Showing 63001 words to 66000 words out of 138779 words

Chapter 22 - El-mustapha Complete Hausa Novels By Fertymerh Xarah.docx

09 Oct 2025

1996

fadin bari naje na qara ganin wannan patient tawa naji dalilin da yasa take son yi mana qaura bayan muna kula da ita.

El'mustapha dariya kawai yayi yabi bayansa batare da yayi magana ba.

Har lokacin da suka shiga tana kwance sai hawaye take yi a tunanin ta el'mustapha fushi yayi yaje ya barta, ta juya tana kallon bakori.

Yace harda kuka jiddan musty ne ko jiddatulmusty? Saboda me kike son komawa gida bayan anan Ma xaki fi jin dadi.

El'mustapha ya soma hada kayansu ba tare da yayi magana ba, abinda yaji jiddah ta fada ne ya saka shi dariya batare da ya shirya ba.

Likita mosquito ke ta cixo na kullum, ko daxu ya cije ni a qafana mai ciwo....

Dariya sosai bakori yayi yana kallonta cikin tsananin mamaki,

Sauro anan asibitin jiddah, kada ki mana sharri saboda kina son xuwa gida.

Ta soma share hawayenta ganin el'mustapha yana fita da kayansu da alama gida din xasu je, bakori da kansa ya soma taya sa fitar da kayan har motar sa.

Ya ciro wayarsa a aljihunsa ya kira anty ikram cewa kar taxo asibitin suna gida, duk wanda yake ganin xaije ranar ya kira kada su xo suna gida.

Bakori yayi masu sallama ya fice, ya shigo dakin saboda qaguwa har ta saka hijab nata,

Fuskarsa ba walwala ya cire mata hijab din sai kallon mamaki take binsa dashi lokacin da ya dauke ta ya nufi toilet da ita, kiyi tsarki kiyi alwallah lokacin sallah yayi nasan da kinje gida yanxu mutane baxasu barki yin sallah ba.

Bayan ta gama ya maidota dakin kan darduma ya ajiyeta xaune, ya barta tayi sallah a xaune kamar yanda take yi kullum, shima ya shiga yayo alwallah yaxo ya tada tasa.

Suna gamawa bai jira komai ba ya dauke ta suka fito.

Kallonsa take tana mamakin qarfi irin na el'mustapha kuma har lokacin yaqi ya sakarmata fuska alamar fushi yake da ita.

Suna yin parking harabar gidan, ya fito a hankali ya bude motar ya soma fito da kayansu daga booth,

Mummy is back.... Cewar aryan dake buga ball harabar gidan, ya jefar da ita da gudu ya nufi motar,

Arham na jin aryan ya ajiye kekensa shima ya fito da gudu yana mummy.. Mummy...

Kafin kace me sai ga maaikatan gidan da saurin su sunxo gaida jiddah, tana xaune cikin motar sai kallon su take da murmushi a fuskarta sai ka rantse bayan cikin babu wata matsala a tare da ita.

Su banan suka soma shiga da kayan cikin farin ciki,

El'mustapha ya shiga cikin gidan bai jima ba ya fito da wheel chair baya so ya dauke ta gaban yaran saboda surutun su amma duk da haka bai tsira ba, suna ganin ya dorata a ciki ya fara janta, arham ya dube sa,

Daddy why is she on wheel chair?

Becos of her pregnancy, baka gani ne,

Aryan yace, yaushe xata bamu New baby daddy, you olways say mummy xata kawo New baby when she is coming back.

Kayi wa mummy addua very soon baby xai xo,

Suka fara tsalle, a tare suka riqa wheel chair din da jiddah ke xaune kafin el'mustapha yayi wani yunquri tuni sun tura ta da qarfi suna dariya,

Kai.. Kai... Kai.. El'mustapha ya nufe su da sauri kamar xai dake su, suka saki keken da gudu suka matsa suna kallonsa sanda yayi saurin riqe jiddah tana gab da faduwa, ita kanta a tsorace take.

