Showing 45001 words to 48000 words out of 138779 words
Chapter 16 - El-mustapha Complete Hausa Novels By Fertymerh Xarah.docx
ta qarasa dakin da sauri sukayi kicibis da keken arham har ya taka mata qafa,
Ta dauke qafar da sauri tana yatsina fuska, arham ya soma dariyarta.
Meyasa aryan ke kuka, ina anti jiddah?
Bata nan shine yake kuka?
Bata nan, banan ta maimaita cike da mamaki, ta juya ta fita xuwa harabar gidan, tabbas bata nan dan babu alamar motarta a gidan,
To ina anti jiddah xataje da magrib haka, ita bata da waya ballantana ta kira ta taji, tana tsaye gurin yaran suka fito, haka ta riqa jin faduwar gaba, taji bata jin dadin jikinta babu nutsuwa a tare da ita wanda bata san dalili ba tunda ba yanxu bane jiddah ta fara fita.
Ta dauki aryan dake kuka, kukan sa na qara rikitata tana jin ba daidai ba a jikinta, bata da nutsuwar da xataje tayi sallah, sai ta tsinci kanta tana xubar da hawaye.
Asp Bello yaxo alwallah ya ganta tsaye da aryan yana kuka, ya tambayi dalili ta gayamasa.
Yace tun daxu ta fita gashi bata dawo ba kada oga ya dawo bata nan, sai da akace wani a cikin mu ya bita tace nan ne kusa urgent aka kirata baxata jima ba.
Shiru kawai banan tayi, shima ya juya, ta Goya aryan bayanta tana jijjigashi sai safa da marwa take a harabar gidan, arham na rakube gindin wata flower.
Suna haka aka wangale gate din duk suka juya suna kallo.
Motocin el'mustapha ne suka shigo, gabanta ya tsananta faduwa, aryan ya soma qoqarin saukowa ba musu ta sake shi daga shi har arham suka nufi motar mahaifinsu da gudu suna murnar dawowarsa.
Daddy is back...
Duk da gajiyar da yake dauke da ita bai hana masa daukan su duka ba, babu walwala a tare dashi, tun daxu yake jin weakness a jikinsa, ga wata irin faduwar gaba da yake ji, tare yake da babban aminin sa ibrahim wurin aikinsu daya sai dai kowa da nashi matsayin.
Ba ku gaida second daddy ba cewar el'mustapha yana kallon yaran,
Suka soma dariya suna kallon ibrahim,
Second daddy ina wuni...
Daga ibrahim har el'mustapha ba wanda baiyi dariya ba, ya sauke su yana kallon banan sanda suka qaraso gurin,
Ta gaidashi tare da abokinsa kanta a sunkuye.
Me kukeyi anan keda twins?
'Anty jiddah ce tun daxu ta fita bata dawo ba, sai ga hawaye sharrr na bin kumatunta.
Nan take yaji gabansa ya fadi, ya juya yana kallon motocin gidan duka suna nan har ta uwani banda ta jiddah, kenan jiddah ita kadai ta fita.
Ibrahim yace kun duba ko ina a gidan bata nan ne?
Tace wlhy ko ina mun duba bata nan.
El'mustapha ya juya ya nufi gate,
Yaushe jiddah ta fita daga gidannan.
Daxu sir, suka amsa masa cikin girmamawa,
Ya akayi kuka barta ta fita ita kadai ko akwai wanda ya bita ne.
Suka soma inda inda cikin rudewa, kowa ya kasa magana saboda tsoro abinda ya qara fusata el'mustapha har yayi masu tsawa, ba shiri daya ya soma magana,
Munyi iya qoqarin mu ta bari muje da ita taqi, tace its urgent an kirata ne yanxu xata da..... Bai qarasa ba el'mustapha ya dauke shi da Mari cikin bacin rai abinda basu taba gani ba tun tarayyar su dashi.
What nonsense are you telling me, ya nayi daku a gidan nan saboda tace haka sai kuka barta ta tafi, kuka xauna kuka miqe qafa anan, to miye amfanin ku if you can't stop her.
