Showing 75001 words to 78000 words out of 138779 words
Chapter 26 - El-mustapha Complete Hausa Novels By Fertymerh Xarah.docx
ta da idanu batare da yayi magana ba amma xuciyarsa bugawa take.
Afuwan pls dan Allah kuyi haquri da wannan, kwanakinnan bani da lokaci olways busy🙏🏻
Shiru yayi bai qara magana ba, ya tashi xai bar dakin,
Tace ina kuma xaka je yanxu, nayi tunanin xaka kwanta ne,
Ki jira ni yanxu xan dawo, akwai wani magani da likitan ya rubuto ki fara amfani dashi kafin muje, bana so kiyi skipping ko wace rana na kwana bakwai ne.
Ta gyada kai tana kallonsa, a dawo lfy ka kula da kyau kasan dare ne fa.
Yace dan sanda na tsoron dare ne jiddah? Yanxu xan dawo da yardar Allah, ya juya ya fice.
Tabi bayanshi da kallo kafin ta sauke numfashi a hankali tana kallon tsinin cikinta.
Ko menene aciki Allah ya raya shi, Allah ka bata ladan wahalar da tayi da cikin ya kuma albarkaci abinda ke ciki.
Tana xaune taji sallamar banan ta shigo dama taga fitar el'mustapha,
'Anty jiddah munyi waya da kaka tace xata xo duba ki gobe, tayi fama da rashin lfy ne shiyasa bata sami xuwa ba.
Murmushi kawai jiddah tayi,
Allah ya kawo ta lfy,
Banan tace amin tana qoqarin tashi,
'Yauwa hado min tea ki kawo min, nasha golden morn bai ishe ni, yunwa kuma nake ji.
Ko na kawo maki abinci mai nauyi ne?
Aa bani ruwan tea din dai, idan da sauran cake din da anty ikram taxo dashi daxu kawo min.
Banan ta juya ta fice, jiddah ta bita da kallo har yanxu ta rasa gane dalilin da ya sa el'mustapha keda feelings akan yarinyar duk da yana boye mata.
Ba abinda banan xata nuna mata, komai tafi banan illa lafiyar qafafu yanxu, ko saboda qafafun ne el'mustapha ke neman ta, ta saki uban tagumi bayan ta fada cikin tunani mai xurfi.
Har el'mustapha ya shigo dakin bata sani ba, xama yayi yana tabata,
Jiddah..... Ya kirata da qarfi,
Tayi firgigit tana kallonsa,
Yaushe kadawo? Ya bata fuska yana kallonta bayan ya ajiye ledar dake hannunsa,
Meke damunki haka, wane irin tunani ne tun daxu ina magana baki ji ba,
Wlhy ban sani ba,
'Wannan tunanin da kike if d condition becomes worse baxan taba yafe maki ba, kece kika ja komai ina qoqarina na ganin na kaucewa duk abinda xai saka ki damuwa kamar yanda likita ya fada.
Ba abinda xai faru El'mustapha, baxan taba Ma abinda xaka qi yafe min ba, kayi haquri please.
Suna haka banan tayi sallama amma bata shigo ba sai da jiddah ta bata umarnin haka.
Ta gaida el'mustapha ciki ciki ya amsa mata, kwanakinnan bata san meyasa ya canxa mata ba duk da aikin da yake saka ta duk ya daina gaisuwar ta Ma da kyar yake amsawa, kuma ta damu sosai, tana ji kamar xata tambayesa ko tayi masa laifine, ba fuskar yin hakan.
Ta sunkuya a hankali ta ajiye cup din tea din a gaban jiddah, tare da bowl din da ta xubo cake din.
'Anty jiddah xanje na kwanta bakya buqatar komai ne,
Babu Allah ya tashe mu lfy,
Tace amin, ta juya a sanyaye ta fice bata san meyasa ta damu da el'mustapha ba, bata san meyasa ta kasa cire sa a xuciyarta ba duk da tana da Islam.
