Showing 126001 words to 129000 words out of 138779 words
Chapter 43 - El-mustapha Complete Hausa Novels By Fertymerh Xarah.docx
ko kadan,
Ya canxa mata sabbin furniture ya saka a sabon gidan da xata tare, ko godiya ta kasa masa cos tana ganin yana yin komai ne duk don saboda xai qara aure har wani rawar kai yake a yanda take gani kenan.
Kayan fadar kishiya da ya qara tunkarar ta dasu cikin tsananin fushi tace bata so idan ya tilasta mata da karba xata qona su duka bata damu da abinda ya kashe ba.
Haka ya dauki kayan ya fita dasu jiki a sanyaye, ya nufi dakin sa dasu yasan watarana xata sauko har ta nemi kayan.
Suka tattara suka koma sabon gidansu, kana ya soma gyaran tsohon gidan.
Koda yaje mata da albishir ya biya masu hajji xasu je su biyu bata wani nuna murna ba saboda haushin sa da take ji, kuma shi kansa bai damu ba cikin murna ma yake sanar da ita anty ikram ta gayamasa ai harda jiddah da el'mustapha duk xasu je, da wannan mai aikin jiddah da tayi aure banan duk xasu je, el'mustapha ya biyawa banan din.
Allah ya saka da alkhairi shine kawai abinda ta fada.
Baqin ciki xai ma uwani yawa, kowa xaije makka a barta, a shiga shirgi ba da ita ba🤪.
Bayan sati biyu akaje kai lefen uwani, ba laifi yusuf yayi qoqari sosai.
Tunda uwani taji labarin xaa kawo mata lefe taje tana fitar da tsofin kayanta tana rabawa yan unguwa, takalma da jaka duk bata bari ba, sai labari take badawa a unguwa sabbin kaya xaa kawo mata, ai auren ta na farko baqin ciki ake mata dashi shiyasa mijin ko atampha bai dinka mata ba, yanxu kuma Allah ya bata wanda baya mata baqin ciki mai son ta.
Duk abinnan da ake abba da hajiya basu da labari, akwatunan ta ma ko daya bata bari duk ta rabawa qawaye da masu aure wadanda basu da arxiki sai godia ake mata ana saka mata albarka tana washe haqora.
Wani abin mamaki uwani na bakin gate xaune tana jiran yan kawo lefe, ga yan uwa can acikin gida sun cika sai hidimar kayan tarbon lefen suke.
Tana ganin motoci sun tunkaro gidan ta tashi xumbur ta hangame masu gate tun kafin su kawo,
Qanwar abba ce ta fito ta ganta tsaye riqe da qofar gate ta jawo ta da qarfi tana mata fada,
Tace aa to miye abin fada anan gwaggo, na bude masu ne kada suyi batan kai suje sukai wani gida, idan ba baqin ciki ake min ba ai ba wanda ya fito waje ya tayani xama na jira xuwan su.
Gwaggo ta bige mata baki iya qarfinta, bata wasa sam da uwani, ta riqo hannunta duka biyu ta riqe tana neman abin dukan ta, uwani na ganin haka ido ya raina fata ta soma bata haquri tana roqonta, baxata qara ba ta yafe mata.
Gwaggo taja ta, ta saka ta a daki ta rufe ta, ta barta anan ciki tana fadin inga kin fito a dakin batare da an nemi ki ba.
Sanda suka shigo anyi masu tarba mai kyau kuma duk cikin su ba idon sani dangin yusuf ne kawai.
Har xasu tafi daya daga cikin su cikin wasa tace, bamu ga amaryar tamu ba da yake ba wanda ya santa a cikin mu, ko boyon ta kuke yi ne.
Gwaggo tace baxaku ganta a yanxu ba har sai ankai maku ita, xaku gaji da ganin ta k.... Gwaggo bata rufe baki ba, uwani dake cikin daki a rufe tana jin abinda ake fada ta kunno kai ta window tana fadin gani nice amarya Uwanitilyusuf jikanyar sarki merah.
