Showing 66001 words to 69000 words out of 138779 words

Chapter 23 - El-mustapha Complete Hausa Novels By Fertymerh Xarah.docx

09 Oct 2025

2000

nayi karatu na sami ilimi, wlhy yayana baiyi karatu ba iyakar sa primary, saboda iyaye na basu damu da su nemawa ya'yan su ilimi ba, har gobe ina jin dadin da ban taso a gurin su ba da ko na arbiya banda a yanxu.

Ban sanar da ita komai ba saboda bansan yanda xata dauki xancen ba ina matuqar tsoron abinda xai hadani da ita taxo tana min kallon muguwa mai manta alheri.

Nayi qoqarin boye sirrin amma kusan kullum dare sai yaxo min dakina, ina barci xanji yana shafa jikina, da kokowa da komai nake samu na kwaci kaina naje na buya a toilet.

Ko na rufe dakin da key xai bude da wani ya shigomin, idan kuma fita unguwa tayi ta barni saboda nayi girki wlhy a gidan mu nake xuwa nayi mata saboda tsoron sa.

Da abin ya soma yawane na tattara kayana xan bar gidan, abinda anti bilkisu ta dauka saboda na girma xan mata butulci naje na barta, ta wahala dani tun ina qarama sai yanxu da girma yaxo mata nake son gudu na barta.

Ranar nayi kuka kamar me kuma tayi ta tambayata dalili naqi na gayamata illah na haqura na cigaba da xama a gidan.

Sai wani dare ne daya riskeni a daki ashe bayan fitowarsa ta tashi bata ganshi ba sai ta biyo bayansa,

Yanda yake qoqarin yi min fyade ta qarfi ya saka na soma ihu sosai iya qarfina a daren ashe ummana taji.

'Anty bilkisu na shigowa taga abinda yake qoqarin min ta saka ihu tayi kansa tana neman kwace ni a hannunsa kada ya jimin ciwo.

Tun da ya ganta kunya ta lullubeshi amma saboda halin su irin na maxa sai ya fara borin kunya ya hau dukanta,

Ina tare mata dukan, ya soma dukana iya qarfinsa, ta kasa jurewa ne taxo tana jansa tana kuka tana roqonsa ya daina kada ya jimin ciwo.

Marin ta yayi tare da hankadata ta bigi qarfen gadon da nake kwanciya akai, faduwar da tayi gurin ashe bata numfashi, yana ganin haka ya fita da gudu ya bar gidan,

Naje gareta ina kira sunanta tare da jijjigata amma ko motsi batayi, kuka nake bana ko ganin gabana naje ina debo ruwa ina kwara mata a tunanina ko suma tayi amma ko motsi batayi.

Ina cikin wannan halin ne sai ga mijin ya dawo tare da iyayena da yan sanda cewa na kashe masa mata harda kukan sa uwani.

Tsoro da faduwar gaba, ga tashin hankali suka min yawa, ummana bata yarda da maganarsa ba saboda ihu na da ta jiyo a lokacin sai ta soma kwankwanto, amma Abbana dukana ya riqa yi yana jifana da mugayen kalamai kan cewa naci amanar matar data riqeni da amana.

Hankalina ya tashi na soma jijjigata ina fadin ki tashi anti bilkisu ki gayamasu gaskiya, ki gayamasu bani ce na kashe ki ba, amma ina, inaji ina gani aka samin ankwa aka fiddani gidan ni kuka ummana kuka.

Ba wai ina kuka saboda qaxafin da aka min ba ina kuka rabuwa da anti bilkisu, ina kuka na rasa wannan matar mai haquri da amana,

Wlhy bani na kashe ta ba shine abinda kawai nake fada a kullum amma bani da shaida sai Allah kuma shi kadai xai iya fiddani a wannan hali da nake ciki.

Uwani ta xuba mata idanu tana kallonta, labarin ta ba qaramin girgixata yayi ba, bata ji wata nadama a tare da ita ba sai da ta tsinci kanta tana baiwa ladidi labarin tata rayuwar.