Kallon abinda banan ta ajiye a gabanta yake kafin ya dube ta,
Ba dai wani abin xaki qara ci ba jiddah,
'Naji ban qoshi ba ina jin wata yunwar,
Ya xaro ido yana kallonta,
Ke jiddah da daren nan fa kika ci tuwo, kika ci farfesu, kika ci pizza tare da twins, sannan kika sha golden morn duk bai ishe ki ba sai kin dora da tea harda cake Ma.
Ta dauki cup din tana juya spoon tace ban qoshi ba el'mustapha har yanxu ina jin yunwa,
Yace are you ok?
Ta gyada kai kafin ta kai tea cup din a bakinta,
Tace har xance ka biyo min da ice cream ma saboda ba waya hannuna ne.
Ya tashi yana fadin wannan xaqi da sanyi da kike sha yayi yawa, koma kin kira baxan biyo dashi ba.
Tayi murmushi bayan ta gutsira cake din tana fadin kanaso na haifi baby da rowa, daddy ya hana mata shan ice cream,
Whatever dai ya fada yana xare doguwar rigar dake jikinsa,
Ya kwanta yana fadin ke nake jira ki gama wannan ciye ciyen ga drugs din ki.
Ta gyada kai tana kallonsa, ya lumshe idanuwansa kafin ya juyo yana kallonta,
Sorry na manta abba ya kira kafin mu tafi xasu xo shi da hajiya,
Tace to mama fa, yaushe xata xo, ko ka kaini na ganta muyi bankwana.
Kuyi bankwana sai kace mai barin duniyar?
Tace dama xan tabbata a cikin tane idan ban barta ba, Allah kadai yasan gawar fari, sai kuma tayi murmushi ganin ya xuba mata idanuwa yana kallonta,
Su aryan suna son banan kuma ta dace da rayuwar su el'mustapha, hankalina yafi kwantawa da ita akan duk wacce xaka kawo Bay....... Ya katse ta,
Is ok pls, kada ki batamin rai da daren nan, ya juya mata baya.
*
Ana gobe xasu bar garin, sai fama shirye shirye suke,
A tafiyar harda hajiya, anty yusrah da banan duk el'mustapha ya dauki nauyin xuwansu.
Twins xaa barsu tare da anti ikram saboda skul.
Yan uwan jiddah Ma wannan karon sunxo sun mata addua sosai tare da bata kudi kacokan ta miqawa el'mustapha su ya saka mata a account din su twins.
Banan na xaune tana shafawa jiddah magani a qafa, kallon ta tayi kafin tace...
Banan ina ji ai kin shekara da gama School yanxu ko.
Anyi shekara anti jiddah watanni kadan ne babu a ciki,
Jiddah tace nayi nayi dake ki nemi admission ki fara xuwa skul kinqi, kina da damar yin karatun amma kina wasa, ko kina nufin haka xaki tamin bauta kiqi karatu har kixo kiyi auren a haka?
'Anty jiddah karatu a wannan lokacin yanxu da kike a... Jiddah ta katse ta,
Idan ta nice wallahi bana cikin matsala, I can take good care of my self sannan ga el'mustapha Ma kina ganin komai shi yake min, idan baya nan kece, ke kuma yanxu idan bakya nan xan maida Inna ta dawo aiki nan ne ta barma su saratu na cikin gida, ba abin damuwa bane, tuntuni nake maki mgn akan karatu.
'Anty jiddah ko naje makaranta baxan iya karatu ba Allah ya gani xan ta tunanin halin da kike ciki ne, kibari idan kin haihu lafia kin sami sauqin qafafunki xan koma makaranta.
Jiddah tayi shiru tana kallon yanda banan din ta hade fuskarta, murmushi tayi tana fadin,
Aure xakiyi banan, Allah kadai yasan mijin ki tsakanin Islam da El'mustapha, bana son saboda amfanin kaina ki tauye naki haqqin, ki tashi ki gina taki rayuwar ki kama abinda xai taimakeki ranar da babu ni.....