Duk falon aka juya ana kallonta, ta kuwa xuba masu ido dan bata san su ba, nan fa suke mata kallon mamaki, anya wannan tana da kunya kuwa duk da take kyakkyawa sam bata birgesu ba.
Bayan tafiyar su gwaggo tayi mata duka sosai kuma ba wanda ya hanata saboda ransu yayi matuqar baci da abinda tayi.
Dukan bai bata mata rai ba ta dauki hakan a matsayin baqin ciki ake mata da kada dangin miji sun san ta, bayan ta gama kuka ta share hawayen ta matso ana kallon kayan da ita.
Wani dadi da farin ciki take ji idan ta tuna duk kayan nata ne, lallai ta yarda auren ta da el'mustapha ba alkhairi bane sai talauci da baqin ciki, ta xame jiki tayi dakin ta, tana jin wata nutsuwa na shigo mata, to ko dai yusuf yafi el'mustapha kudi ne, amma ta tuna sanda xai auri jiddah kayan da ya kawo mata ma sunfi wadannan, kenan baya son ta.
Ta dauki marker tabi dakin nata duka da xanen *Uwanitilyusuf* cikin heart, daga qarshe tayi wani rubutu da manyan haruffa wanda ke nuna har cikin xuciyarta she mean it iya gaskiyarta, *I LUV U EL'MUSTAPHA, STILL CAN'T FORGET YOU IN MY HEART*, ta xauna gurin tana kuka sosai,
Bayan kwana biyu uwani ta soma saka kayanta na lefe tana fita, koda hajiya ta lura tayi mata magana anan take sanar da ita ai tuni ta kyautar da kayanta bata da na sakawa a yanxu sai sabbin.
Sosai abba ransa ya baci koda ya duba har akwai kayan da basu dade da dinkawa ba kuma masu tsada duk ta kyautar,
Tunda uwani taji abba na maganar xai maidata inda malami, hankalinta ya tashi taje da gudu ta cire kayan ta nufi dakin hajiya tana da wasu kaya acan ta saka ta fito tana kuka.
'Abba kayi haquri sharrin shaidan ne da sharrin xuciya, baxan qara ba, dan Allah ka yafe min abba kada ka kaini gurin sa kashe ni xaiyi.
Ganin abba da gaske yake ta soma kururuwa tana kuka iya qarfinta, yana riqo hannunta ya saka ta mota ta xube gurin a sume, bata manta waccan wahalar ba.
Ga bacin rai ga dariya sune suka saka abba a gaba, hajiya ta xuba mata ruwa a jiki.
Bayan wasu awanni suna xaune a dining suna cin abinci uwani ta dube sa tana fadin.
'Abba ina fa sane da cewa baka bani sadaki na ba, nasan ana baiwa mace sadakinta, ko anti jiddah ta bani nawa da el'mustapha ya bada.
Suka yi shiru suna kallonta, ta cigaba da fadin ai maigadi ne ya fada min daxu, ina so nayi jari da kudin na tallafi kaina da ya'yana masu xuwa.
Hajiya tace wane kudin xakiyi jari dashi, duka sadakin naki nawa ne?
Ina da wayo hajiya, baxaa min wayo a cinye min kudi ba, ko anti jiddah ma ta bani kuma na tuna sanda aka bata sadakin ta a hannunta kuka bata abunta.
Amma ai da aka bata maidawa tayi, hankalin ku ba daya ba.
Hajiya a bani nima nayi hankali ai, itama dan tana da kudi ne ta baku ni kuma kowa yasan talakace bani da kudi, abani a buna kada nayi wani laifi ace xaa hadani da Malam.
'Abba ya tashi ya fita bai jima da shiga dakin sa ba ya fito dauke da kudi a hannunsa, ya bawa hajiya yana fadin kirga min kiji nawa ne.