A lokacin ne take tunawa da alherin jiddah a gareta, haqurin ta da kawaicinta, soyayyarta da kulawarta, sacrifice din ta akan abinda take matuqar so da qauna a duniya,

Ta matsa kadan cikin tsoron irin kallon da ladidi ke mata na tuhuma,

Karo na farko a rayuwar uwani da taji tayi nadama akan wani abu da tayi a rayuwarta, xuciyarta ta cigaba da bugawa, idanuwanta na hasko mata jiddah da halin da ta saka ta a ciki,

Ta rumtse idanuwanta.  da qarfi bayan ta kai tafukkan hannuwanta a fuskarta ta saki wani irin kuka da bata taba yin sa ba.......

Vote.....

Yawan voting yawan posting😂

EL'MUSTAPHA

Haske Writers Association

Home of experts and perfect writers

Fertymerh Xarah💞

44

Kuka kike Uwani? Saboda me xakiyi kuka, mai xuciya irin taki bai kamata ya karaya da wuri haka ba..... Cewar ladidi tana kallonta cikin takaici.

Uwani ta dube ta idanunta taf da hawaye,

Ban taba nadama a rayuwata ba sai wannan karon, ban taba ganin banyi dai dai ba sai yau, ban taba jin tausayin wani a xuciyata ba sai yau, na dauka cewa duk abinda nake yi dai dai ne saboda ina son cimma wani buri nawa, babu mai gayamin gaskiya na dauka..... Nikam ya xanyi da rayuwata, ya xan gyara rayuwata, taya xan tunkari jiddah nace ta yafe min, na cutar da ita na sani kuma *NAYI NADAMA*, ta fashe da kuka.

Ladidi tace kadan Ma kika gani uwani, kinji haushi kuma ke butuluce maci amana kuma muguwa at the same time, xama da mace irin ki babu amfani domin ke abin gudu ce,

Koma me xakice wlhy nasani, na cutar da matar da ta riqeni amana kamar qanwarta, ta dauki iyayena tamkar nata, ta sakani makaranta tare da kula dani da xuciya daya, na dauki soyayya na dorawa mijinta tayi shige da fice wurin jajircewa dan ganin na mallakeshi saboda ciwon da nake mata na qarya, ta bani shi a matsayin mijin aure na, ni kuma na cutar da ita, na banxantar da rayuwarta, nayi qoqarin kashe ta da ya'yan ta domin na mallaki mijinta, na manta alherinta a gareni, nayi sanadiyar xamowar ta gurguwa, dan Allah ni wace irin mace ce marar imani, Dame duniya xata kirani, wane hali iyayena suke ciki a yanxu na baqin cikin dana saka su, ta cigaba da kuka sosai.

Shiru ladidi tayi bata tanka ba amma cike take da haushin uwani, ita wace irin xuciya ce da ita haka?

Ina ma nice ke uwani, ina ma nice na tsinci rayuwa irin taki mai cike da kulawa da amana, ina Ma nice akan position din da kike ciki before not now, ta ya xanyi wasa da dama ta nayi sake da kyautar rayuwar da Allah ya bani tare da uwargida mai sanyin hali irin na jiddah, ban ganta ba amma naji ina son ta a xuciyata, ita macece da xaa yi alfahari da samun irin ta, Allah ka jiqan anti bilkisu ka gafarta mata ka kuma dubeni da idon rahama ka fitar dani cikin wannan halin da nake ciki.

Runkes ta tsame hannuwanta cikin abincin da take ci, tana sud'e yatsun hannunta tana kallon ladidi, batare da tunanin komai ba ta shafe hannun a jikinta tana murxa yatsun hannuwanta.

Labarin ki ladidi yayi matuqar bani tausayi, naji tausayin ki matuqa, amma kinga wannan shegiyar ko kadan ban tausaya mata ba, kuma baki Ma ga komai a cikin rayuwar ki ba tukunna matuqar bakije kin roqi iyayenki da jiddah gafara ba.

