Showing 15001 words to 18000 words out of 138779 words
Chapter 6 - El-mustapha Complete Hausa Novels By Fertymerh Xarah.docx
12, I like your comment 👌🏻
20
'Washe garin ranar sama sama suka gaisa da Hajiya,
'hajiya kiyi haquri bana son fushin ki ko kadan, tunda na taso ban taba fuskantar wannan canjin daga gare ki ba, ki sassauta min fushin ki agareni ba alkhairi bane.
'baxaki taba ganin canjin fuskata har sai kin janye mgnr ki akan uwani ta auri el'mustapha, Sam ban amince ba shiyasa tun farko da ta gayamin daga ni har abbanku ba wanda ya goyi bayanta.
Kallon mamaki jiddah ke mata, ashe Ma tasan da mgnr kenan, tuntuni uwani keson el'mustapha aka boye mata meyiwuwa wannan dalilin ne ya saka har ta kamu da ciwon xuciya bata sani ba.
Kuka jiddah keyi sosai mai taba xuciya wanda kukan yayi matuqar daurewa hajiya kai,
Jiddah saboda na hana uwani ta auri el'mustapha ne kike wannan kukan?
'bana son na rasa uwani ne hajiya, tare muka taso muke rayuwa tare da ita, baxan so ta rasa rayuwarta saboda abinda take so ina da iko akan sa ba, meyiwuwa el'mustapha yana cikin qaddarar mu shi mijin mu ne.
Mijinki ne jiddah ke kadai bana son kibiye uwani Sam ban yarda da ita ba, mahaifinta Ma bai amince da auren ba, tunda kinji xaki iya kije gaki ga uwani ki aura mata abinda kike so a rayuwarki amma bada yawun bakin mu ba, ina roqon Allah ya albarkaci rayuwarki jiddah ya kuma kareki ga duk wanda ya nufeki da sharri, ke yar halaq ce.
Godiya jiddah tayi ita kadai tasan abinda take ji a xuciyarta game da wannan auren, tana tsoron uwani tabi wata hanyar da bata dace ba domin ta mallaki el'mustapha kamar yanda taji tana fada, tana tsoron uwani a yau da komai nata.
Kusan marece suka iso abuja, uwani taxo yi mata barka da dawowa da son jin bayanin iyayenta daga jiddah amma bataga wannan fuskar ba, babu alamar wasa a tare da jiddah tunda suka gaisa bata qara kallon uwani ba, toilet ta nufa domin ta watsa ruwa.
Jiddana ta tafi gida ta dawo amma na rasa gane kanta, bai jira cewarta ba ya fara making love da ita,
Duk abinnan da yake idanun jiddah a lumshe suke tana tunanin watarana fa haka xaiyiwa uwani,
El'mustapha kuwa sosai ya rungumeta wata qila inda hali da ya tsaga qirjinsa ya sanyata ciki saboda qaunarta, mai yiwuwa sannan ne xai xamo contented.
Sai da komai ya lafa ya fahimci jiddah kuka take, kukan da nayi matuqar daure masa kai,
Duk sai ya rikice, kukanta da hawayenta suna matuqar daga hankalinsa
Ya tarairayo ta ya dorata akan qirjinsa, cikin sassanyar murya yake tambayar _did I hurt you jiddah?_, ta girgixa kanta, batasan yanda xatayi masa mgnr ya auri uwani ba domin tana matuqar tsoron abinda xai biyo baya, sai dabara ta fado mata, cikin sheshshekar kuka tace,
Ni dai ka qara AURE...
Sai ya janye jikinsa da nata cikin mutuwar jiki da sagewar gwiwowi, tare da tsananin mamakin jin wannan kalmar daga jiddansa, wani irin kallo yake jifanta dashi,
Kafin in baki amsa jiddah ko nabi umarnin ki ina so nasan dalilinki na son na qara aure?