Hajiya ta qirga kudin tana fadin dubu hamsin ne, ya karba ya miqawa uwani yana fadin ga sadakin ki.
Ta karba tana murna harda godia, ta tashi ta dauki kudin dake hannunta duka ta hada ta fita tana fadin ni yanxu bana qaunar mota a rayuwata, ina da wadda el'mustapha ya bani xanje na dauko ta.
Ta jima sosai da fita sai gata ta dawo da wani mutum ya goyo ta akan babur.
Da gudu ta shiga cikin gida ta kira iyayen nata suxo suga ta siye sabon mashin vespa wanda ake yayi 🛵,
Ai abba ni xan riqa hawa abina duk inda xanje akan sa xanje, yanxu haka ana kan koya min tuqin sa, har masallaci idan xakaje ni xan riqa kaika ka huta da xuwa da qafafu tunda baka xuwa da mota.
Gobe da asuba ka tadani barci xan kaika masallaci, hajiya idan xakije maqota ki gayamin duk xan kaiki bana so kiyi ciwon qafafu ki tsufa da wuri, ai na gayamaku ni bana maku baqin ciki da na samu kamar kun samu ne, tayi cikin gida da gudu.
Halin da mahaifan nata suke ciki Allah kadai yasani, washe gari abba baiyi qasa a gwiwa ba ya sake daukarta ya nufi gurin wani malami da ita tsoronsa kada tayi aure tana wannan abin auren nata yaxo ya mutu ba kowane mutum xai iya xama da ita a hakan ba.
Malamin magani ya bata, dana turare dana sha suka dawo gida.
Cikin ikon Allah aka soma mata amfani da su.......
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
67
A gurguje....
Bikin uwani da yusuf sai matsowa yake yayin da iyayen ke iya bakin qoqarin su na ganin ta nutsu, kuma alhamdulillah abin yana ragewa kadan kadan.
Surayya tun tana damuwa tana kuka har ta daina ta xubawa sarautar Allah ido, tana so taga yanda xamanta xai kasance da uwani duk da ba gida daya bane.
Hajiya sai faman gyaran amarya take, uwani na faman washe baki, ashe hajiya na sonta take boye mata, lallai jiddah tayi mata baqin ciki domin bata mata wannan gyaran ba shiyasa akace kishiya abin tsoro da gudu ce, wai uwani ke cewa kishiya abin gudu ce🤔
Duk ranar da hajiya ta manta ba ta bata ta sha ba ita da kanta take tuna mata, hajiya bata mamakin rashin kunya irin na uwani tunda tasan ko wacece ita.
Ba suyi wani dogon biki ba kasancewar kowa yasan uwani baxawara ce🤪, duk bikin da ake jiddah ta halarta kuma sosai ta bada gudumuwar ta, banan ma taje da jiddah ta gayamata,
Ta bawa uwani gudumuwar hadaddiyar cooler mai kyau da tsada, amma uwani ta rena.
An gaya maki abbana bai siyamin inda xan sakawa mijina abinci ne, qila ma kin xubo kayan mallakar miji aciki na xuba abinci na basa ki mallake min shi.
Banan tace subhanallah anty uwani, kin manta ina da aure bayan wannan ma ni ban taba bin boka ko malami ba a rayuwata, ashe har yanxu baki canxa hali ba.
Uwani ta tashi tana fadin, me kike nufi kina nufin ina da wani mugun hali ne, waye ma ya gayyace kixo min biki, banda baqin ciki ki rasa abin bani sai wannan cooler ni kayan mata nake so na gyara kaina kar na xamo bora a gaban miji.
Banan girgixa kanta kawai tayi sauqin ta ba kowa a dakin sai su biyu kawai da ta kunyata a yau, banda anty jiddah me ma xai saka taxo bikin uwani, jiddah ta shigo da sallama tana fadin hayaniya nake ji me ya faru?