Ni kin ganni na, Mahaifina na kashe da hannuna.... duk suka xuba mata ido suna kallonta da mamaki cikin tsoro.

Murmushi tayi mai dauke da kwallah a idanuwanta,

Tace bana nadama kuma bana jin xan taba nadamar kashe sa a rayuwata.

Sunana Rukayya, makarantar boarding nayi acan suke kirana Runkes, ina matuqar son iyayena da qanena a xuciyata, nice babba a gurin su.

Tun da na taso a gidan mu na sami mahaifiyata cikin qunci na rayuwa dalilin mahaifina, auren hadi ne aka masu daga iyayensu, bai taba son ta ko tausayinta ba, amma mamana tun sanda aka daura auren su ta dauke sa matsayin qaddarar ta, ta rungumeshi da hannu bibbiyu, tana girmamashi, tana qoqarin ganin ta faranta mashi ko yaya ne amma shi baya ganin, kullum cikin mata fada, mistake kadan xata masa ya hauta da duka koda a gabanmu ne ba ruwansa, koda baqi ne a gidan bai damu ba.

Mu uku mata sai yara maxa, in taqaice maku ban taba ganin axxalumin mutum da baisan darajar mace ba kamar sa, yes babana ne amma xan iya baiwa duniya labarin sa, I don't care ko xata xageni ban damu ba.

Sanda na gama secondary School dina na koma gida ne na tarar da wani tashin hankali a gidanmu, can you imagine babana yayi lalata da qanwata dake bimin, yar cikin sa kuma a gaban idon maman mu tana gani tana kuka, qanwata kuka.

Bansan yanda xan gaya maku halin da na tsinci kaina aciki ba ranar,

Muka dauke ta muka je da ita asibiti, ko kwana batayi ba ranar ta mutu, nan take mamana ta xube gurin a sume.

Xuciyata da kwakwalwata baxasu dauka ba, as my age at that time, ban isa na dauki irin wadannan tashin hankali ba, ban san yanda xanyi da rayuwata ba, babban tashin hankalina ace mamana ta mutu yanda naga likitoci sun duqufa neman ceton rayuwarta.

'Na bar asibitin naje na sanar da yan uwanmu, sai gasu kuwa sun xo asibitin cikin jimami.

Ni na boye masu abinda mahaifina yayi akan qanwata, nace wasu ne suka mata fyade kuma baa gane ko su waye ba.

Kowa ya tofa albarkacin bakinsa na tsinewa duk wanda keda sa hannu a mutuwar qanwana, haka suka dauko gawar suka dawo da ita gida, aka mata wanka, sutura da sallah kafin akaita makwancinta duk wannan abin da ake mahaifina bai sani ba sai da ya dawo gida.

Daya sami labarin mutuwarta babu tsoro ko nadama a tare dashi kuma ko addua bai mata ba, ni na rasa gane kansa qiyayyar da yakewa maman mu harda mu baya sone ko me?

Har aka sallamo mamana asibiti bai taba xuwa asibitin ya duba ta ba, haka muka cigaba da rayuwa dashi da dadi babu dadi.

Duk wanda yaxo neman aure na baya bari sai yace wai ni yar iska ce,

Da mamana ta same sa da maganar har dukanta yayi a ranar

In taqaice maku sai ga mahaifina yana neman lalata dani kamar yanda yayi da qanwata,

Mamana ta ceceni ranar a hannunsa,

Baa dauki wani lokaci ba ta kamu da hawan jini mai tsananin gaske da yan uwanta suka sami labari suka xo suka dauke ta acewar ta bar mashi ya'yan sa daya kashe ta a banxa gwanda mu mutu a hannunsa ba damuwar su bane itace tasu.