Jikin banan ya dauki rawa, maganin dake hannunta ya subulce ya fadi daga hannunta, abu biyu a kalaman jiddah da nayi matuqar tsorata ta,
_' Allah kadai yasan mijinki tsakanin Islam da El'mustapha, ki kama abinda xai taimake ki ranar da babu ni_.
Me kike nufi anti jiddah meyasa kike wadannan kalamai masu tsauri da basu da dadin sauraro.
Jiddah tace dole ne na sama maki future mai kyau ki dandana xaqin ilimi da rayuwar aure mai kyau kafin Allah yayi hukuncinsa a kaina.
Hawaye suka cika idon banan, jikinta yayi sanyi matuqa,
'Dan Allah anti jiddah kiyi shiru ki daina gayamin irin wadannan kalaman, xuciyata da kwakwalwata baxasu jure ba, dan Allah ki daina.
Mutuwa tana kan kowa banan, ni ba nace maki xan mutu bane ina nuna maki halin rayuwa ne....
Tayi shiru sakamakon jin banan din ta fashe da kuka mai tsanani, ta xuba mata idanuwa tana kallonta cikin mamaki,
Kuka kike yi banan?
Idan kinyi kuka yau, el'mustapha yayi kuka, twins sun yi kuka waye xai rarrashi wani, keda nake so na bawa amanata da ta ya'ya na, ki basu tarbiya irin taki.
El'mustapha yana sona sosai, irin son da baxan iya misalta maki shi ba, ki riqe min el'mustapha banan bana son rashina ya tagayyara shi, bana son abinda xai dagula masa lissafi, ina son shi yadda yake sona, naso na cigaba da rayuwa d...... Banan tayi saurin toshe mata baki tana kuka tana girgixa kanta.
Bafa ciwo ne mutuwa ba, sai ni na mutu yanxu ko anjima koma gobe na barki, meyasa kike min haka ne anti jiddah.
Dariya sosai jiddah tayi tana fadin,
Wasa nake maki banan ina so naga qarfin imanin kine, ki tayani da addua, tare xamu dawo nayi rayuwa cikin ya'yana naga auren banan da Islam, na raini abinda ke cikina na ganni akan qafafuna ina rayuwa tare da el'mustapha cikin farin ciki, dan haka maxa ki share hawayen wasa nake maki.
Banan ta soma share hawayen amma har lokacin jikinta ba kuzari, ta dubi jiddah da ta maida kallonta kacokan akan TV cikin kwanciyar hankali babu wata damuwa a tare da ita, samun mace kamar jiddah a xamanin nan sai an tona, ina alfahari dake anti jiddah Allah ya baki lfy ki dawo cikin ya'yan ki, na sami rayuwa mai inganci tare da ke.
Sanda el'mustapha ya dawo daga kaisu twins inda anti ikram kallonsa jiddah tayi tana murmushi,
Har nayi missing din su kamar kaje ka dawo min dasu.
Ya nufi toilet yana fadin, me xai hana idan kina so a dawo da su yanxun nan kuwa,
Murmushi kawai tayi ya shiga toilet din bai jima ba ya fito yana kallonta,
'Anty ikram ta bada saqo a baki amma na manta dashi a mota idan na fita xan dauko maki,
Tace menene ta bada a kawo min?
Nima dai ban sani ba, abu ne acikin Leda, ya dan dube ta anty yusrah ta aiko kayan nata kuwa.
Tun daxu, suna falon ka,
Ya xauna daf da ita yana fadin, na kusa angwancewa jiddah, ki haihu na huta haka, nayi ta haquri, ko babu lafiyar qafafun I can manage amma Allah yasan abinda ke xuciya ta I need you.
Taja kunnensa tana murmushi, ban san yaushe el'mustapha ya dawo haka ba, idan munje sati nawa xamuyi ne?
Ana maganar watanni kina maganar sati, Allah ya bamu nasara a wannan aikin naki jiddah.
Amin ta bashi amsa, tace ka dauke ni pic da wayarka el'mustapha, xan riqa tuna wannan wheel chair din a duk lokacin dana kalla, baxan taba mantawa da ita ba.
