Showing 51001 words to 54000 words out of 186400 words
Chapter 18 - ATSAKANIN SOYAYYA COMPLETE By Maman Shakur .txt
hancin ta yacire ya ijiye agefe yana kallon fuskarta, idanunta sun cicciko da hawaye har ganin kanshi yake ta hawayen tsabagen yanda suke shining kaman madubi, kwanto da kanshi yayi slowly yana wani irin kallonta kaman da idanu suke communicating yadaura forehead dinshi akanta tareda cupping face nata yana kallon hawayen dake zubowa daga gefen idanunta, dan lumshe ido yayi kafin yabude su ahankali ya zuba mata dara daran eyes dinshi, murya chan ciki yace "am sorry, I yelled at you the other day, am sorry Aneesah na, am so sorry please forgive me, what can I do to erase the memory from your heart?" yadanyi shiru tareda sake lumshe ido yana sauraran yanda numfashi ta ke sauka kan temporal bone dinshi kafin ahankali yasake bude idanun yazuba matasu, bakinta ne ya shiga motsi tanaso tamai magana yadaga ta, lips dinta suka shiga rawa kaman wacce aka jonama electric shock, kafe pink lips din nata da ido yayi dat are so pinkish barin ma yanzu datake zaxzabi sai suka kara zama pink sosai jiyayi numfashinshi na neman daukewa the way her lips are doing looks damn sexy and tantalising, gently ya manna nose dinshi kan nata yana breathing heavily kaman akwai wani magnetic force that's pulling him towards her lips, lumshe ido yayi da sauri a wani irin hankali kaman matsoraci yadaura lips dinshi kan radiant tender lips dinta dat are so warm sabida zazzabin datake yi.
[14/03, 18:37] Aishat Muhammad: _*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_
_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤
_✍🏿M Shakur_
2️⃣6️⃣
Wuraren biyar na yamma wayar Ammi tai ringing ganin Baffa ne yasa tai picking da sauri tace "to bari nafito" katse wayan tayi ta kalli Aneesa dake bacci ana mata karin ruwa ta zura talkamta tana gyara hijabi tawuce tafita, a reception din asibitin tagansu Baffan Aneesa dakuma dayan Baffan kawu Sani tsaye suna kalle kalle, suna hango ta suka taho itama tana tahowa tsayawa duk sukayi bayan sun iso tace "sannunku da zuwa, kunsha hanya, muje" tai gaba suna biyeda ita har dakin da aka kwantar da Aneesan shiga duk sukayi Baffa da sauri yakarasa gaban gadon yana kallon Aneesan gidansu su uku maman su ta haifa shine Babba sai mahaifin Aneesa dasuke kira da mai Kwato saikuma Sani autan su dasuke cema Na Sani, dasuka taso mahaifin Aneesa shi Allah yafima arziki danshi harkan gona yake yana noma sosai yanada gonaki sunfi goma sha biyu, idan yay aikin gona ya sayar da amfanin gona saiya saro shanaye yana bashi yana tayashi kiwo duk yaran da matayen shanun zasu haifa na shine yace yabashi haka suke rayuwan su suna rufama juna asiri haryazo ya auro Ammi, Ammi batada iyaye sun rasu tun tana yarinya a hannun kakan ta ta taso, bayan wata uku da bikin ta kakanta tarasu itama, shekara daya da aurensu Ammi ta haifi yarta mace kyakkyawan gaske dayasa mata suna Fateema sunan maman mahaifiyar kakansu kenan, sai ana cemata Aneesa, Aneesa nada shekara biyu aduniya wata rana yaje gona maciji ya sareshi shinefa yadinga ciwo dudda an zuke dafin macijin sai ciwon yadawo babban gaske akace yanada ciwon sugar ne saisa yaki warkewa, haka ciwon nan yadinga cin kudi yadinga cin kudi, saida aka saida gonakin shi kakap aana maganin turenchi ayi na hausa amma ba'a ganin chanji duk ba'a daceba kafin Allah yazo ya amshi ran abinshi, bayan yarasu babu yanda basuyi da Ammi ba sutafi da ita kaduna chan family house amma Ammi tace ita bazata bisu kaduna ba, basu takura mataba suka barta a gidan har Aneesa tai shekara biyar Baffa yazo zai karbe ta dan kyan ya mace ta tashi akulan mahaifi amma Ammi tace bazata bayar ba, babu yanda basuyi da ita ba taki basu ko ranan nan maganan dayazo mata kenan zai tafi da Aneesa amma taki yarda harda kukan ta wai mesa sukeson rabata da yarta.
