Showing 51001 words to 54000 words out of 138779 words

Chapter 18 - El-mustapha Complete Hausa Novels By Fertymerh Xarah.docx

09 Oct 2025

2009

bana son ko sunan ta naji an ambata a tare dani, ta cutar da rayuwata baxan taba yafe mata ba, ta soma kuka.

Inna ige tace ni Allah xai saka maki jiddah tabbas wannan matar baxata gama duniya lafiya ba.

Ina so na taimakeki jiddah amma ina jin tsoro,

Jiddah ta dube ta, kada kiji tsoron komai na gayamaki mijina dan sanda ne, idan suka maidaki gida yau ki qoqarta kije ki sanardashi, xan baki lambar wayar da xaki kirasa ko kuma na baki address din office din sa.

Inna ta ciro wayar ta cikin xaninta jikinta na rawa ta miqawa jiddah tana fadin,

Ko ki gwada kiransa yanxu kiji, jiddah na qoqarin amsar wayar taji wani sauti daya hargitsa tunanin ta sai ga Inna xube a qasa cikin jini,

Jiddah ta rude taja baya tana kallon qofar, kurma ne tsaye fuskarsa tamau ba alamar imani a tare dashi, ba tare da tunanin komai ba ya dauke fuskar jiddah Mari, tayi dif saboda Marin ya shige ta sosai, ta dauki lokaci kafin jinta ya dawo gare ta sai ga jini na fita ta hanci da bakinta.

Goga.. Goga.. Kurma ke kiransa cikin kakkausar murya kamar wani basaraken xaki, goga na shigowa ya nuna masa Inna ige,

Dauke min wannan shegiyar ka fice min da ita a gidannan, ajiye ta a qofar gidan idan mun tashi shiga gari muje da ita mu yar da.

Goga ya juya ya kira yan uwansa dan baxai iya ba shi kadai, yana mamakin me tayi aka harbeta.

Ke dan ubanki ni xaki ci amana, kinma samu ina tausayamiki bana baki wahala har kike son tona min asiri, to daga ba wannan xan nuna maki ko waye kurma, babu sauran tausayi tsakanina dake, kuma kome kike so ke xakiyi da kanki ba wanda xan koma daukowa.

Rarrafo ki fito nan, tun bansa kan bindigar nan na fashe maki tsakiyar kai ba,

Da sauri jiddah ta soma rarrafowa tana kuka, a falon ya nuna mata inda xata xauna tana kallo aka fita da gawar Inna, a wane qauye Inna take su waye yan uwanta duk bata sani ba, ashe haka suke da yawa bata taba sani ba harda mata a cikinsu kowace tana xuqar sigari,  maxan kuwa sai giya suke sha, ta juya tana kallon inda kurma yake xaune suna hada ido sai da cikinta ya hautsina, mararta ta qule saboda wani fitsari da yaxo mata.

Ina jin fitsari, shine abinda ta fada tana kallonsa cikin rawar jiki,

Ya xuqi sigari ya furxar da iskan yana kallonta,

Kiyi sa a nan ki xauna a cikinsa, xan axabtar dake ne na daina tausayinki,

Tayi tunanin idan tayi fitsarin Dame xatayi sallah, dama a xaune take yin abinta, yanda take ji baxata iya riqe fitsarin ba, ta riqe cikin tana sharar kwallah, sai ga fitsari na fitowa qasanta ya soma gangarawa,

Kurma ya bita da kallo bayan ya ajiye sigarin, ta tsorata a tunaninta ko wani abin xai mata ne,

Tace kashi nake ji...

Shima kiyi sa anan dan ubanki, kurma ya fada bayan ya tashi yana gyara bindigarsa,

Goga... Goga...

Kawo min ruwa da tsumma ta gyara gurinnan da ta bata kafin na hasala na dauke dayan qafar da bullet.

*

Kwana biyu uwani ba kudi kuma tana so ta fita ko mai babu a motar ta, duk ta kode ta dawo wata iri, ko gayun yanxu an daina, ba ruwanta da kowa a gidan.