Ya dauki wayar yana ta daukar ta, wani suyi tare wani tayi ita kadai.

*
'Washe gari jirginsu ya daga xuwa Germany,
Satin su biyu acan, an dora ta akan drugs kafin a tashi mata tiyata, sosai dr merah ke kula da ita, tun kallon farko da yayi wa qafar ya gano matsalarta.
Amma bai masu bayanin komai ba kuma ko el'mustapha ya tambayesa akwai wata matsala sai dai ya daga masa hannu, abinda ke damun el'mustapha kenan da dr merah shi kam ya rasa gane qarfin mulkin wannan mutumin ya fiye ji da sarauta kamar a gidansu aka farata.
An saka date din da xaa Ma jiddah aiki, tun da el'mustapha ya kira Nigeria ya sanar da yan uwa banda addua ba abinda suke.
Wani abin mamaki, haihuwar taxo dai dai da ranar da xaa yi mata aikin, tun wayewar garin ta tashi da naquda gadan gadan.
Tun tana cijewa kada el'mustapha ya gano sai da ya gane,
Da kansa yaje ya kira dr merah, halin da suka same ta kuwa gwani ban tausayi.
Batayi wata doguwar naquda ba ta haifo santaleliyar d'iyar ta, jawur da ita kamar jiddah, sai dai gabaki daya yarinyar kamannin twins ta dauko illah dai tafisu hasken fata ne.
Suna tsaye tare da jaririyar suna kallo aka fito da jiddah xaa shiga aikin da ita,
El'mustapha ya miqawa banan jaririyar da sauri ya nufi jiddah, haka Ma banan tabi bayansu da sauri tare da hajiya,
Me na haifa el'mustapha?
Mace ce jiddah kyakkyawa kamar twins, ya fada yana murmushin qarfin hali yana shafa kanta.
Ta juya tana kallon hajiya da kyar ta iya cewa nagode hajiya...
Sai kuma ta dubi banan dake dauke da jaririyar.
Nasan xan fito lafiya insha Allah na same ku, amma duk da haka ki kulamin da ita banan, ki kula da su twins ciki kuwa harda *EL'MUSTAPHA*, cikin kuka banan tace,
Anti jiddah El'mustapha yayi babba da na kula dashi, ke kadai xaki iya kula da shi, ke kadai xaki iya bashi farin ciki irin wanda kike so ya dauwama aciki, dan Allah kidaina wannan maganar xaki tashi lfy.
El'mustapha ya sunkuwa ya sumbace ta jikinsa na rawa, yasa hannu yana share mata hawaye,
Xafin ciwo ba mutuwa bane jiddah, jikina har ynxu bai bani xakije ki barni ba xamu rayu tare har abada mu kula da ya'yan mu, you will get well soon Jiddatulmusty and El'mustapha is for only you jiddana, bana buqatar kulawar kowa sai naki, ya janyo hannunta ya hada qaramin yatsansa da nata,
Yace mun qulla, idan har akayi nasara akan aikin aka fito dake lfy I promise you kome kike so a duniyar nan xan maki shi indai baifi qarfina ba,
Tayi murmushi tana qara riqe mararta dake ciwo,
Idan kuma na mutu fa,
Baxama ki mutu ba jiddah stop saying dat rubbish ya bata ransa sosai, ta shafi fuskarsa tana murmushi,
Sorry Musty na, pray the best for me, xan dawo na cigaba da rayuwa da kai ina matuqar son ka.
Yace yauwa jiddatulmusty, ya sunkuyawa dai dai kunnenta yana rada mata addu'o'i da xatayi,
Tayi murmushi tana nanata addu'ar da ya gayamata a xuciya cikin hope din xata rayu tare dasu.
Haka aka jata aka shiga da ita, banda addua babu abinda suke.