Addu'a yagama tofama Aneesan dake bacci ya juyo ya kalli Ammi yace "ai yanzu hankalin ki ya kwanta ko Maman Fateema? Yarinya babu wuyan duniya dabaki bata, yau tana kasuwa, gobe tana gidan chan yin lalle, wanchan garin yin lalle, ketai aiki takawo miki kudi, kaganta tana shagon chan tana shagon nan, babu kalan Iskan duniyan nan da yarinyar nan bata shaka, ba baki barin yarinya tahuta ya za'ayi bazatai rashin lafiya be eh? An gayamiki ita injin ce?" da sauri Kawu Sani yace "ya isa Yaya yanzu ba lokacin fada bane muna asibiti" cikin fushi Baffa yace "sai anyi fadan, ka barni nafada mata gaskiya tazaci tsoronta akeji, ni uban yarinyar nanne" ya nuna Aneesa dake kwance kan gado yace "ni mahaifin tane, duk duniyan nan a yanzu babu wanda keda iko da ita kaman ni, koko idan aka barki da ita zaki iya aurar da ita ne iyye?" ya tambayi Ammi cikin fushi, yace "tabani yarinya natafi da ita kaduna ta shiga cikin yan uwanta su Rukkaya, da Asiya, da Maimunatu amma taki koko ance miki idan natafi da Aneesan cutar da ita zan dinga yi ne kokina ganin zan zauna nabude ido ina gani ana cutar da Aneesa agida nai shiru ne? Ballema nasan inhar ina raye babu wanda ya isa ya cutar da ita" dan shiru yayi yana kallon Ammi data saukar da kanta kasa yace "wlh kawai banson na tauye miki hakki ne, amma inhar baki shirya kula da yarinyar nan da hannu bibbiyu ba karbanta zanyi kome zai faru yafaru kina jina" dan murmushi Ammi tayi aranta tace "maza kenan su kullum gani suke baka kula da yara da kyau" kujera Baffan yaja yazauna shikuma Kawu Sani yazauna abakin gadon, dago kai Ammi tayi ta kallesu dan murmushi tayi koba komi Baffa tsoho ne kuma yayan baban yarta ce dole tabashi hakkin shi tasan ya isa da ita bawai bai isa bane kawai bataso ya karbe mata abu daya datake gani taji dadi ne aduniya, ahankali tace "kayakuri Baffa, kuyakuri dan Allah, zan kara kiyayewa" shiru yayi baice mata komiba ahankali tace "akwai abinci Baffa nazuba muku" girgiza kai yayi tareda saukar da ajiyan zuciya yace "kibari muyi magriba tukunna, inane ofishin likitan muje maganshi musan nawa zamu biya?" "kana fita ka mike gun zakaga ofishin" kallon sani Baffa yayi yace "kaimuje sabida kome aka rubuta ka karantomin naji" tashi yayi suka wuce suka fita koda sukaje wajen likita cemusu yayi wanda yakawo su jiya asibitin yabiya kudin komi addu'a suka dingamai su Baffa, Dr yace karma suji komi anjima zaizo zasu ganshi saisumai godiya atare duk suka wuce masallaci danyin sallan magriba.