Sorry sir suka fada jikinsu a sanyaye,
Waye tace ya kirata..
Bata fada ba sir...
El'mustapha ya furxar da wani xaxxafan iska a bakinsa
Yace believe me idan wani abu ya sami jiddah, ya sami aikin kune, daya bayan daya duk sai na sauke ku, kuje ku nemo ta duk inda ta shiga ina jiranku.....
Ba bata lokaci suka shiga motoci suka raba hanya, el'mustapha ya dafe kansa da hannuwansa biyu, tunani yayi da sauri ya xaro wayarsa aljihunsa ya soma qoqarin kiran layin jiddah, kwata kwata bata shiga, ya kira mamanshi yana tambayar jiddah taje,
Bata xo ba el'mustapha, me ya faru, me ya sami jiddah ne?
Ba komai ya tsinke wayar, hajiya ya kira yana tambayar ta jiddah,
Ba muyi magana da ita xata xo ba kuma bata xo din ba,
Ya tsinke wayar da sauri, hankalin hajiya ya tashi, ta gayawa abba Sam jikinta bai bata akwai lfy ba, Allah yasa ba wani abin ne ya sami jiddah ba.
Duk inda el'mustapha ke sa rai ga ganin jiddah yaje sai ace masa bata je ba, gidan qawayenta duk inda yasan tana xuwa sunje ranar shida ibrahim.
Duk wannan bidirin da ake uwani na dakin ta kwance abinta ta saka earpiece a kunnenta tana shan waqarta abinta batare da damuwa ba.
Banan kuwa tayi qoqarin ganin twins sunci abinci ta saka su barci da kyar saboda fitinar mom din su, ta gabatar da sallolinta tare da addu'ar Allah ya bayyana jiddah ya kare ta daga sharrin masu sharri.
Dawowar su el'mustapha tayi dai dai da dawowar yaransa, kowane jikinsa a sanyaye babu labari amma ga motar ta sun sama a hanya sun rufe sunxo da key kasancewar babu iska a tayoyin.
El'mustapha yayi shiru kamar xaiyi kuka, tunani yake me ya fitar da jiddah, waye ya kirata urgent, su waye suka dauke jiddah, meyasa suka dauke ta, me jiddah tayi masu, sai ya juya xuwa cikin gida, hannunsa yasa yana dauke wasu kwallah.
Insha Allah xaa ganta ka kwantar da hankalin ka xamu tsananta bincike daga yau xuwa gobe, kada kasa damuwa a xuciyarka, cewar ibrahim yana kallon el'mustapha bayan sun xauna a falon.
Innocent jiddah, sun dauke min jiddah akan wane dalili?
Wa kake xargi el'mustapha, waye kake ganin xai iya yi maka hakan.
Mutum daya nake xargi, jiddah bata da abokin gaba ko fada, kuma ni a iya tunani ban san nayiwa wani ko wata wani abin da xaa kullace ni ace xaa dauki mataki akan matata ba.
Waye kake xargi,
Uwani nake xargi, el'mustapha ya fada yana kallon ibrahim cikin seriousness.
Nafi kowa sanin uwani bata son jiddah, she can do anything for her I know, idan har uwani na da sa hannu a batan jiddah believe me ibrahim wlhy xan iya kashe ta, I hate her.
Ya daga murya yana kiran banan.
Ina uwani?
Ina ji tana ciki, ita Ma ban ganta ba duk yau.
Kiramin Uwani taxo yanxu.
Pherty...... ✍🏻
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
35
Uwani ta shigo falon tana tauna cingam, yanayin fuskar el'mustapha yasa ta shiga taitayinta, ta tattaro nutsuwarta guri daya ta xauna tana gaida su.
Kallonta el'mustapha keyi da idanunsa da suka rikide, observing yake akan ta, yana son sanin wani abu a tare da ita,
Muryar ibrahim taji yana fadin, Jiddah bata sanar dake inda xata je ba kafin ta fita.