Saboda el'mustapha ya cancanta ace yana da mata biyu, matsayinsa ya kai, shekaru kusan nawa rabona da haihuwa ya kamata ace su Aryan suna da qanni yanxu kuma nasan kaima kana buqatar hakan,
Ya dade yana kallon kyakkyawar fuskarta a dan hasken farin wata daya keto shara sharan farin labulen dakin, kafin yayi murmushin takaici ya xauna sosai ya bata baya.
Hauwa'u haihuwa ce tasa na aure ki ko kuma tun bayan haihuwar twins kin taba ganin wata alama dana nuna maki ta ina son na qara haihuwa?
Ta girgixa kanta, idan Ma haihuwar ce ke kike baiwa kanki ne? Inaji ko haihuwar ce baki taba yi ba baxaki nemi na qara aure ba ballantana Ma kin haihu,
Ni ina son yarane a ynxu el'mustapha, ina so naga yara sun cika gidannan, shiyasa nake son ka qara aure dan Allah,
Ki gayamin idan twins ba yara bane, baligai ne, yaran dake nursery 2 yanxu sune ba yara ba, wai me kike nufi ne jiddah?
Xatayi magana ya daga mata hannu a fusacce, ya isa... Ya isa jiddah.... Sai ma ya rasa me xai ce mata saboda takaici, dogon tsaki yaja ya dauki wayoyinsa ya bar mata dakin.
Jiddah ta bisa da idanuwanta karo na farko a rayuwar auren su da el'mustapha yayi irin wannan fushin da ita, amma ya xatayi farin cikin su take so, bata son a sanyasu wata hanya da bata dace ba a ruguza masu farin cikinsu ta lura uwani komai xata iya a ynxu da take ganin take takenta,
El'mustapha yayi wannan fushin dan tace ya qara aure ina ga idan yaji uwani ce xai aura?
Dole ta dage ta nuna masa fa da gaske take har lokacin da xai sauko ya amince.
Kwanaki uku suna kan wannan taqaddamar, inyayi fushi sai kuma ya sauko yayi dariya wai jiddah ke son ya qara aure, baisan jiddah ita kanta qarfin hali kawai take ba, tana matuqar axabtuwa da rashinsa kamar yanda shima yake yi.
A rana ta hudu ya kasa jure wannan tsiri da take masa na shariya, dan bashi da wannan juriya ta wannan fannin ta inda take samun weakness din sa kenan, sai ya cafki hannunta ya langabar da kai kamar qaramin yaro, idanuwansa sun juye sun rikide xuwa ja, idan Ma wasa take zai gwada ta shima ya gani ya nuna ko a jikinsa.
Jiddah na baki wuqa da nama, kece mijin kece matar, ki xabo min duk yarinyar da kike ganin ta dace dani don bani da idon kallon wata d'iya mace tun daga lokacin da Allah ya mallakamin ke....
A hankali take dubansa yayin da gabanta ya tsananta bugawa
Ganin yanayin ta, qiris ya rage ya saki dariya amma sai ya cije,
Yace ki nema min niko acikin manya manya qawayenki ne ko riqaqqun yan boko irin su Nabila Mohd,
Haushi ya kama jiddah sosai, ga kishi ga kuma ganin ya maida abin xolaya,
Ya rungumota ta baya ya dora kanshi a kafadunta, a sanyaye yace,
'ko kin daina sona ne jiddah kike neman kai dani? A da ko kallona wata tayi wanda bai maki ba sai kin kwana baki min magana, amma yanxu duk kin daga hankalinki wai inyi aure which means kin gaji dani, kin daina sona, kina neman mataimakiya a yanxu don ki huta, meyasa jiddah, me nayi maki, wane canji kika fuskanta daga gareni domin inyi gaggawar gyarawa?
In gayamiki gaskiya baxan iya sharing kaina ba, ina da kyankyami kin sani, ba kowace mace xan iya hada jiki da ita ba, babu, ban taba ba, kuma bana fata, baxan iya adalciba, ance kuma idan baxaku iya adalciba ku xauna da daya.
Amma inkin gwammace ranar qiyama in tashi da shanyayyen barin jiki, all the same sai na auri Nabila, kinga daganan sai ku qara danqon xumunci abotarku tayi qarfi ni kuma na sami yara da yawa shikenan?