Hankalin ta ya tashi sosai bata iya barin mu a hannunsa sanin halinsa, ta roqe su su barta taje da ya'yan ta mata kada ya lalata mata su idan ya so a bar masa maxan.

Maxan ma sune qanana a cikinmu kuma suna buqatar kulawar uwa idan mama taje ta barmu da su ya xamuyi da rayuwar mu.

Sai a sannan ne baba yayi magana ya bada haquri akan komai ya wuce insha Allah.

Kamar gaske ya daina shiga shirgin mu babu ruwanshi damu yana yin rayuwarsa shi kadai baya kula kowa a gidan koda kuwa mun gaidasa baya amsawa.

Babu ruwanshi da cin mu ko sha, sutura ya dade da daina yi mana komai maman mu ke mana dayake ita tana da abinta kuma tana karban salary irin na local government haka, so bata damu ba, hakan da yayi ya fiye mata alheri na ganin ya daina kula mu.

Bayan kwana biyu sai ya fara kawo mata a gidan ya kwanta dasu har Safiya dan baya tsoron Allah, a haka washe gari xai sallame su batare da yaji kunyar ko mu dake ya'yan sa ba.

Maman mu da baqin cikin haka take kwana kullum dare na Allah sai tayi kuka kafin ta kwanta, a boye takeyi kada mugani kuma ni bata san nasani ba, sannan ta hana muyi masa magana ko rashin kunya duk wanda yayi da kyau ya sani.

Haka muka xubawa sarautar Allah ido muna roqon Allah ya kawo mana sauqin abin.

Bana manta wannan ranar a rayuwata, ina wanka sai ga baba ya shigomin a toilet kafin nayi wani yunquri sai naga ya soma cire kayan jikinsa yana tunkaro ni.

Kokowa mukayi sosai har na samu na kwaci kaina daga gare sa, ina qoqarin fitowa ya biyoni tsantsin ruwa suka ja sa ya fadi ragwaf a gurin,

Bacin rai da gushewar tunani ya saka ban lura da jinin dake fita a hanci da bakin sa ba na dauki bucket na soma dukan sa dashi ina kuka.

Jinin dana ga yana fita a jikinsa ya saka na saki bucket din na fito a gigice ina ihu.

'Na kashe baba.... Shine abinda ya fito bakina lokacin da mukayi ido biyu da mamana.

Jikinta na rawa naga ta nufi toilet din hankalinta a tashe bata jima ba ta fito da sauri tana kallona.

Me kika masa rukayya? Jikina na rawa na gayamata komai ban boye mata ba.

Ta dafa ni tana kuka sai dai ta rasa me xata ce,

Ana haka sai ga qaninsa yaxo gidan da kayan wankinsa a hannu dama shi ke masa, koda ya ga abinda ke faruwa ya fita da gudu neman yan sanda.

Rukayya ta cigaba da kuka tana fadin, mamana tace ita ta kashe babana, ta dauki laifin ta dorawa kanta bata yarda aje dani ba.

Ni kuma naqi amincewa da hakan saboda qannina, idan taje ta barmu taya xan iya kula da su, bani da komai da xan kare kaina da su, gwanda ita mahaifiyace sunfi buqatar ta akaina, kuma taya xata dorawa kanta laifin da ba itace ta aikata ba, axo a hukuntata a banxa.

Ta share hawayen ta tana fadin, an kusa yanke Mani hukunci bada jimawa ba, ni na kashe mahaifina kuma nasan dole a kashe ni nima, duk maana taxo nan sai tamin addua tana kuka take barina.

Qaddara ta kenan haka Allah ya tsaramin tawa rayuwar kuma na karba da hannu biyu tare da fatan Allah ya bani ikon cinye jarabawar har lokacin da xaa yanke min nawa hukuncin cikin wannan watan.

Kuka sukeyi sosai babu mai rarrashin wani a cikinsu.

Daga sama su kaji muryar Aj na basu nata labarin.