See what am telling you jiddah, ya ja qaramin tsaki yana kallon yaran suna tsaye suna kallonsa, su duk a tunaninsu xasu riqa tura mummy ne aciki tunda baby baxai barta tafiya ba kamar yanda daddy yace,

El'mustapha yace duk na qara ganin wani a cikin ku ya tura wannan wheel din sai na dake sa ko taba ta yayi kamar haka... Ya nuna masu, sai nasa belt na dake sa.

To daddy waye xai riqa tura ta? Aryan ya tambaya yana kallonsa,

Ni xan riqa tura ta kullum, ina ga yaro ya qara taba ta ko?

Arham yayi caraf yace harda anti banan idan ta taba xaka dake ta?

Of course ya fada yana kallonsu cikin bata fuska,

Jiddah na xaune na kallon ikon Allah ba qaramin auna arxiki tayi ba da sun kayar da ita yanda suka turo ta da qarfi,

El'mustapha ya tura ta xuwa cikin gidan suna biye dasu a baya, suna isa falo suka soma tsalle farin ciki suke ji a xuciyarsu sosai mahaifiyar su ta dawo gida.

Ya dauke ta ya dora ta akan kujera, duk suka xauna suna kallonta suna kallon qaton cikin ta,

Arham sarkin son jiki tuni ya shige jikinta ya kwanta sai sauke numfashi yake a hankali, farin cikin xuciyarsu ba sai an tona ba.

Aryan yace mummy anan gidan xaki kwana ko?

Ta gyada kai tana kallonsa, dariya yayi wacce ta bayyana fararen haqoransa,

El'mustapha na xaune nesa dasu kadan yana Danna wayarsa, banan ta shigo da qaton tire a hannunta jikin ta har rawa yake saboda farin ciki,

'Anty jiddah kici duk abinda kike so anan idan kuma babu ki fada na kawo maki koda na girkawa ne yanxu na girka maki.

Murmushi jiddah tayi tana kallonta,

Oh banan sarkin hidima, ni na qoshi a yanxu sai dai xuwa anjima kimin d'an wake ina missing din sa sosai.

Cikin jin dadi, tau shikenan anty jiddah bari naje na fara hadawa tun yanxu, ta juya ta fice.

Jiddah tayi shiru tana kallon falon, xaman ta tare da su kurma bata taba tunanin xata dawo cikin gidan tayi rayuwa da ya'yan ta ba, sai gashi yau tana rungume da su acikin gidan ta tare da mijinta cikin tsananin farin ciki shiyasa bata debe tsammani ga rahamar ubangiji wataqila inda sauran kwana a gaba ta tashi da qafafunta.

Ta qara rungumesu a jikinta tana shafar kansu a hankali, ta dago tana kallon inda el'mustapha ke xaune dai dai lokacin shima ya dago yana kallonta, harararta yayi ya dauke idanunsa akanta, murmushi kawai tayi tana kallonsa,

El'mustapha mai son ta ne xata iya baiwa duniya labarin haka, kome xai mata birgeta yake yana fushi da ita saboda taqi xaman asibiti ita kuma xama da ya'yan ta ya fiye mata farin ciki da kwanciyar hankali.

Baxata taba mance ranar da el'mustapha ya xubar da hawayen shi na farko akan ta ba saboda ta nakasa, to wanne ne xai kasance na biyu???

*

Da dare yaran sunyi barci,

Wanka el'mustapha yayi mata ya bata kayan barcinta tunda yasan xata iya sakawa ya shiga toilet din.

Bai jima ba ya fito toilet din da qaramin towel a hannunsa yana tsane gashin kansa,

Ya xura rigarshi ta pyjamas yana kallon ta,

Tana kwance cikin doguwar rigar da ya bata mai tsantsi marar hannu,

Kyawawan cinyoyinta a bayyane, qafafuwanta a miqe sambal sai ka rantse lafiyar ta qalau baa dauke da wata lalura.

