Showing 144001 words to 147000 words out of 186400 words
Chapter 49 - ATSAKANIN SOYAYYA COMPLETE By Maman Shakur .txt
ya matukar tashi tace "Aliyu me haka, me amfanin satoni dakayi? Baka da lafiya, ina zaka kaini eh? U are risking our lives, Aliyu dan Allah ka komar dani gida kar hankalin Ammi yatashi" dudda yanajin kukanta har zuciyan shi amma ko kala baice mataba harsukakai garin zaria yadauki hanyar gidan sarkin zazzau.
Harsuka kai gidan sarkin zazzau Aneesah kuka take, dogarawa ne suka tare motarsu agaban Gate din shiga cikin gida hakan yasa yay wining glass down, dogarin dake sanye da jan malummalum ne yazo yana leka motar yace "kai samari wakake nema kanada appointment ne koko bakasan gidan sarki mai daraja kake ba?" lumshe ido yayi ahankali sanan yabude, ahankali yace "acema mai Martaba Aliyu Ibrahim Muhammad ne, dan gidan senate president of Nigeria" yafada authoritatively, tsayawa chak dogarin yayi yana kallonshi kafin da sauri yace "gyara parking bari ashiga asanar dashi" yay maza yajuya daya daga cikin dogaran dasunkai goma awajen yaje yasama yamai magana a kunne da sauri dogarin yay cikin gida, parking Aliyu yayi agefe yanajin yanda take kuka har lokacin batare data dago kanshi ba dudda kukan natabamai zuciya amma baice komiba, lumshe ido yayi ya jingina da kujera ko kadan baida lafiya, almost 15min suna ahaka yaji anyi knocking tinted glass din motar nashi yaja glass din kasa, cikeda girmama wa dogarin haryana dan dukawa yace "angaishe ka yaron manya jikan manya, dan gidan hutu marika nijeriya kasarmu, Mai Martaba yace amaka iso zuwa fada, shigo da motar" kunna motar Aliyu yayi ahankali yaja motar cikin gidan sarkin, gidan kaman wata kasa tsabagen kyau da girma, parking yayi a inda ake parking yabude mota yafito dogarin na jiransu daga gefe, zagayowa ta inda Aneesah take yayi yabude kofar har lokacin kanta akasa, ahankali ya tsugunna ta wurin murya chan kasa ta yanda dagashi zai ita zasuji yace "tashi mu shiga ciki if not I will carry you a kafada na wlh" yitayi kaman batajishi ba hakan yasa yace "okay" tashi yayi ahankali tsaye yana tattare hannun riganshi yadaura hannunshi daya kan bayanta daya tawajen kafafunta zai dauketa da sauri ta tashi tana goge hawaye tana hararanshi da idanunta dasukai jajir duk hawaye yabata kwaliyan da akamata tace "wlh katabani saina wanka maka mari" murmushi yayi ahankali murya chan kasa yace "okay let's go in bakiso" fitowa daga motan tayi azuciye kaman zata bugeshi kamshin datake yi yawani bugi fuskarshi ahankali yamaida kofar yarufe yana binta da kallo, yakaraso inda take tsaye hannunshi yamika ahankali yakama hannunta ya rike ya kalli dogarin dake jiransu yace "muje" bugemai hannu tayi cikin kuka sosai amma yaki sakinta, ganin tafaramai gardama zatamai rashin kunya yasa yace "wlh zan dagaki, let's go" binshi tayi tana goge kwalla har aka kaisu durmemen fadan sarki dayaji kayan adon sarauta, wasu fadawa ne aciki, da kuyangu saikuma Sarkin Zazzau daya manyanta sosai danya tsufa tukup dake zaune kan kujeran sarauta yana kallonsu ga wasu bayi guda biyu dakemai fifita, faduwa kasa dogarin yayi yace "taakawanka lafiya sarkina sarkin zazzagawa, sarkin sarakuna, gashinan anshigo dashi" da kai sarki yamai alamu daya tafi hakan yasa yatashi yatafi, duk kukan da Aneesah take suna hada ido da sarkin tahadiye kukan tsaf dan gabanta ya mugun fadi, ahankali Aliyu yadan dukar dakai ya daga hannunshi. "barka da warhaka mai Martaba" gyadamai kai