan wannan yarinyar dake neman tarwatsa mata farin cikin ta dana mijinta.

Kici abincin jiddah, ga maganin ki Ma baki sha ba, tun daxu sai tunani kike kina kuka kada dai duk akan banan ne?

Ni baxan iya ci ba hajiya xuci.....

Uhm uhm fa jiddah, el'mustapha ya gayamin abinda kika masa sam banji dadi ba, na gayamaki tun farko idan har mataki xaki dauka ki tsawatar wa banan itace mai laifi ba el'mustapha ba,

Ita Ma fa el'mustapha take so hajiya, meyasa suke son rabani da farin cikina, meyasa sai el'mustapha suke so, meyasa mutanen dana yarda dasu na basu amana ta suke yaudara na, na rainesu da hannuna su taso suna son mijina.

Ki kwantar da hankalin ki jiddah, idan har uwani ta yaudare ki ta auri mijinki ta cutar dake banan baxata auri el'mustapha ba, ya rantse baya son yarinyar nan, kema ya rantse maki, ya kike so ya yine xai maki rantsuwa da qarya ne?ni kam ban baki tarbiyar da mijinki yana fada kina fada ba dan baki taba ganin nayi da abban ku ba, idan yana fada shiru nake koda nice da gaskiya indai ransa ya baci na bashi haquri sai kiga ya sauko daga fushin ya xauna mu fahimci juna, ban san ki da wannan ba sam ba halin ki bane, banan din ya kamata ki hukunta ba el'mustapha ba, yaron nan yana son ki jidda.

Amma hajiya s.... bana son gardama idan ya shigo ki bashi haquri kece baki da gaskiya nayi masa rashin kunya ki tsaya ki saurare sa kinqi sai fada kike, kuma kada ki sake sako yarinyar nan a fadan ku har kice baxaki shayar da ita ba.

Jiddah ta fara kuka sosai kowa laifin ta yake gani, sunqi su gane halin da take ciki da abinda take ji a xuciyarta, wane haquri ne batayi ba a baya, wane jajircewa ne batayi ba na ganin ta aurawa uwani el'mustapha wanda haqurin bai mata amfanin komai ba sai Ma wahala da ta shiga, saboda me yanxu xata haqura ta bar banan tana son mijinta, idan su basu san xafi da radadin da ta fuskanta a baya ba ita ta damu da ta ta rayuwar kuma baxata taba bari el'mustapha ya auri banan ba indai tana numfashi a doron qasa.

Ba kuka nace kiyi ba, kici abinci kisha magani, yau na lura ko barcin rana da kike yi bakiyi ba kada ki jawo wa kanki wata matsalar.

Jiddah bata kula ta ba illah kukan da ta cigaba da yi, suna haka el'mustapha ya shigo dakin, duk da taji shigowar sa hakan bai sa ta dago ko daina kukan da take ba.

Hajiya tace naji dadin xuwan ka, taqi taci abinci tun daxu maganin Ma bata sha ba sai kuka take.

Ya ajiye kayan da je hannunsa har lokacin fuskarsa ba walwala akwai sauran fushi a tare da shi,

Yace saqo ne Dr merah yace a bata daga gurin matarshi kafin taxo duba jiddah, ina ji kamar abinci ne aciki.

Hajiya ta duba kayan, abinci ne da kayan marmari na lambu da ganin yanda aka hado kayan fruit din kasan gidan sarauta suka fito, ta debi abinda take so ta fita goye da jaririyar tana fadin idan bata ci ba kanta, ka xauna kaci ka qoshi sauran ka bani na cinye sai tayi ta cin kukan.

El'mustapha dai bai ce komai ba, xuba abincin yayi ya qarasa gurin jiddah, tana jinsa a kusa da ita ta dago tana kallonsa, fuskar nan tasa ba walwala sai taji ba dadi jikinta yayi sanyi, ba qaramin abu ke saka el'mustapha wannan fushin mai tsanani ba.

Ya debo abincin a spoon ya kai bakin ta, ta riqo hannunsa, cikin rawar murya tana xubar da hawaye,

Tace kayi haquri el'mustapha, baxan qara ba.

Yace ba komai ya wuce kici abincin,

Baka haqura ba idan har wannan fushin bai bar fuskar ka ba, forgive an forget baxan qara ba I promise you.

Yasa qaramin yatsansa yana share mata hawayen kafin yace na haqura jiddah

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login