Tana xaune taji dawowar su aryan daga skul, ta fita daga dakin sukayi karo da aryan a falo,

Sai da ya tsorata da ganin ta, ya juya da gudu ya bar falon tsoronta suke sosai, tan fitowa taga driver yan so fito da arham motar yaqi sai kuka yake,

Rufe motar ka kyaleshi kada ya fito ina ruwan wani, uwani ta fada bayan ga rufe arham a motar, ta karbi key din motar ta juya cikin gida ta shirya ta fita kafin el'mustapha ya dawo, dama tun bayin mutuwar mamansa take samu tana fita.

Arham yayi kuka sosai har barci ya dauke sa a motar, ya kwanta yana maida numfashi, uwani na fitowa Sam ta manta da wani arham a motar ta shiga ta ja abinta ta fice daga gidan, ta jima da fita sai ga el'mustapha ya dawo, bashi da wani buri a yau kamar ya gansa a gaban uwani, sun riga sunyi tracing layin har record na yanda tayi da jiddah ta fito gidan duk yana da.

Yana fitowa sai ga banan dauke da aryan sai dube dube take alamar tana neman inda arham ya shiga.

Sun dawo skul amma banga arham ba cewar banan tana kallon el'mustapha,

El'mustapha yace arham ai baxai bata a gidannan ba indai driver ya dawo dashi, where did you left him aryan.

In the car... ya fada yana kallon el'mustapha,

Suka juya suna kallon motocin gida,

Yace sauke shi banan xo ka nuna min wace mota ce,

Ya qanqame banan alamar baxai sauka ba, ya dube sa yana fadin daddy our school car, ai anty uwani ce tace a barshi a ciki tunda baxai fito ba shine taje ta rufe shi acikin motar.

El'mustapha ya duba ba motar, hankalinsa ya tashi yana tambayar driver dake kai su skul, yayi masa bayanin komai, ya dawo yana kallon banan koma ciki da aryan cool your mind komai yaxo qarshe.

Wayar sa ya ciro, office din su ya kira yana buqatar yan sanda nan da minti goma, ya dubi DSP Bello Marona😜,

Kiramin ibrahim na kasa samun sa, ya laluba aljihunsa yaji bindigar sa na nan, ya juya da sauri ya shiga cikin gida, bai jima ba ya fito cikin uniform din sa, fuskar nan tasa ba walwala ko kadan.

Amma ta ina xasu soma neman uwani, ina ta nufa duk basu sani ba sai sun jira dawowar ta.

Jiddah kuwa da kyar ta gyara gurin, sai taji cikin ya koma mata gefe daya, tayi amfani da ruwan da aka kawo ta xuba a jikinta tunda ba wani xane da xata sauya, duk abinda take idanun kurma na kanta har lokacin da uwani ta shigo gidan.

Tana yin parking arham na tashi daga barci, ta fita daga motar cikin sauri ko rufewa bata yi ba, ya tashi yana kalle kallen sabon gurin da ya gani a yau, yana ganin inda uwani ta shiga ya fito yabi bayanta batare da tsoro ko fargaba a tare da shi ba.

Uwani na shigowa suka ci karo da kurma,

A kashe min jiddah ka gayamin ko nawa ne xan biya daga yau xuwa gobe,

Jiddah ta dago tana kallonta cikin tsananin tsoro da mamaki,

Kurma ya xuqi sigari yana murmushi da alama xancen ya masa dadi tunda xai yi kissa,

Mummy........ Shine sautin da suka ji ya fito dai dai qofar shigowa falon, gabaki dayan su suka juya suna kallonsa,

Bugun xuciyar jiddah ya tsananta da ganin arham, tsoro ya bayyana a fuskarta lokacin da taji uwani na fadin,

'Na manta yaro nan yana cikin mota naxo dashi, tabbas idan na koma dashi asirina xai Toni xai iya gayawa el'mustapha, shima ka kashe shi....