Shigowa sukayi dakin harda likita har lokacin bacci take, Baffa yace "likita wanan baccin baccin lafiya ne daiko" dan murmushi Dr yayi yana zuba wani allura a drip din yace "eh na lafiya ne, wanan ruwan da ake karama ta shike sata wanan baccin shizai sa magun gunan subi jikinta" "to masha Allah" bude kofan da akayi yasa daukan su harda Ammi duk suka juyo suna kallon kofan, Dady ne sanye da manyan kayan dake jikinshi tunna safe sai bodyguard dinshi daya dake biye da shi yariko manya manyan ledoji bin kowa na dakin Dady yay da kallo kafin yakara so ya babbasu hannu suka gaggaisa ya kalli Ammi dake gaban gadon yace "yamai jiki bacci takene" gyadamai kai Ammi tayi ta kalli su Baffa tace "Baffa kutaya mu godiya shiya kawomu asibiti shiya taimaka mana" ta kalli Dady tace "Alhaji ga kawun nin Aneesa daga kaduna suka zo yau" kafin ma Dady yay magana Baffa yakara bashi hannu suka gaisa yace "angode, angode, angode, munji duk abinda kamana daga bakin likita, ubangiji Allah yasaka da alkairi bamu da abin biyanka saidai muna rokon Allahu Subhanahu Wata'ala ya sakamaka da alkhairi" murmushi Dady yayi yace "kudena godemin dan Allah inda ace d'ana baida lafiya koyana neman taimako na tabbatar zaku taimaka mishi kuma ai koba hakaba?" da sauri Baffa yace "maganan ka gaskiya, zamu taimaka mai, ai shi d'a dakake gani nakowa ne, Allah dai ya shirya mana su sanan ya raya mana zuri'a yakare yakuma tsare mana su" atare duk sukace Ameen, Dady ya kalli Ammi yace "tom saida safe, agaidamin da y'ata inta tashi" dan murmushi Ammi tayi tace "Allah yasaka da alkhairi mun gode da dawainiya" Dady ya kalli Baffa da Kawu sani yace "bismillah Alhaji" da sauri Baffa yace "to, to, to, bismillah muje" bude kofa Dady yayi yafita Baffa da kawu sani suka bishi a baya har zuwa wajen asibiti, wani eatry Dady ya shiga suna biye da shi suka zauna kan table, Dady yace "meza akawo mana Alhaji" hannu Baffa yadaga yace "masha Allah akoshe muke, mungode" murmushi Dady yayi still yasa aka kawo musu drinks sanan ya gyara zama yace "masha Allah inamai tsananin farin cikin ganinku ayau, da farko dai sunana Alhaji Muhammad Ibrahim Darham, ina aiki amatsayin senate president of Nigeria, matana uku sanan yarana ashirin, namiji daya gareni wacce matata tafarko wacce Allah yama rasuwane ta haifamin shi" atare Baffa da kawu sukace "Allah yamata rahama" "Ameen, Aliyu sunan yaron saikuma sauran yarana mata, bazan muku karyaba Jiyan nan nafara ganin mahaifiyar Aneesa wuraren sha biyun dare wanda nafi yarda kaddara ce yahada mu dan bancika yin dare a anguwan hakaba na taimaka mata mukakai Aneesa asibiti, Alhaji" yakira Baffa ahankali, amsawa Baffa yayi yace "na'am Alhaji Muhammad" dan murmushi yayi yace "muba yara bane munriga mun manyanta munyi kwana biyun, tun ajiyan dana fahimci kaman mahaifin Aneesan yarasu ne naji mahaifiyarta ta kwanta min arai ainun inata tunanin yanda zan bullowa al'amarin sai gashi kicibus Allah yahadani daku yau kaga yanda Allah ke abunshi ko" yafada yana murmushi yace "da izinin ku amatsayin ku na yan uwan mahaifin marigayin mijinta nakeso inhar kun yarda inason mahaifiyar Aneesa so na aure, auren sunna, kuma karkuji komi Aneesa nariga na dauke ta amatsayin ya inada yara mata guda goma sha tara karata cikin yarana su zama ashirin abin alfahari ne agareni, wanan ce daman maganan danake so namuku da fatan banyi laifi ba bankuma yi karambani ba" washe baki Baffa yayi murmushi fal fuskarshi yace "masha Allah, masha Allah, Alhaji Muhammad ina cikin tsananin farin ciki da