Uwani ta yatsina fuska tana kallonsa, idan xata fita bata gayamin ai, nima bana gaya mata kowa yana rayuwarshi ne shi kadai.
'Wannan rayuwar bata yi ba Sam uwani, cewar ibrahim yana kallonta fuskarsa ba walwala, keda bakinki kike fadar baki damu da rayuwar jiddah ba? Ke wace irin mace ce mai manta alheri? Ki tuna jiddah ta taimakeki ta tallafi rayuwarki, abinda take matuqar so fiye da komai a duniyar nan ta sadaukar maki uwani, ba kowace mace xata iya abinda jiddah tayi akan ki ba, tana xaune dake da xuciya daya ne, tana sonki tana son kyautata maki tana so ku xauna xama na amana ku hade kanku domin farin cikin mijinku, duk wanda yasan jiddah yasan mutuniyar kirkice bata da keta a rayuwarta ko niyar cutar da wani, kiji wata magana da kike fada yanxu ba dadin ji wai ba wanda ya damu da rayuwar wani kowa yana tasa rayuwar nan, na tabbata da jiddah ce baxakiji wannan kalma a bakin ta ba.
Jikin uwani yayi sanyi, tabbas gaskiya yake gayamata akan jiddah, sai tayi qoqarin fooling dinsu kada su xargi wani abu a tare da ita.
Nagode da nasihar da kake min a ynxu kuma insha Allah xan gyara, bari Ma naje na bata haquri.
Ibrahim ya qara tsaidata, kina nufin wai bakisan abinda ake ciki bane game da batan jiddah.
Kallonsa take baki a bude,
Wlhy ban sani ba, ina taje ne.
Banan da el'mustapha sai kallonta suke, kwata kwata banan bata xargin uwani akan batan jiddah ba kamar yanda el'mustapha ya kafe ta da idanuwa yana observing wasu abubuwa.
Yau na shiga uku, baa ga anti jiddah ba, ina taje da wannan cikin me ya same ta, sai ta soma hawaye.
Banan ma ta soma sharar kwallah,
Abinda uwani taji el'mustapha ya furta ne yayi kusan sumar da ita daga inda take xaune,
Jiddah ta gayamin kece kika kirata a waya ta fita, ina kika kai min matata ta?
Ni? Uwani ta tambaya tana fiddo idanuwa saboda tsananin tsoro da rudewa,
Wlhy ban kira ta, bana waya da jiddah, saboda me xan kirata ta fito?
Jiddah xata min qarya kenan ya qara tambayar ta bayan ya kafe ta da manyan idanuwansa yana son ya gasgasta xargin sa akanta.
Uwani ta qara rudewa ta fashe da kuka wanda ke nuna a tsorace take, amma tunani take har yaushe jiddah ta kira el'mustapha ta gayamasa, kodai so yake ya nuna mata halin su na yan sanda ya gani tunda haka suke bincike mai tsanani akan wanda suke xargi.
Wlhy bani na kirata ba, kowa yasani bana waya da jiddah, ban ma san sanda ta fita daga gidan ba ina daki a kwance, wlhy bani bace ban san komai a kai ba.
El'mustapha ya qara kallonta, Uwani idan nagane da sa hannunki a batan jiddah........ sai kuma yayi shiru ya barwa kansa sani, ya cigaba da fadin ke nake xargi kuma har yanxu xuciyata ke take xargi, xan iya shigar da qara kotu akan ina xargin ki da batan matata saboda nasan ba kyason jiddah baki da buri a duniya na ganin kin kawar da jiddah saboda ki mallaki xuciyar el'mustapha, kinsan nasan bakya qaunar jiddah itace din dai bata gano hakan ba, itace ta rasa gano illar uwani a tare da ita, ta dauki so da amana ta baki wanda ke baki da wani buri na ganin kin cutar da jiddah,
A matsayina na dan sanda xan cigaba da bincike lungu da saqo na ganin masu sa hannu a batan jiddah, xanje na nemota a duk inda take, indai kina da sa hannu a batan jiddah ayi gaggawar maidata inda aka dauketa, ko rantsuwa nayi baxanyi kaffara ba indai da sa hannu uwani a batan jiddah believe me ibrahim alqawari ne nine mutum na farko da xan fara kamata dumu dumu da hannuna, ya tashi ya fice zuciyarsa na quna.