GET WELL SOON JIDDATULMUSTY ❤
'Hajiya dan Allah kiyi haquri ki maidani titin da kika dauko ni ko ki bude min wannan gate naki na fita da qafafuna,
Hajiya Mariya ta tsaida cin Apple da take tana kallon uwani a wulaqance,
Tace kin gama gyara kitchen dinne,
Uwani tace da ban gama ba xaki ganni nan ne, har toilet din da kika ce na wanke, duk dakunan gidannan na gyara, ni nagaji dake nagaji da ganinki ki barni nayi tafiyata.
Kallonta take batare da mamaki ba xaman da sukayi da uwani ta fahimci yarinyar bata da tsoro gurin maida magana sai kaje dukanta ta soma baka haquri amma bakin baxai yi shiru ba ta rasa wace irin yarinyace wannan,
Tace kije tsakar gidannan shima duk sai kin share sa'anan ki dawo.
Uwani ta gyara tsayuwarta, hannayenta akan qugunta kerere take kallonta,
Nifa bamai aikin ki bace, ban taba yiwa kowa bauta ba sai ke, kibarni nayi tafiyata, na rasa me kike nufi dani, baki gaji da ganina bane.
Tana ganin Mariya ta tashi ta fita da gudu da tsintsiya a hannunta, ta daga murya tana fadin,
Kin sato nine kiyi kudi dani, nafi qarfin ki ko wanda xai yankani kisha jinina na kalleshi sai ya girgixa, tun da naxo gidannan ban taba ganin kowa yaxo ba sai kace mayya, ku.... Tayi shiru sakamakon ganin hajiyar ta fito da wata xungureriyar bulala, ba shiri uwani ta sunkuya tana shara,
Tace me kike cewa uwani, maimaitamin banji da kyau ba,
A sanyaye uwani ke kallonta,
Hajiya tunda baki ji mgnr ba abarta kawai ta wuce ta sunkuya da sauri tana sharar.
Dogon tsaki hajiya taja ta juya,
'Na daukowa kaina jaraba wannan shegiya ni ta isheni a gidannan, sai na gama axabtar dake xan fiddaki.
Uwani ta nufi gate din bayan ta ajiye tsintsiya, ta soma kiciniyar bude gate din amma ta kasa kusan kullum sai ta gwada yin hakan, ta leqa ta gate din tana fadin,
Wayyo a taimakeni, akwai wani a kusa ne, wata mata ce ta sato ni, a taimakeni.
Shiru bataji alamar motsin kowa ba,
Ta tsugunna tana leqe ta qasan gate yanda xata ga mai wucewa da kyau,
Kicibis idanunta na sauka akan wani qatoton kare baqi wulik sai fiddo harshe yake, taja da baya da sauri hade da dafe qirjinta saboda yanda yake bugawa, yanda taga Karen yana huci kamar xai cinyeta, aikuwa da ya tona mata asiri idan ya rabata da duniyar saboda baqin ciki ne xai mata.
Ta tashi ta cigaba da shara, tana gamawa ta shiga gidan,
Mariya.... Mariya take kiran hajiya🤔
'Na gama kixo ki sallameni idan ba haka ba wlhy sai in qona gidannan, nifa banda mutunci baki sanni bane sai na nuna maki, tun muna mu biyu kixo ki fiddani cikin wannan gidan naki mai wari da qaxanta, ashema dadin komai baa ci, ya'yan ki ma cikin wahala suke, tuni na gano kina daya daga cikin mutanen dake min baqin ciki da jin dadin duniya shiyasa kika kawo ni gidannan, to baxan xauna ba, hajiyata nake so ehe, itace ke sona bata min baqin ciki tana tausayina.
Tayi shiru tana saurare, bata ji an amsa ba kuma babu alamar motsi a gidan, ta lallaba a hankali ta isa dakin hajiya Mariya.
Ta xare idanu lokacin da ta tsinkayota kwance ta ware qafafunta tana tura wannan abun tsakanin cinyoyinta.
Jikin uwani ya dauki rawa ta juya da sauri tana maida numfashi.
Ita kam nata taba ganin musiba irin wannan ba, kaico da wannan rayuwa ta matar nan, ta xauna ta buga tagumi tana hawaye.
Wai ni meke faruwa dani ne, me nakeyi