Jiddah ta xaro idanu tana kallon lokacin da arham ya nufo ta da gudu yana kiran,

I miss you mummy...... Jiddah ta daqa hannu tana tsaidashi cikin daga murya ganin kurma ya saita shi da bindiga,

Noooooooo Ar..... tayi shiru sakamakon kukan bindiga da taji, ta bude idanuwanta dai dai lokacin da arham ya fadi ragwaf a jikin uwani dake kusa dashi,

Kurma ya maida bindigarsa ya ajiye yana fadin shima yana cikin Bill xaki biya kudin aikin sa,

Uwani ta dauki arham taje har gaban jiddah ta ajiye mata shi, jini ya taba gyalenta batare da ta sani ba, murmushi tayi tana kallon jiddah kana ta juya ga kurma.

Xan yi ma waya, kana kashe ta xan gayama inda xamu hadu na baka kudin bana son na cigaba da xuwa nan saboda xargi.

Ina sauraren ki cewar kurma, uwani ta juya tabar gidan.

Jiddah ta maida kallonta ga arham dake kwance a gabanta, ta rungumoshi tana kallon inda aka har besa a hannu ne,

Kurma ya dube ta yana fadin kuskure aka samu kika ga na harbesa a hannu, xuciyarsa na so harbawa aka sami akasi, amma ba komai tunda ya mutu ai shikenan, ya tashi ya bar falon yana wata tafiyar qasaita.

Kuka yaqi yaxo mata a wannan lokacin, sai jiri take gani, tana son tayi kukan ko xata sami sauqin xuciyarta amma ta kasa, kuka Ma rahamane, ta qara rungumeshi a jikinta bayan ta sumbaci goshinsa, addua take Allah yasa kar ya mutu, ina ma xata sami wanda xai taimaka yaje mata dashi asibiti, tana jin ihunsu a gida,

Ta soma jijjiga arham, bata yarda ya mutu ba, arham ka tashi, mummy is with you, dan Allah karka mutu ka barni, sai ta gigice tana neman xaucewa,

Help me, please help me and save his life, ta soma waige waige kamar me neman wani a gurin.

Uwani na isowa ta ci karo da motocin yan sanda a gidan, gasu tsatsaye birjik kamar masu biki.

Tayi parking ta fito tana Jan tsaki a xuciyarta, kicibis suka yi karo da juna,

Ina kika kai min arham shine abinda ya fada idanunsa akan fuskarta,

Tashin hankali ya bayyana qarara a fuskarta, ta soma musa bata ganshi ba, batare da tunanin komai ba ya dauke ta da Mari har biyu masu kyau.

Ina kika kai jiddah da arham nake tambayarki,

Ta dafe kuncin tana kuka lokacin el'mustapha ya lura da jinin dake gyalenta,

Jinin menene wannan uwani, ta xare idanu tana kallon wurin,

Ya shaqo wuyanta a gurin,

Kada kice kin kashe min yaro uwani, ina kika kai arham da jiddah, answer me please,

Ta soma kakarin mutuwa, ba qaramin shaqa yayi mata a wuya ba, duk wurin ba wanda yayi qoqarin karbanta hannunsa saboda duk yaran sa ne sai ibrahim kadai shima da kyar ya kwace ta hannunsa,

Ka barni na kashe ta ibrahim kafin naji mutuwar arham a bakinta, dama na gayama nine mutum na farko da xai fara kamata dumu dumu, ya xaro bindigarsa ya sai ta a goshinta.

Ibrahim yasha gabansa da sauri yana fadin,

Me kake yi el'mustapha, control your temper, idan ka kashe ta ina xamu sami inda arham da jiddah suke, baka tunanin abokan aikin nata suka ji mutuwarta su gudu dasu ko su kashe su.

Xamuje ta kaimu inda suke yanxu, kowa ya shiga mota cewar ibrahim yana kallon sauran yan sanda.