Ibrahim ya kalle ta shima jikinsa yayi sanyi sosai,
Kinji abinda el'mustapha yace uwani, tsakanin ki da Allah ba hannunki a batan jiddah, ki fada min gaskiya ni xan iya kare ki a gurin sa kuma nayi maki alqawari baxan taba bari ya sake ki ba hassalima xanyi qoqarin ganin na dai dai ta ku ya so ki kamar jiddah.
Iya kar gaskiya ta nake fada maku banda masaniya akan batan jiddah.
Indai kinsani dan Allah karku cutar da jiddah,
Ya tashi yabi bayan el'mustapha suka barta anan, banan Ma tashi tayi ta barta.
Washe gari tunda sassafe ibrahim da el'mustapha suka baxa yan sanda bincike ta ko ina, sai sanarwa ake ga duk wanda ya ganta idan kuma kidnapping ne a sanar da su ko nawa ne xasu biya amma kada su taba lafiyar jiddah.
Sai lokacin da hajiya taga hoton jiddah a TV ana sanarwa batan ta sa'anan ta san halin da ake ciki, kuka tayi shi sosai, ranar ita da abba suka je abuja babu kwanciyar hankali tare dasu.
Mama Ma baa barta baya ba, batan jiddah ya taba xuciyarta har ciwon ta ya dawo saboda damuwa, gwanda ace mutum ya mutu da ace ya bata baa san halin da yake ciki ba.
Duk sisters din el'mustapha suma sun shiga damuwa sai dai babu mai xargin uwani duk a cikin su sai hajiya kadai da el'mustapha.
Yanda uwani ta dage tana kuka tana neman jiddah ya saka sauran mutane basa xarginta amma banda hajiya.
Tace nice na haifeki uwani, na raini ki da hannuna har kika kawo wannan lokacin, ba wanda xai bani labarin halinki ciki da waje sai Ma ni da xan bayar, nafi kowa sanin wacece uwani duk da jiddah ta fini kusanci dake amma Sam bata san halin ki ba, nasan ba kyason jiddah, nasan kin auri mijin tane saboda ki raba ta dashi, ki tuna yanda yarinyar nan tayi shige da fice na ganin kin auri mijinta duk da kowa baya so, ta dauki nauyin karatunki, cin ki, shan ki da suturar ki duk yana hannunta, bata taba aiko mana ko kudin handout naki a bada ba duk itace, ta dauke ki tamkar qanwarta uwa daya uba daya, ta dauki iyayenki da daraja fiye da yanda kika dauke su, ta girmama su tana masu tarbiyar da bakya masu, ta rufa wa iyayen ki asiri da dukiyar ta wacce itace mahaifinki ke juya mata, ta so ki da xuciya daya, ta xauna dake babu cutarwa, ki dubi girman Allah ba dan iyayenki da basu da daraja a gurin ki ba idan kina da sa hannu a batan jiddah kiyi gaggawar maidata kada ki bari a cutar da baiwar Allah, salihar mace mai haquri da yakana.
El'mustapha na labe duk basu sani ba, inda yake labe hawaye yake sai kunga yanda ya koma cikin kwanaki biyu da batan jiddah, ya fita hayyacinsa bashi da lokacin kowa da komai sai na kewar jiddah, xuciyar shi babu sukuni sai faduwar gaba a duk lokacin da ya dubi twins suna neman mahaifiyarsu,
Uwani ta dubi hajiya sosai kalaman hajiya sun shige ta, wannan karon kukan da take na gaskiya ne ba dan komai ba sai dan tausayin jiddah, meyasa jiddah keda masoya haka, meyasa mutane da yawa suka damu da batan jiddah, meyasa mutane da yawa suke kuka suna mata addua, meyasa kowa ke fadin alherin jiddah ake yabata a ko ina,
Taurin kai irin na uwani Sam bai sa taji xata fadi gaskiya ba duk da tayi nadama, tafiso sai burinta ya cika tasan akwai lokacin da watarana xasu manta da jiddah su shafe shafinta a rayuwarsu hakan xai bata damar cimma burinta na ganin ta mallaki el'mustapha yanda take so.