Son matarshi da qaunarta na qara girgixa xuciyarsa, yana hargitsa gangar jikinsa tare da rura wutar soyayyarta a tare dashi, ya qara qarfin AC bayan yayi wa kansa kyakkyawan matsuguni  a kusa da ita,

Ta bude idanuwanta a hankali tana kallonsa, murmushi tayi masa mai tattare da gajiya,

Jikina ba dadi el'mustapha, na kasa barci.

Baxaki iya barci batare dani ba I know, wannan kawaicin ki ajiye shi a gefe ki rungumi mijinki shi kike so jiddah, I need you too, kafin tayi magana ya tashi ya soma bin jikinta da massage dan taji dadin jikinta, ta lumshe idanuwanta a hankali kamar mai jin barci.

Ki bude idanun ko na daina, baxakiyi barci ki barni cikin damuwa ba, for how many long, bakya tausayin bawan Allah nan jiddah?

Dariya ta subulce mata jin yanda yayi mgnr cikin marairaicewa, ta bude idanun tana kallonsa,

Ka gayamin na nawa kayi na biya ka kaga babu sauran damuwa sai ka barni nayi barcina hankali a kwance,

Da tsada nayi kema da tsada xaki biya, ki biyani da soyayyar ki jiddatulmusty, ki shayar dani abinda xai dade a xuciyata bai gushe ba for only today jiddah, ya qara langabar da kansa.

Jiddah taka ce har abada, soyayyar jiddah ka dade da samu tuntuni, babu wani sauran guri da ya rage a cikin xuciyata da ban cike shi da qaunar el'mustapha ba, sai ta tsinci kanta da matuqar jin kunyarsa a yau ta dauke kanta gefe tana murmushi mai bayyana farin cikin dake xuciyarta.

Shi ma yabi ta da wani murmushin da har abada baxai taba gushewa a xuciyarta ba, yabi bayanta a hankali ya kwanta bayan ya soma xuba mata xafafan kiss a ko ina na gangar jikinta.

El'mustapha ya dauke ta ya jefata  a wata duniyar soyayya da ta jima bata je ba, ya mantar da ita rashin lafiyar dake jikinta, ya mantar da ita damuwarta har tana jin kanta kamar jiddah farko mai lafiya, ya rungumeta hannu biyu tare da nuna mata xallar soyayyarsa batare da ya kyamace ta na kasancewar ta nakasashiya ba, ta saka hannuwanta biyu ta rungumeshi sosai kamar xata maidashi ciki saboda so.

*#Asuba ta gari*

*Jiddatulmusty*

Pherty........... ✍🏻

2 days....

Yana dakin jiddah yana shirin fita office kamar yanda ya qudira a yau, tunda aka kwantar da jiddah asibiti bai je ba sai yau.

Ya juyo yana kallonta, tana xaune akan wheel din ta, ta tsura masa ido tana kallon duk wani movement nashi a dakin.

Oh ni el'mustapha, shikenan na xama gwauro komi ni kema kaina andaina min, matata sai dai ta miqe qafafu ta xauna tana kallona.

Murmushi kawai tayi batare da tayi magana ba, ya dawo gabanta ya xauna yana kallonta.

Tun daxu kike bata fuska jiddah, baxan jima ba xan dawo, I know your condition baxan je na barki ba, ya shafi fuskarta yana kallonta,

Me kike so naxo maki dashi? Sai ga hawaye sharrr na bin kumatunta, el'mustapha yaja numfashi ya dawo gabanta ya tsugunna,

Saboda xan fita kike kuka jiddah?, ta girgixa kanta a hankali, ta dora hannunsa akan cikinta,

Ni nagaji da xaman ne, cikin ba dadi duk yanda nayi bana jin dadin sa.

Yace sorry jiddah kin kusa haihuwa ki huta, in kira maki banan ta xagaya dake cikin gidan ko xakiji dadi,

Ta girgixa kanta da sauri,

In kwantar da ke ne, sai kiyi barci kafin na dawo, ta gyada kanta tana kallonsa, yaja keken har wurin gadon ta, ya dauke ta ya kwantar da ita yana kallonta.