Uwani tayi caraf tana fadin, anty jiddah wai banan fa mai aikin mu ta waye har tayi arxikin da xata kawo min gudumuwa dubi fa.
Jiddah tace laifine dan ta kawo maki? Ita da ta tashi yin nata nawa kika bata, ba dan ni ba kina tunanin ma xaki qara ganin banan, meyasa kike haka, meyasa har yanxu kin kasa nutsuwa kisan me kike?
Kina goyon bayanta kenan, ni xan dauka haka ba dan halin ta ba albarkacin kine, ni duk mai min baqin ciki na gano sa Allah bana iya xama dashi.
Jiddah tayi caraf ta kwace cooler tana fadin baki isa ba, ta miqawa banan, koma da ita gida baxaki bata ba, idan kinyi niyar kyautarwa ne kibawa hajiya.
Banan ta karba tana fadin shikenan anty jiddah, uwani ta bita da kallo cikin mamaki da haushi dan tama rasa wane irin baqin ciki ne jiddah take mata haka, amma xasu hadu...
An daura auren yusuf da uwani, kuma a ranar xaa wuce da amarya.
Tun da aka xo daukar amarya ake ta daru taqi ta shiga mota ita lallai sai akan sabon vespa din ta xaa kaita gidan mijin ta.
Wai wace irin mata ce yusuf ya aura haka?cewar daya daga cikin mutanen da suka xo daukar amarya.
Dayar tace magana ne kawai banyi ba, amma tun ranar da muka xo kawo lefen ta na gane bata da kunya da nutsuwa, banda iskanci ina aka taba daukar amarya daga kaduna har abuja akan vespa?
Tsohuwar tace lallai da sake, wallahi da nasan tun farko matar da yusuf yake nema kenan da baxai aure ta ba, yanxu ma bata baci ba xai iya sakin ta.
Aa Inna dan Allah kiyi haquri, inaji yarinyar dama tun farko bata da nutsuwa anty ikram ta gayamana komai akanta shiyasa kika ga bata goyon bayan auren komai ma bata saka hannunta a ciki ba.
Inna tace amma meyasa tun farko baku sanar dani hakan ba, da ba abinda xai saka a daura wannan auren, ita ikram din ai bata taba gayamin ba.
Inna ai anty ikram xatayi maganin ta, tana tsoronta sosai, ki xuba idanu kawai kiyi kallo kada ki sakawa xuciyarki bacin rai.
Inna ta shige mota tana taunar goro cikin jin haushin uwani.
Lamarin uwani kuwa sai da aka kira abba kafin ta shiga mota amma sai da aka saka mata vespa a bayan motar tukunna, cewar baxataje ta barshi ba.
Jiddah bata tsaya daukar amarya ba tana can tare da masu gyaran gidan na uwani suna jiran isowar su.
Kuyanga Qaumi ce ta shigo dauke da airah tana kuka sosai,
'Anty jiddah, airah ta tashi daga barci sai kuka take taqi ta karbi abincinta.
Jiddah ta karbe ta tana fadin, kada kije nesa yanxu xan kira ki karbeta da tasha, saboda sun kusa isowa, ina sauran abokan xaman naki,
Ranki ya dade muna tare da su a waje,
'Yauwa, kije xan neme ki, ta fita,
Banan tace wai anty jiddah ni bansan wadannan kuyangun ba hala an canxa maki su ne.
Eh tuni sarki ya canxa min wadancan basa son aiki, shine ya bani Maryam, Hajja, Saina da Mom sadeeq.
Banan tace cab kice duk yan kayan baqin ciki ne aka hada ki dasu.
Jiddah murmushi kawai tayi.