Uwani batayi magana ba sai sharar kwallah take, ita Ma hajiyar kuka take,
Tace indai uwani akwai sa hannunki aciki baxan taba yafe maki ba, kuma baxaki taba cimma duk wani buri naki ko quduri akan jiddah ba, idan kuma babu hannunki ciki ina roqon ko waye Allah ya Toni asirinsa da gaggawa.
Duk wadannan kalamai na hajiya bai sa xuciyar uwani ta karaya ba ita a tunanin ta haqqin mahaifiyarta baxai taba kamata ba tunda ba cin amanar ta tayi ba.
A hankali el'mustapha ya janye jikinsa daga qofar dakin, tafe yake baya ganin gabansa, kuka yake kamar mace idan ya tuna jiddah da cikin dake jikinta, jiri ya soma dibansa, lokaci daya ya fadi gurin ragwaf ba numfashi a tare dashi.
Inna ta saki ihu domin itace a gurin sanda el'mustapha ya fadi, hajiya da uwani suka fito a firgice, securities Ma suka shigo a firgice kowane dauke da bindigarsa tunanin su ko wani abinne daban.
Ganin el'mustapha kwance a gurin yayi matuqar tsorata su, nan da nan aka dauke sa suka nufi asibiti dashi.
Gida da waje maqota abokan arziki, yan uwa babu abinda suke a duk lokacin da suka kai goshin su qasa yayin sujjada banda addu'ar Allah ya bayyana jiddah ya kare ta ya kuma Toni asirin wadanda suka sace ta.
*Team Jiddatulmusty kuyi haquri😒*
*Team Uwanitilmusty kuyi ta murna*
*Team El'mustapha kuje xuwa jinya*.
Pherty........ ✍🏻
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
36
Bayan sati biyu
Cikin kwanakin da jiddah tayi ta dawo wata iri, tayi kuka har ta godewa Allah, bata da wani tunani a xuciyarta yanxu sai na mijinta da twins nata.
'Ashe gaskiya el'mustapha yake gaya mata game da uwani, uwani ba mai qaunarta bace, yanxu ne ta gano abinda el'mustapha ke nuna mata a lokacin yake son ta gano, kenan yasan uwani qaryar ciwo take masa domin ta cutar da rayuwarta, she didn't deserve dis hatred from uwani.
Ta soma kuka mai fitar da sauti, mai nuna alama da baqin cikin dake tattare da xuciyarta, tayi nadama kuma ta tsani uwani a rayuwarta, tana jin baxata taba yafewa uwani ba, yau gashi ta dalilin uwani ta kasa sarrafa qafar ta daya, ta raba ta da ya'yanta da mijinta, ta raba ta da jin dadin ta, an kawo ta an girke inda babu kulawa cikin qartin maxa, ta kwana dasu ta yini dasu, basu da aiki sai shan barasa da chacha, sallah Ma a xaune take yin ta shima wai sai sanda suka ga dama suka kawo mata abinci da ruwa take yin rarrafe ta shiga toilet da kyar tana kuka.
Yanxu kuma taji cikin yayi mata wani iri, ya qara nauyi, motsin da yake yi a da yau kam bata jisa ba,
Ya Allah ka raya min abinda ke cikina, ta maida kanta jikin gwiwowinta tana kuka sosai.
Tana haka goga ya shigo, shi dai Allah ya sanya masa tausayin jiddah, sati biyu da yayi tare da ita ya gane tana da sanyi, tana da nutsuwa da kamun kai sosai yanda take ta rufe jikinta