Ta ture shi da sauri duk da jikinta yayi matuqar sanyi da kalamansa domin gaskiya yake fada mata, don shi baya fadin abinda ba haka bane a xuciyar shi don kaji dadi ko dan ya faranta maka, in hakane kenan el'mustapha da gaske xai iya auren Nabila?
Magana take yi a xucci bata san ta fito ba, ya sauka a gadon ya xauna dabas akan carpet, ya dauki hannu ya rafka uban tagumi,
Ni *el'mustapha* na shigesu duk yanda nayi ban yi dai dai ba, to ki fadi yanda kike so ni mijin tace ne.
Idanunta fal da hawaye wai ana wata ga wata,
Yanxu el'mustapha son nabila kake?
Yayi murmushi yana lasar labbansa,
Yaya baxan so taba tunda aminiyar matata ce kuma itace xata riqa bani ya'ya a yanxu.
'ni ba wannan nake mgn ba,
Ya miqe tsaye yana fadin koma wane iri kike magana shine, yarinyar nan rikicinki ya isheni, son ta nake na soyayya wanda ake soyewa kiyi k'uli-k'ulin kubura dani ko kiyi ta kuka har hawayen ya qare....
Duk da kuka take batasan sanda tayi dariya ba, ganin ya dawo ya rungumeta yasa ta biye masa.
She have no choice banda ta rungumi mijinta mai sonta mai qaunarta, ta nuna masa sonsa kadai ne a xuciyarta.
My wattpad phertymerh1
*EL'MUSTAPHA*
*Haske Writers Association*
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
*
21
2 days......
Banan yau kinje makaranta kuwa?
'banje ba anti jiddah,
'meyasa baki je ba,
Ta soma inda inda cikin fargaba, dama.. dama anti uwani ce ta hanamin xuwa yau.
'akan wane dalili?
'ta bani kayanta ne na wanke bayan na shirya xanje makaranta, na roqi ta bari har na dawo na wanke shine taqi, makarantar ma tace baxan je ba.
'kira min uwani, banan ta tsorata ta xaro idanu,
'Anty jiddah kiyi haquri, xata ce nakawo karar tane gunki dukana xatayi.
Jiddah bata kula ta ba, ta daga murya tana kiran uwani kusan sau biyu kafin ta amsa,
Ta fito da sauri harda wani russunawa,
'Anty jiddah naji kina kirana,
'akan wane dalili xaki hana banan xuwa makaranta?
'aiki na sakata anty jiddah taqi tayi saboda ta raina ni.
'wannan ba hujja bace uwani, ban taba gayamiki kowacece banan bane, marainiya ce bata da iyaye, kakarta ta kawo amanar ta tayi aiki a gidan nan, kuma kina gani lokaci lokaci tana xuwa duba ta, kasancewar ta marainiya yasa na saka ta makaranta domin ta sami ilimi da xatayi alfahari dashi watarana, ina son maraya kuma bana so naga an takura maraya duk mai yin haka baxan xauna inuwa daya da shi ba, ba banan kadai ba duk masu aikin gidannan, babba da yaro har tsofaffin ina lura dake ba wanda kike ragawa, duk cikin su ba wanda ke qarqashinki ko kike ciyarwa game da takurasu da kikeyi kada ki sake, kuma daga yau kada ki sake baiwa banan wankin kayanki, akwai washing machine idan baxakiyi da kanki ba kibari.
Uwani ta hadiye wasu yawu da kyar yayin da wani qololon baqin ciki ya taso ya tokare xuciyarta, baa taba wulaqanta ta ba kamar yau kuma wai agaban shegiyar nan banan, idan ta xamo matar gidan ta hana mata iko dasu, wlhy ta ja masu, amma tunowa da tayi ita ke nema yasa ta qara russunawa hade da kwantar da muryarta,
'Allah ya huci xuciyarki anty jiddah insha Allah xan kiyaye, ta juya tana kallon banan kamar da gaske, banan kiyi haquri nima ina son maraya a xuciya na.