wanan batu naka badan komi ba dan shi auren nan dakake ganinshi rahama ne sanan rufin asirin y'a mace ne, tun Fateema na yar shekara biyu mahaifi ta yarasu amma mahaifiyarta taki yarda tai aure, bazan boye makaba banji dadin yanda take rayuwa daga ita sai Aneesan, banji dadi sabida Aneesa yanzu ta tasa wata rana dole tai aure idan tai aure haka takeso ta cigaba da zaman kadaici? Aisai wani ciwo yakamata, abinda za'ayi shine zan sameta da maganan nan yau yau dinan kome tace zan sanar dakai gobe dan zanso ayi auren kafin nakoma kaduna to anriga an girma me za'a wani daga biki kaman bikin yara? To kagani dazaran ta yarda ana sallaman Fateema daga asibiti gobe ko jibi zamuje masallaci adaura auren, zaman su gida su kadai hadari ne gwara yanzu dazaran tadawo karkashin ka saika killace ta nima hankalina zaifi kwanciya nasan cewa na sauke nauyi na lura sanan nakula da iyalin kanina nabada matar shi aure gun kamilin namiji, sanan abu na karshe dazan fadama Alhaji Muhammad shine nayaba da hankalin ka dakuma mutuncin ka yasa kaga na amsa maka maganan nan siteret, dan haka karike amana, karike su amana, kai babba ne, kanada yara mata ka rike Aneesa da mahaifiyarta amana, idan Aneesa na rashin ji kotama badaidaiba ka kirani ni dinan zanzo har gida na lallasa maka ita, ina kuma rokon Allah daya sanya alheri da albarka ciki, mahaifiyar Aneesa kuwa karka damu zamu shawo kanta" murmushi sosai Dady yayi kaman anmai kyautan Aljanna yace "nagode Alhaji, in sha Allah bazaku taba samuna dacin amana ba" murmushi kowa yayi suka mimike bayan Dady ya biya kudin suka fito daga wajen Dady yamusu sallama yatafi.
_*duk wacce takaranta min littafi batare data biyaba, Allah ya isa, idan kinason book dinan chat me up 07012181461*
[14/03, 19:27] Aishat Muhammad: _*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_
_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤
_✍🏿M Shakur_
2️⃣7️⃣
Saida suka fara tsayawa sukai isha'i sanan suka shiga asibitin, sallama sukayi tareda bude kofan dakin har lokacin Ammi na zaune kan kujera tana kallon Aneesan, zama sukayi abakin gadon sunama Ammi sannu, ahankali Ammi tace "nakawo abinci Alhaji?" girgiza mata kai Baffa yayi yace "bari tukunna yanzu akwai maganan damuke so muyi" dan gyara zama Ammi tayi tace "to Baffa" dan shiru Baffa yayi saikuma yace "Maman Aneesa tsawon wanan shekarun damukai tare tun ina miki kallon matar kanina yanzu kallon kanwata na jini nake miki wacce nakeda iko da ita koba hakaba?" gyadamai kai Ammi tayi tace "hakane Alhaji" gyadakai Baffa yayi cikin nuna gamsuwa da amsan data bayar yace "tsawon wanan shekarun dakika nuna kezaki rike Aneesa bazaki bamu itaba dudda naji haushi amma ban takura mikiba, kikazo kikace ke zaman rainon yarki zakiyi bazakiyi wani aure ba shima ban takura miki ba na barki, ayau nakawo miki wata babbar magana da bazan boye mikiba sonake yau kibani girmana a matsayina na mahaifin yarki sanan waliyinta, kimin biyayya sanan kisani kome nakeso nayi abu mai kyau ne agareki sanan abinda zai ban kwanciyan hankali ne kinajina" gyadamai kai Ammi tayi ahankali gabanta nadan faduwa, dan shiru Baffa yayi yana kallon fuskarta ganin yanda ta natsu duk tabashi hankalin ta tana sauraronshi yasa yace "sonake kiyi aure maman Fateema" da sauri Ammi tadago kai ta kallai cikin wani irin yanayi na damuwa tace "aure Alhaji?" "e, aure maman Fateema nakeso kiyi, aure rufin asirin mace ne, yarinya dake duka dukan ki nawane da zaki ce zaki zaune ahaka ke bazakiyi aureba zaki dinga kula da yarki ne angayamiki