Kiyi barci banda tunani jiddah baxan jima ba xan dawo, meeting din ya xama dole ne kinga sai kirana ake.

Ta gyada kanta tana kallonsa, ya sumbace ta yana qoqarin tashi, yaji tana fadin.

Allah ya dawo da kai lafiya,

Yace amin jiddatulmusty, cikin murmushi ya dauki wayarsa da key din sa ya fice bai qara kallonta ba dan yasan xata karya masa xuciya, kamar kada wannan lalura ta same ta duk ta xama rigimammiya bai sani ba ko cikin ne oho.

Tun da ya isa wurin meeting ake ta masa jajen abinda ya sami matarsa wadanda basu sami damar xuwa ba kenan,

Murmushi yayi kafin yace I am soliciting for your kind prayers, my wife was free and discharge, thanks for your concerns, ya xauna.

Sun dauki fiye da awa biyu suna meeting din, duk hankalinsa yana gida binni binni yake kallon time,

Qarar message yaji a wayarsa yana dubawa kuwa yaga jiddah ce,

_Feeling lonely El'mustapha, kaqi ka dawo ni na gaji da kwanciya_.

Jikinsa na rawa ya tura mata,

_on my way, am sorry_!

Ya maida wayar aljihu cikin qaguwa da meeting din.

Fitowarsa meeting keda wuya mutane suka yo masa caaaa abinka da babban mutum mai matsayi,

Menene el'mustapha ya tambaya cikin mamaki yana kallonsu,

Sir yan media ne suka xo, tuntuni suke xuwa basa samun ka, suna so suyi interview da akai akan kidnapping na matar ka.

Ibrahim yace, kuyi haquri yana sauri har xuwa wani lokaci,

Ka barsu el'mustapha ya fada yana kallonsu yana kallon agogon dake hannunsa, minti biyu na baku.

Da sauri suka nufe sa, bayan sunyi guntun bayanin da xasuyi suka soma tambayar sa,

Sir ance anyi kidnapping matar ka, ka ganta? Su waye suka sace ta?

Eh na ganta kuma masu laifin da aka kama suna hannun hukuma sauran kuma an kashe su, shikenan ya tambaya cikin qaguwa?

Sir ance sister din tace ta saka aka dauke ta saboda wata buqata tata daban, wace buqata ce wannan kuma wane mataki ka dauka akanta, harda ita tana hannun hukuma ne ko me?

El'mustapha ya gyara tsayuwar sa yana fadin what I know if you are working on something that you really care about, you don't have to be pushed, the vision pulls you...... Ya fara tafiya, sukayi ruuu xasu bisa yan sanda dake gurin suka hana har sanda ya shiga mota yabar wurin da sauri.

*

Wayyo Allah, Wayyo Hajiyata, Abba kuxo ku taimakeni, wlhy kashe ni xasu yi, na tuba abba ka yafe min.....

Sautin muryar uwani ke tashi dakin da aka rufe ta tare da wasu mata hudu wadanda kusan kullum sai sun axabtar da ita saboda kafiya da taurin kai irin nata.

Duk suka mata magana sai ta maida, idan suka saka ta abu batayi, bata respecting dinsu su kuma basa raga mata ko yaya ne a xamantakewar su.

Yanxu ma daga wurin karbo abinci suke, sun amshe nata sun cinye ta masu mgn suka yi taron dangi suke dukan ta.

Sai da suka mata liga liga su ka barta suna huci,

'Dan ubanki ni xaki gayawa magana akan wani abinci na banxa to an cinye idan akwai wanda xai kwatar maki yaxo kuma yau bake ba cin komai ko kin karbo anjima wlhy baxaki ci sa ba sai dai ki mutu, shegia tsigagiya cewar runkes tana numfashi.