sarki yayi kafin ahankali cikin muryanshi na wayanda suka manyanta sosai yace "Aliyu, ina mahaifinka? Meke tafe dakai haka kwatsam kaman anjehoka? Wacece wanan atare dakai dake kuka haka?" yay maganan yana kallon Aneesah datama kasa magana sai goge kwalla take kanta akasa, cikin dakewan zuciya Aliyu yace "satota nayi Mai Martaba, yaune bikinta" shiru Mai Martaba yayi yana kallon Aliyun yanda idanunshi sukai jajir kallo dayama yamai yagane baida lafiya, sanan yasake kallon Aneesah, cikeda fikra irin na wayanda keda ilimin rayuwa yace "meke faruwa tsakanin mu biyun nan" ajiyan zuciya ahankali Aliyu ya sauke yace "sonta nake mai Martaba, itama kuma tana sona, iyayen mu sun sami matsala dake neman kawo nakasu a soyayyan mu dan aurar da itama yau zasuyi, bazan iya jurewa ba na shirya nai shigan mata naje na sato ta, nakawo ta nan dan kama soyayyar mu adalci da abinda yakamata" Aliyu yakarashe maganan ahankali yanadan taba kirjinshi dayakeji kaman zai tsage, ganin yana fama da ciwo yasa Mai Martaba bai cemai komiba yana kallon yanayin shi har na kusan minti hudu saida yaga yajanye hannun daga kan kirjinshi sanan yakira sunanshi cikeda natsuwa. "Aliyu, yimin magana da kyau, kafadi iyakar gaskiyan dakasani domin kuwa Allah nasama yana kallon mu gabaki daya, meke faruwa fadimani daga farko zuwa karshe kafahimtar dani" ajiyan zuciya Aliyu yasauke yace "mahaifina nada mata uku, wata hudu zuwa biyar dasuka wuce yakaro tahudu..........." anatse yake bama Mai Martaba labarin komi tundaga farko har karshe har zuwa Prison Aneesah da kuma yanda akayi yasato ta yau sanan yay shiru.
Kallon Aneesah mai Martaba yayi anatse yace "haka maganganun shi yake Fateemah?" gyadama mai Martaba kai tayi ahankali tace "eh hakane" shiru Mai Martaba yayi yana kallonsu, a ido kadai zaka gane irin son da Aliyu yakema yarinyar, shiru yadanyi sanan yafara jawabi. "Aliyu karkai tunani dan akwai kyakkyawan alaka tsakanina da mahaifinka zaka iya kawomin komi na dauka a'a sainai bincike, amatsayina na sarki inada ikon na aurar da yara irinku wayanda suke son juna tsakani ga Allah amma sabida wata matsala ko gaba dake tsakanin iyayensu da rashin jituwa yasa suka hana auren to a irin wanan case din, yaran kan iya kawo kansu gareni na wakilce su nakira shaidu na dauramusu aure abisa sunna, Fateema tambayoyin dazan miki yanzu shine zasusa na aurar daku dan haka kibani amsa tsakanin ki ga Allah, abinda kikeso shizan miki bazan taba miki doleba kinajina" gyadamai kai tayi ahankali tana goge hawaye, shiru Mai Martaba yayi yana jiran tasami natsuwa, wajen minti biyar yabata sanan yace "Fateema Bintu" ahankali tace "Na'am Mai Martaba" anatse yace "inaso ki gayamin tsakanin ki ga Allah, wanda zaki aura yau kina sonshi koko mahaifiyarki da Baffan kine sukace saikin aureshi? Kifadi mani gaskiya" hawayen daya zubo mata ta share, ahankali tace "nima bansani ba ko ina sonshi ko bana sonshi, amma Ammi na na sonshi tace na aureshi" shiru mai Martaba yayi yana kallonta, yay kusan minti biyu ahaka sanan yace "wanan karan ma baniso kimini karya kaman yanda kika amsamini tambayata ta farko haka nakeso ki amsamini ta biyun nan, tambayoyi uku kacal zan miki, me mahaifiyarki tace miki game da Aliyu?" shiru tayi tasa hannu ta share hawayen ta kafin cikin muryan kuka tace "ta...tace" tadanyi shiru kafin ahankali tace "tace inhar ita ta haifeni na manta da Aliyu arayuwata, zata nuna musu nima y'a ce kaman kowa kuma abin so, dan haka inhar ni yar