hakan zaiyu ne? Banda ma haka amusulunce hakan baida kyau, kin taba tunanin yanayin da zaki shiga duk randa zaki aurar da Fateema kiyi watanni shekaru baki ganta ba kintaba tunanin yanayin da zaki shiga yanda zakiyi coping?" shiru Ammi tayi tana kallonshi takasa magana, dan murmushi Baffa yayi yace "to kingani, gwara kiyi aure duk randa zatai nata auren kina gidan mijinki karkashin mijinki akwai wanda zai dinga debe miki kewa kinajina" gyadamai kai Ammi tayi ahankali, murmushi yasake yi ganin batamai gardama ba, ahankali yakira sunanta "Maman Fateema" ahankali tace "na'am Alhaji" anatse Baffa yace "Alhaji Muhammad Ibrahim wanan mutumin daya taimaka miki yakawo Aneesa asibiti dazu yasame mu da wata magana da tamin dadi ainun, ya nunamin shi daga ranan daya fara ganinki yaji yana matukar sonki ainun" wani irin murmushi Aneesa da tun dazu dasuka fara magana yatashi tayi cikeda jin dadi, da sauri Ammi ta kalli Baffa, gyada mata kai Baffa yayi yace "inaso kiyi tunani sosai bazan takura miki ba, gobe nakeso kibani amsa kuma ko kadan banso adau lokacin dazaran an sallami Aneesa za'a daura auren dan zanzo mu daura auren kafin mubar garin nan, Inaso ki natsu kiduba lamarin da kyau, kuma namiki alkwari gobe ni nan da Na Sani zamu fantsama garin nan muje muyi binciken halinshi inmun dawo zamu fadamiki maimuka gano sanan saimuji amsan ki saimu kirashi, inamiki kwadayin aure sosai, so kiyi tunani kinji karki takura ma kanki, Allah ya sadamu da alkhairan shi" gyadamai kai Ammi tayi ahankali tace "Ameen" murmushi yayi yace "to bamu abincin muci mutafi" plate tadauka ta zuba musu tavasu sunaci ana hira sama sama saida suka gama sanan suka mata sallama suka tafi.
Tagumi Ammi tabuga tana tunani sosai sai hango fuskan Dady take, dan motsin da Aneesa tayi yasa tadago kanta ta kalleta ganin idanunta abude yasa ta tashi da sauri tareda daura hanunta kan goshin Aneesan tana murmushi tace "Aneesa na kin tashi zakiyi fitsari nakaiki bayi?" girgixa ma Ammi kai tayi tana murmushi, murya chan kasa tana lum lumshe ido tace "Ammi ki yarda ki aureshi ni inason shi wlh, inason Abba Ammi, please ki yarda kinji" Aneesa tai maganan tana murmushi sosai baki Ammi tabude cikeda mamaki tana kallonta tace "ke, so dama idanunki biyu kinajin duk abinda muke cewa ko" gyadama Ammi kai tayi tana murmushi sosai tarike hanun Ammi tace "Ammi please kinji ki yarda, dan Allah" hararanta Ammi tayi tace "Common kimin shiru anan, zakiyi fitsarin ko bazakiyi ba" turo baki tayi tace "ni banaji, kuma inyazo gobe sainace mai Ammi na ta yarda su Baffa su daura auren" haba Ammi tarike tana kallon Aneesan cikeda mamaki tace "kaman rashin lafiyan nan yasamiki rashin jine ko Aneesa wanan magana haka" dan murmushi Aneesa tayi tace "inda ni namiji ne dani zan badake Ammi" daka mata duka kadan Ammi tayi acinya hakan yasa tafashe da dariya sosai Aneesan tana safe kanta dake mata ciwo Ammi tace "ahh lallai lafiya tasamu, zanci gadanku ne" rungume cikin Ammi tayi tace "please Ammi na ki yarda kinji for me Ammi na, ni inason shi" shiru Ammi tayi tana sauraron ta kafin tadan sauke ajiyan zuciya tace "to shikenan, zanyi tunani in sha Allah" matseta Aneesa tayi tace "yauwa Ammi na, my Ammi najin magana ta, my Ammi is a good girl" dariya sosai Ammi tayi tana shafa kanta tace "Allah shirya" haka suka dinga hira kasa kasa harta sake komawa bacci.
[15/03, 13:07] Aishat Muhammad: _*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_
_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤
_✍🏿M Shakur_