Wadda ake kira da A.j kuwa xama tayi tana numfashin,

Ke har kin isa ki same mu a gidan mu kice xaki mana rashin kunya, yar firit dake haka wannan ko sa'an autan gidan mu kinyi, xan koya maki hankali ne, tasa hannu ta jawo uwani keeeey,

Tashi xaune ki share hawayen nan tun ban nakasa ki ba,

Uwani ta tashi jiki na rawa, ga qafarta sai ciwo take sosai duk da gurin ya warke wajen dukanta suka ji mata ciwo a wurin.

Jikinta sai kyarma yake, ga yunwa dake damunta,

'Dan Allah kiyi haquri anti Aj, karki qara dukana,

Aj ta bige mata baki tana fadin, shegiya mayya inta fara baka haquri kamar gadon ubanta kaci.

Runkes ta xauna batare da tayi magana ba banda hararar uwani ba abinda take.

Ladidi ce kawai ba ruwanta, bata hayaniya da kowa a cikinsu kuma tasha gayawa uwani idan bata gyara ba xasu kashe ta ne a banxa tunda kusan kullum sai sun dake ta saboda taurin kanta.

Ladidi tace yi haquri aj ki kyaleta dan Allah,

Ladidi ki daina tausayin wannan ja'ira yanxu ne kin taimaketa anjima ta fara maki rashin kunya ni maganin ta xanyi.

Babu komai yi haquri ki barta baxata sake ba.

Kinci albarkacin ladidi da sai kin yabawa aya xaqin ta, tashi ki ban wuri sakarya, kuma da kin karbo abincin nan ki kawo shi idan ba haka ba wlhy daren yau baxakiyi barci ba, uban ki xanci a dakin nan.

Ladidi taja hannun uwani suka matsa can nesa dasu kadan, sai dingirsa take, suka xauna

Tace wai uwani meke damun kine tun da kika xo gidannan kwana biyu kacal kikayi kowa ya sanki, ko abinci akaje karba sai kinyi fada da mutane, ayi maki magana kina maidawa meyasa.

Uwani ta share hawayen tana fadin, ke ina ruwanki dani ne, tunda kin gayamin naqi ji basai ki barni ba, idan sun kashe ni miye damuwar ki, ai gwanda su kashe ni na huta da wannan rayuwar dana ke ciki.

Ladidi tayi shiru bata mamakin kalaman uwani ta saba gayamata magana mai xafi fiye da wannan.

Tace uwani gayamin laifin me kikayi aka kawo ki nan,

Sai ke kin fara fadamin naki tukunna, haka kawai kiji sirrina batare dana ji naki ba.

Ba abin damuwa bane uwani, sunana ladidi, inda na fito basai na fada maki ba, mu biyu ne a gurin iyayen mu nida yaya na, akwai wata maqociyar mu mai suna bilkisu bata taba haihuwa ba kuma tana son yara sosai, haka kawai Allah ya dora mata sona a xuciyarta.

Kullum xata je gidan mu ta daukoni, tabani abinci tamin wanka, tana min komai da nake so, kasancewar mijinta yafi iyayena kudi sai suka bata ni a matsayin yar riqo.

Ta riqeni da amana tamkar yar cikinta, tana sona ta sakani a makaranta boko da islamiya, tana min sutura sosai idan kika ganni sai ki dauka itace ta haifeni.

Sai ya xamana babu ruwana da iyayen da suka haifeni sai nafi sati Ma banje gidan ba, su kuma basu damu dani ba tunda ga yaya na.

Girmana na tasowa a lokacin mijin nata ya soma nema na da lalata, wai xai aureni ya jima yana sona tun ina qarama, idan Ma ina so xai iya sakin anti bilkisu ni ya aure ni dan idan bai same ni ba rayuwarsa xata iya lalacewa.

Ban taba jin sonsa ba uwani, ina masa kallon ubana kuma yaya na, ina son anti bilkisu kamar yanda take sona, ban taba ji ko sau daya a rana xan iya cutar da ita ba ballantana har na iya lalata da mijinta ko auren sa.

Matar da ta raine ni tun ban san kaina ba, ta fito dani a mutum,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login