Pherty ta gaishe ku,

_Afuwan pls xaku ji ni shiru na kwana biyu, due to some problems, nagode da qaunarku ga littafin El'mustapha._

Pherty luvs you ol😀

EL'MUSTAPHA

Haske Writers Association

Home of experts and perfect writers

Fertymerh Xarah💞

38

Ba abinda ke tashi a gidan sai sautin kida da raye raye, abokansu daga wani gu sai xuwa suke, kowane da makamin sa hannu, suna tafe suna shan giya wasu na xuqar sigari.

Ko taron me suke yi yau? Kurma yaci gayu cikin wasu qananan kaya, wando three quarter na black jeans, rigar farar mai qaramin hannu, sai qafafunsa dake sanye da sneakers👟, baqin glass ne sanye a idanuwansa, sai wata shegiyar hula da ya dora akan sa, ya gogu fa sai Ma kun ganshi😀

Yana riqe da qugun wata budurwa tashi, bra ce kawai sanye a jikinta sai wani guntun buje ko pant babu a cikinta, tunda yasa hannu qasan bujen nata hankalinsa ya nemi gushewa,

Ta qara banqaro kirjinta tana xuqar sigari, hannunta daya na kan hannun kurma dake cikin bujen nata,

Baxan jure kallon wannan shashanci ba gwanda naje nayi kallon masu d'an kamfai🤧.

Har lokacin jiddah na rungume da arham, kanta yayi nauyi sosai, ga jiri da take gani idanunta sunyi jawur saboda kuka kuma har lokacin bakinta bai mutu ba wajen kiran wanda xai taimake ta.

Tana jin hayaniyar su, tana jin yanda suke shewa,

Help... Somebody help shine abinda goga yaji jiddah na furtawa lokacin da ya shigo da tashi budurwar.

Bai san wainar da ake toyawa ba ya qarasa yana fadin,

Ina kika sami yaro, ta bude idanu da kyar tana kallonsa, tana ganin goga ne jikinta ya dauki rawa saboda yana matuqar tausaya mata da taimakonta.

Yaro nane ya kashe min shi, ka taimaka ka kaimin shi asibiti, dan Allah ka taimakeni kada ya mutu.

Ya taba arham yana kallon inda kurma ya harbesa,

Shi wannan yaron menene laifinsa, meyasa kurma yake marar imani ne,

Numfashinta ya soma sama sama,

Tace ka taimakeni, ka kaimin shi asibiti kada ya mutu, dan Allah ka taimakeni.

Ina je dashi asibiti xaa iya kamani ai is very risk idan baki sani ba, bari naje na kira maki likitan dake duba mu a duk lokacin da aka harbi wani a cikin mu, ki kwantar da hankalin ki yanxu xan dawo.

Bai jira cewar ta ba ya tashi ya fice da gudu ko budurwarsa bai waiwaya ba cikin tausayin jiddah.

Jiddah ta qara rungume arham banda sumbatar sa ba abinda take sai kuka.

*

Suna qoqarin saka uwani motar sai ga su hajiya da abba, sunxo yiwa el'mustapha gaisuwar mama, sunyi masa a waya basu sami damar xuwa ba sai yanxu.

Hajiya ma jiki yayi nauyi, ciwon qafafu take fama dashi.

'Abba yace lafia el'mustapha na ganku haka.

El'mustapha bai yi magana ba, akwai kunya sosai tsakanin sa da surukin sa, ibrahim ne yayi masu bayanin komai.

Inna lillahi wa Inna ilaihir raji'un, iyayen suka juya suna kallon uwani tana tsaye abinta ba alamar nadama ko wani dana sani a tare da ita, ta dauke kanta gefe daga kallonsu tana tunxuro baki.

Hajiya kam har da kuka,

Tace duk yanda nayi dake uwani akan idan kina da sa hannu a batan jiddah kika musa, kika bar baiwar Allah da ciki cikin uquba, anya uwani xaki ga annabi kuwa, kwata kwata babu imani a xuciyarki, baxan taba yafe maki ba kije gaki ga duniya.