Labarin ku ya bani tausayi matuqa nawa duk mai sauqi ne akan naku, Sunana Amira, ana kirana da Aj kasancewar sunan saurayina Jamal.

Baxan boye maku ba ni macece mai matuqar kishi sosai, ina son Jamal kamar raina bana son mace ko wace iri ce ta rabe shi, ko qanwarsa ban yarda da ita ba indai akan sane.

Idan yaxo hira inda nake ina bashi kulawa sosai na ganin na faranta masa, bawai na bashi jikina baa, tsabtacciyar soyayya muke dashi kuma na tabbata har a ransa yana matuqar sona.

Idan xai koma gida baya sani nake bin bayansa a cikin napep ko saman Babur idan ban sami mai napep ba,

Ina bin bayansa na gani ko xai tsaya da wata mace a hanya ko kuma xai biya gurin wata mace ne ban sani ba, sai na tabbatar ya shiga har cikin gidansu da motarsa hankalina ke kwanciya na dawo gida na biya mai napep din.

A school kowa ya sanmu tare ana kirana Aj shima haka ake kiransa, Department din mu ba daya ba amma duk da haka na saka a dubamin duk ranar da ya kula wata macen a gayamin.

Harta kai bana boye masa kishina a gurinsa, ya sani har baya son ganin ya batamin.

Amira indai akan mace ne ki kwantar da hankalinki Jamal ne kin riga kin samu har abada baki da miji kamar ni..... Kullum mgnr sa kenan a duk lokacin da kishina ya motsa.

Nifa har mamanshi ina kishi, duk ranar da yaxo gurina da wuya ne bata kirasa a waya cewar yaxo ba ko kuma tana buqatar yaxo ya xata aikeshi, sosai abin ya fara damuna har nake ganin kamar da gangan take min haka.

Yace amira ummana Ma bata san ina xuwa wurin ki ba kawai dai buqatar ta tana xuwa dai dai da sanda naxo nan ne kuma baxan qi xuwa gurin ta saboda ina matuqar son ta mahaifiya tace.

Kalamansa sun matuqar bata min rai ashe har akwai macen da Jamal xai so a duniya bayan ni ya dauketa da muhimmanci haka, kwata kwata kishi ya rufe min idona na manta cewa wannan matar fa mahaifiyar sa.

'Washe gari na shirya naje har gidan saboda nayi warning din ta akan abinda take min bana so.

Tace ke kuma wacece, daga ina haka? Wane yaro kike magana akai Jamal ko Mubarak?

Jamal nake magana hajiya, nasan ke kika haifesa kina da iko akansa amma ba hakan xai saka ki shiga haqqina ba, kinci naki xamanin kixo kici nawa sai yaxo hira gurina ki soma damunsa da kira akan yaxo meyasa kike min haka?

Tsananin mamakin ta ya saka hajiyar xuba mata idanu, bata gama mamakin ba taga Amira ta xube qasa tana kuka tana roqonta,

'Dan Allah hajiya kiyi haquri idan kinji haushi ina matuqar sonsa da kishin sane dan Allah kidaina min haka idan yaxo.

Tau shikenan cewar hajiya, tace ya sunan kine.

Tace amira,

Kije gida ba komai..... Bayan fita ta Jamal ya dawo gidan take tambayar sa wacece Amira?

Da tsananin mamaki yake kallonta,

Hajiya ina kika san amira?

Tace ina tambayar ka kana tambayata, wacece amira?

Jikinsa yayi sanyi yace wacce xan aura ce hajiya.

Tace Sam ba dai a gidannan ba, kuma tun wuri ka cire ta a xuciyarka baxaka taba auren ta ba.

Meyasa hajiya ya tambaya cikin tsananin mamaki, ina sonta tana sona, kada ki biyewa xancen mutane suxo su bata ta a gurin ki hajiya.

Har akwai wani xance da xanji bayan wanda naji da kunnuwana kuma na gani da idanuwana,

Nan take ta gayamasa komai duk

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login