Jiddah ta dube ta tana fadin, xo ki cigaba da gyaramin salad din kafin abokan wasar naki su dawo,
Banan ta xauna cikin farin ciki, uwani kuwa ji take kamar ta shaqe ta ta huta, ta qara matsawa kadan yanda banan baxata ji taba.
'Anty tunda kika dawo nake xuba kunnuwa naji mesu hajiya suka ce game da mgnr amma kinyi shiru shiyasa har na kasa jurewa nake tambayar ki a yanxu.
Kallonta jiddah keyi cike da mamaki,
'Na tambayeki uwani, ta gyada kai tana kallonta.
'ki gayamin tun yaushe kika fara son el'mustapha,
'wlhy anty na fara sonsa tun ranar dana fara ganinsa, sonsa nake tsakani da Allah da xuciya daya ba dan na cutar dashi ba ko na cutar dake anty kinsani kuma nasan ke baxaki cutar dani ba kasancewar yar'uwa a gareni dan 'Allah ki taimakamin anty.
'taya xan taimakamiki bayan iyayen mu basu amince ba, Yusuf suke so ki aura ba el'mustapha ba.
'ashe har wadanda suka haifeka xasu iya Ma baqinciki a rayuwa? Ta fada a xuciyar ta batare da ta furta a fili ba.
'bayan wannan, ashe xaki iya xaman kishi dani, xaki iya auren mijina ina raye bawai mutuwa nayi ba, meyasa kike son mijina uwani, meyasa kike son rusa min farin cikina, kinsani da xuciya daya nake sonki, xaman ki da Yusuf xai fiye maki farin ciki akan auren ki da el'mustapha domin baya sonki kuma baxai taba qaunar kiba.
Uwani ta soma kuka haiqan, dan Allah kibar mgnr iyayen mu ko bada su ba xan iya aure, a yanxu ke kike riqo na kuma xaki iya auraddani, batun cutarwa kinsani baxan iya cutar dake ba nima da xuciya daya nake son ki, ni nasan yanda xanyi el'mustapha ya soni koda kwatar son da yake miki ne anty jiddah, kuma baxan taba jin haushin soyayyar da yake maki tunda na riga na jima da sanin ta tun kafin na aure sa, dan Allah ki aura min el'mustapha anti jiddah, 'shine farin cikina, shine rayuwata, ki ceci rayuwata xan iya mutuwa a kowane lokaci idan ban same sa ba, banyi niyar gaya maki ba saboda kada hankalinki ya tashi tun jiya da dare nake fuskantar wani irin tari dake sani xubar jini xuciyata tana min nauyi da kyar Ma nake numfashi.
Sosai hankalin jiddah ya tashi, ita dai a rayuwarta tana da tausayi da kawaici da hakan uwani kecin galaba akanta.
Innalillahi wa Inna ilaihir raji'un, dama likita yace kin kamu da ciwon xuciya, shine har kin fara aman jini, subhanallah meyasa uwani kike son rasa rayuwarki saboda abinda baki da iko akai, idan ni na amince ki auri el'mustapha shi kuna yaqi ya xakayi.
'Anty ke xaki sa ya amince, nidai ko shekara daya ne ya aureni dai dai lokacin xuciyata ta sami sauqi sosai akansa, wlhy anti na amince nayi auren shekara daya dashi kice ya sakeni baxan damu ba.
'mutumin da kike so kamar ki mutu har kina son a rabaki dashi auren shekara daya kacal uwani ina son da kika ce kina masa.
Uwani ta daburce ta soma inda.. Inda.. anty ko auren kwana biyu ne ina so ko ba komai burina ya cika na xama matar wanda nake so a rayuwata, wlhy baxan tabbata da mijinki ba kibani shi na shekara guda xan bar mikishi na nesan ta kaina dashi, ina so na sami sauqin ciwon xuciyata na warke daga cutar da ta kamani.