Bayan wani lokaci sai ga motocin amarya sun iso, ana fitowa da uwani a mota ta cire mayafi tana kallon gidan da aka kawo ta, ba wanda ya lura da halin da take ciki sai da suka ji tana fadin,
Shiyasa nake son yusuf kwata kwata a rayuwarsa bashi da baqin ciki, duk wannan gidan nawa ne.
Wasu suka dauki salallami, wasu kuwa suka tabe baki tunawa da suka je da ita yanxu ta gaida iyayen yusuf sai da tayi makamancin irin wannan.
Sai aka rasa waye amarya aciki tun da suka shigo, jiddah tamkar ta nutse gurin saboda kunya, ta jawo uwani ta gyarta hade da kai mata rankwashi mai xafi a tsakiyar kai tana fadin uban waye ya gaya maki amarya na fito da fuskarta.
To baxan kalli gidan bane, gidana ko naki, banda baqin ciki miye n.... Jiddah ta qara bige mata baki.
'Na qara jin muryarki anan wlhy abba xan kira na gayamasa kinsan yanda kukayi kafin axo dake,
Akaje da amarya bakin gado aka xaunar da ita, wasu suka fita suna fadin bari muje muga gidannan kamar ba wanda muka sani ba an gyara sosai gashi an qayata gidan da kaya masu tsada, iyayen ta sunyi matuqar qoqari gsky.
Uwani najin haka ta miqe kar abarta baya gwanda taje ganin gidan ta tsare abinta kada wata tayi mata sata ta wuce da kayan kitchen din ta taji yanxu haka ake yi.
Jiddah ta maida ta da qarfin gaske ta xauna,
Wai baki da hankali uwani, ina xakije, kawaicin ma baxakiyi ba har su tafi.
'Anty jiddah xanje na tsare kitchen dina ne kada amin sata, abba ya siya min kaya masu tsada, baki ga gas dina yafi wanda kika siyawa banan ba idan aka dauke fa.
Cikin takaici jiddah tace to sai me dan an dauke, wallahi kika bata min rai dukan ki xanyi a gidannan.
Uwani tayi shiru tana tunxuro baki, sai ga hawaye suna bin kuncinta, jiddah tayi mata banxa, yau gata ita ke tsaron uwani ita bata taba ganin ana tsaron amarya ba, ta dubi uwani tana fadin,
Wai ke baki da qawaye ne, duk ina suke ko daya ban gani ba.
Cikin takaici tace bani dasu menene.
Jiddah tace au hakane fa, sam na manta da uwani nake magana wadda ke rayuwarta ita kadai.
Uwani ta tabe baki tana fadin ban gayyaci kowa ba duk yan baqin ciki ne, ashe na manta har ta kusa dani ma tana min baqin ciki saboda an kawo ni gidan mijina, kada ayi min snatching ace xaa auri mijina dan na auri mijin wata.
Jiddah ta tabe baki tana fadin, ai rijiya ba gurin wasan yaro bane, mijin wata da kika ga kin aura ai yafi qarfin ki shiyasa har kika kasa xaman aure dashi, wanda kika aura a yanxu ma ai sai da aka bisa da roqo da rarrashi akan has rufa asiri banda haka ai da kin tsinci hoton ki a gidan masallaci ana cigiyar mai so a kyauta.
Takaici ya hana uwani magana ta tashi ta leqa ta window dakin tana kallon harabar gidan kafin tace,
'Yauwa har yanxu vespa dina yana nan kafin yan baqin ciki suyi gaba dashi, na lura yana tsonewa mutane ido sosai...
Gidan yayi tsit yan kawo amarya duk sun watse ya rage jiddah kawai a gidan, ta xauna sosai tayi wa uwani nasiha game da aure, ta qara nuna mata wannan auren daban yake da irin wanda tayi a baya.
Cikin ikon Allah kuwa uwani ta saurareta cikin nutsuwa har take ganin jiddah mai son ta ce bata mata baqin ciki a rayuwarta.
Ganin dare nayi sosai ga el'mustapha sai faman kiranta yake ya