halak ce babu abinda zanyi da dandan wanda yakaini gidan yari" takarashe maganan tana goge hawaye muryanta na rawa sosai, ahankali Aliyu ya lumshe ido he's so hurt kaman zai mutu yakeji, shiru Mai Martaba yayi yana kallonta duk tambayoyin daya mata na tattare da hikima, saida yabari ta natsu sanan yace "sai tambayata na karshe Fateema, inaso kigayamin tsakanin ki da Allah, Fateema kinason Aliyu?" da sauri tadago kanta ta kalli Mai Martaba ido da ido, anatse batare daya bari ta janye idanunta daga kanshi ba yace "karkimin karya, kinason Aliyu ko bakison shi" wani irin rawa kirjinta yafara kaman yanda na Aliyu ke dukan biyar biyar yana bala'in tsoron amsar dazata bayar, lumshe ido Aneesah tayi maganan ganun Ammi nadawo mata _"kicire Aliyu daga ranki, ki manta dashi, inhar nina haifeki keyar halak ce ki manta da Aliyu, baki ba Aliyu Aneesah, me zakiyi da yaron wanda yakaiki gidan yari"_ bude idanunta tayi ta kalli Mai Martaba tace "ba.....banason shi!" ji Aliyu yayi kaman an katsamai zuciya daga asalin jijiyan dake rike da ita tana lilo bayama jin kanshi, kallonta Mai Martaba yayi yanda tarufe fuska da hijabi jikinta na rawa sosai kana ganinta zakasan kuka takeyi, dauke kai Mai Martaba yayi ya kalli Aliyu dake gefenta yace "kaji amsanta ko Aliyu dan haka bazan taba iya auran da daya bayason dayaba sai in duka biyun keson junansu dan haka katashi katafi ita zansa amaidata gida iyayen ta suganta a daura mata aure, tashi katafi Aliyu" ahankali Aliyu yasa hannu yadafa center carpet din dayake zaune idanunshi nawani irin juyawa da kyar ya iya mikewa tsaye kara karfin kukanta Aneesah tayi sosai jikinta na bari, ahankali Aliyu yajuya yadaga kafa da kyar yay taku daya Aneesah nawani irin kuka da karfi, daga kafa yayi ahankali yay taku na biyu idanunshi na neman rufewa yana hanasu, taku na uku yadaga kafa zaiyi idanun suka rufe ruf yawani yanke jiki yazube asume arude Aneesah ta janye hijabin daga fuskarta ta waigo jin karan dataji, da sauri fadawan dake wajen suka zabura zasukai doki da hannu mai Martaba yamusu alamu karwanda yaje, wani irin kyafkyafta ido Aneesah tayi tana kallonshi ganin dai shine zube akasa asume yasa dawani irin gudu tamike. "Ya Aliyuuuuu" tsugunnawa tayi akanshi da sauri tasa hannu tajuyo dashi tana kuka sosai, ta bubbuga kirjinshi. "Ya Aliyu me haka? Katashi, Ya Aliyu dan Allah karka mutu kabarni?" arude tace "suma" wawwigawa tashiga yi ahaukace bottle water data hango agaban mai Martaba yasa ta tashi da gudu bamatasan inda kanta yakeba taje gaban mai Martaba tazuri ruwan tadawo da gudu tana kuka tabude bottle din ruwan ta yayyafa mai a fuska tana kuka sosai, ganin bai ko motsi ba yasa tasa hannuta kan fuskarshi tana wani irin sharemai ruwan fuskan tana kuka sosai tace "Ya Aliyun dan Allah katashi wlh ina sonka, ina sonka Ya Aliyuna, I love you so much wlh" ganin ko motsi baiyiba yasa tadaura fuskarta kan fuskarshi tana wani irin kuka mai tsumma rai hawayen ta na gangarawa suna sauka kan fuskarshi tace "Ya Aliyu dan Allah katashi, I love you so much, babu soyayyar data isa ta shigo TSAKANKANIN SOYAYYAN mu, I believe you, am yours Ya Aliyu na, wake up" tafashe da kuka sosai, dan motsin dataji yayi yasa tadago kanta ta kallai arude tareda kamo hannunshi tarike gam tace "Aliyu, am here wake up, inasonka kaji be stay with me" bude jajayen idanunshi dasuka kankance yayi yadaura akanta, fuskarshi tai cupping da hannayenta dasuka sha lalle sosai tana wani irin kuka ta