Jiddah taja numfashi, tana maimaita mgnr auren shekara daya uwani, idan kika aure sa bayan shekara daya mutane sukaji ya sake sa so kike a xargeni? Idan hakane ki haqura dashi.... Kafin ta qarasa uwani ta duqe gurin hade da dafe qirjinta tana Jan numfashi sosai tana daukewa, ta kakkafe idanuwanta kamar da gaske mutuwa xatayi wanda yayi matuqar ruda jiddah harda banan Ma dake saurarensu,
Jiddah ta soma jijjigata tana kiran sunan ta da qarfi wanda ya janyo hankalin mutanen gidan gare su harda securities din Ma,
Duk aka kewaye su tuni jikin jiddah ya fara rawa ta soma kuka sosai, banan taxo da ruwa ta kwarara mata, ta sauke wani numfashi da kyar tana fadin,
Wayyo qirjina, ku taimakeni mutuwa xanyi, anti jiddah xan mutu, wayyo anti jiddah.
Wani dan sanda a gurin yace, hajiya bari aje da ita asibiti xaifi tunda qirjin nata yana ciwo haka.
Jiddah ta share hawayen ta tana fadin to shikenan, ku kamata ku saka ta a mota kuje, duk abinda aka nema kai sai kayi ni baxan je ba.
Tana tsaye gurin aka fita da ita, ta tausayawa halin da uwani take ciki ciwon so bala'i ne hardai mai tare da ciwon qirji, allah ka baiwa yarinyar nan lafiya ka sassauta mata wannan ciwon, tasan ba laifin uwani bane na son mijinta, laifin sone da baya tunani sai dai kaji sa farat lokaci daya, idan har cutar uwani xata warke na tsawon shekara daya ta amince da auren ta da el'mustapha na tsawon shekara daya tare da yarjejeniya.
El'mustapha tare suka dawo da su arham yaje ya daukosu inda mama, rungume ya'yan tayi tana farin ciki, suma haka ne a gurin su sunyi missing mamin tasu sai faman surutu suke xuba mata.
'Angon jibi kaxo mu fara tattauna kan maganar mu fa,
Kallonta yayi yana xare safar qafafunsa,
'Uwargidan el'mustapha me kike so mu tattauna akai, idan nabila ta amince nima na amince dama xan dauki Hutu kuwa yanda xan angwance da kyau.
Murmushi jiddah tayi cikin qarfin hali tare da danne kishinta.
Tace Uwani bata da lafiya anje da ita asibiti, yanxu ta kai uwani har aman jini take yi, abinda uwani keso ina da iko akansa kuma ina son na inganta rayuwarta, ka taimakeni el'mustapha kada ka bani kunya,
'ina jinki jiddatulmusty kome kike so xaayi, me uwani ke so kudi ko me?
Kai... Kai.. take so el'mustapha, auren shekara daya ne, akwai yarjejeniya akai ku...... tayi shiru sakamakon wani kallo da el'mustapha ya jefe ta dashi sai da tayi suman xaune.
Pherty........ ✍🏻
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
22
Kallon Aryan da Arham tayi hade da fadin, kuje inda banan yanxu xan fito nima, duk mgnr da takeyi jikinta rawa yakeyi tun daga kallon da el'mustapha yake mata.
Suna fita ta juya tana kallonsa cikin marairaicewa,
'Dan Allah el'mustapha kada kaqi... Shut up pls ya katse ta cikin tsawa,
'wai me kike nufi ne, me ya same ki, kinsan me kike fada, na auri uwani, akan wane dalili, ni el'mustapha na auri uwani, lallai yau na saka ki cikin jerin mata marassa hankali da wayo, idan har wasa kike kada ki qara kwatanta min irin wannan wasar domin baxakiji dadina ba, ya tashi a fusacce ya bar falon xuciyarsa na tafarfasa.
Kuka take yi sosai, kukan da bashi da mafita illah ta cigaba da convincing el'mustapha har lokacin da xai yarda da auren, su taimaka su ceci rayuwar uwani dake kwance a asibiti tana fama da ciwon qirji.
Binsa tayi dakin, bakin gado ta xauna tana jiransa har lokacin da ya fito wanka, da sauri ta qarasa gabansa kafin yayi wani yunquri ta