Allah baxai kamani da laifin komai ba tunda bake nayi mawa ba cewar uwani, a xuciyarta take maganar, sai anyi magana ki fara matsar hawaye kina kuka salon ace ni ke sakaki kuka saboda tsabar munafurci, ta gyara tsayuwarta hade da rungume hannayenta a qirjinta,

'Abba baiyi wata wata ba ya hau ta da duka, duk gurin ba wanda yayi qoqarin hanasa kuma duk dukan da yake mata bai raunana xuciyar uwani ba, bako digon hawaye a tare da ita haka take da taurin xuciya kamar namiji.

Shi da kansa ya barta shima dan ya gaji ne,

Tunda kika iya auren mijin jiddah na yafe ki a xuciyata uwani, na cire ki a raina bani da wata 'ya a duniyar nan sai jiddah kadai, yau kin cutar min da 'ya, kin cutar da baiwar Allah salihar mace mai haquri da kawaici akan duk abinda kike mata, kije gaki ga duniya alhakinta kadai baxai barki ba ballantana na iyayenki.

Duk jikinta yayi tsami saboda duka, gefen fuskarta Ma ya kumbura, ta gyara kallabinta ta shiga mota cikin jin haushin tsayuwa da su, ga wani takaicinsu daya cika xuciyarta, duk gurin kallon mamaki ake mata

'Abba yace el'mustapha kayiwa uwani duk hukuncin daya dace da ita a matsayin ka na dan sanda, kada ka tausaya mata ko nauyin dan tana tamu, Sam ba tamu bace kuma bamu Santa ba.

El'mustapha dai baice komai ba har lokacin bashi da wani buri a yanxu kamar ya ganshi tare da jiddah da arham,

Yace abba ku shiga gida tare da hajiya kafin mu dawo.

Ni xan biku naga wane hali jiddah take ciki.

El'mustapha ya riqo hannunsa cikin jin nauyinsa,

Yace baxaka bimu ba saboda bamu san yanda abin xai kasance ba, ko mu kashe ko a kashe mu yan ta'adda ne masu xaman kansu, idan suka mana gardama xamu harbesu ne suma xasu harbemu dan baxasu barmu ba, kayi haquri ka xauna tare da mana addu'ar nasara.

Allah ya kare ku kuma ya baku sa'a akan su, abba ya fada yana kallon el'mustapha uwa ya sa ihu dan baqin ciki da abinda uwani tayi.

Kowa ya shiga mota, suka dauki hanya, maimakon uwani ta basu direction na kwarai sai ta soma basu wrong direction.

Wasa wasa sun kusa xagaye Abuja sai faman tafiya suke a duk inda ta nuna masu, hankalinta kwance ba damuwa tare da ita xatace kubi wannan titin, sai wannan layin.

El'mustapha ne ya fara gano kamar tana yi masu wasa da hankali, ya daka mata tsawa yana tambayarta, ta tunxuro baki tana fadin,

Ni na manta hanyar ne, na manta inda ake shiga aje gurin.

Uwani hukuma cewar ibrahim yana kallonta cikin takaici.

A yanda el'mustapha keji kamar ya kashe shegiya a gurin, duk wani fushinsa da Jan idonsa baxai saka uwani taji tsoron sa ta gayamasu gaskiya gashi kusan awa daya suna yawo a titi, dole sai yabi da dabara da rarrashi, ya dube ta cikin kalar tausayi.

Uwani a hakan kike so na maida aure na dake?

Taji gabanta ya fadi, ta juya tana kallonsa, suna hada ido taji wani sabon sonsa da qaunar sa sun taru a xuciyarta, duk da ya rame wannan kwarjinin nasa yana nan, jikinta yayi sanyi taji kamar ta fada jikinsa saboda tsabar so,

El'mustapha na ganin tana masa wannan kallon ya cigaba da rarrashinta harda riqon hannunta wanda ya saka uwani yin hawaye saboda farin ciki.

Nan take tace su koma titin da xai fitar dasu Abuja, anan ta fara basu direction na gaskiya tanayi tana kallon el'mustapha, bata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login