gyadamai kai tace "yes I love you so much" hannunshi da baida karfi sosai yadaga yakai yatsar shi ahankali yashare kwallan datakeyi yana girgixa mata kai alamun tadena kuka, murmushi kuka tayi hawaye na zubowa ta gyadamai kai da sauri tace "okay bazan kara kukan ba" wani irin murmushi mai Martaba yayi ya kalli kunyangin wajen yace "adau Fateema akai cikin gida" ya kalli sarkin gida yace "akira likitan Mai Martaba sarkin gida, sannan akira jama'a yanzun nan suzo su shaida daurin aure tsakanin Aliyu da Fateema" da sauri kunyangin da mai Martaba ya tura suka karasa inda Aliyu da Aneesa suke suka daga ta sukace muje cikin gida a shiryaki za'a daura muku aure, ahankali ta share hawaye tana waigen Aliyu dake kallonta da idanunshi dasuka kasa buduwa duka, daga Aliyu fadawan sukayi aka kaishi kusada mai Martaba, fadawa da duka ma'aikatan gidan Mai Martaba suka cika falon danya bada izini akira kowa nan mai Martaba yadauka aure tsakanin Aliyu da Aneesah akan sadaki dubu dari dashi mai Martaba yabiya mai, wani irin ajiyan zuciya kawai Aliyu ke saukewa kafin hawaye su shiga saukowa daga idanunshi he just can't believe he's now Aneesah husband, wani irin nishi daya fara yasa Mai Martaba yace adaukeshi ayi chan wani kebantaccen flat da bakin Mai Martaba masu mahimmanci ne yakesawa akai wajen yasa aka kaishi daidai likita ya iso aka shiga dubashi, dubashi likita yayi tsaf sanan yamai allura bayan yama mai Martaba bayanin ciwon zuciyane da kuma tsantsan damuwa, saikuma zazzabi dan ruwa ya dakeshi amma wanan alluran zai saukar dashi, zai dawo da daddare yazo dubashi, godiya mai Martaba yamai sanan yatura kuyangi yace "ace in angama shirya amarya akawota bangaren mijinta".
_duk wacce ta karanta batare data biyaba ban yafeba, in kinason book dinan, chat me up 07012181461_
[23/04, 08:19] Aishat Muhammad: _*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_
_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤
_✍🏿M Shakur_
7️⃣1️⃣
_how to pay_
_zaki turo 300 ta account number na 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turo evidence of payment to my watsap number sainai adding naki a group din a tsakanin soyyayya, marasa bank zaku iya turo katin MTN_
_Gidan Biki_
Paracetamol Inna taballo tabama Ammi da kanta kewani irin ciwo zazzabi yarufeta sosai tace "sannu ga paracetamol kisha ina za'ai haka yau bikin yarki ko daurawa ba'a yiba zazzabin yarufe ki, su Baban Hamma ma sunje su dauko limam a mota dan ruwa yahanashi fitowa gashi babu abin hawa su ango har sun iso da mutanenshi duk ana waje ana jiran dawowan su, yanzu kinga har biyu da rabi Baban Hamma yakira yace suna hanya kawai daurin auren karfe uku ne, ungo dan Allah sha ko zaki warware kisami karfin yin hadamar bikin Yarki" ahankali Ammi tamika hannu ta karba tareda tashi ta zauna tana karanto addu'a sabida gabanta sai fadi yake daidai lokacin Mubarak Auta ya yaye labulen dakin Aneesah da Ammi da Inna keciki yaci gayu sosai yana kumbure kumbure, kai Inna tadago ta kallai tace "kai lafiyan ka zaka fadomana daka ba sallama har a dauro auren ne ka shigo cikin mata ko kunya bakaji ka kadai namiji a gidan dake cike da mata" turo baki yayi yace "ni har yanzu ba'a dauraba Baffa basu dawoba, kuma yunwa nikeji kibani abinci inna" hararanshi Inna tayi cikeda takaicin wanan sakarcin irin nashi tace "wai kai Hamma wani irin sakaran yaro ne, yunwa yunwa saikace ba'a baka abinci, yanzu ka tsayane a daura auren dakai bazakayi ba saika shigo gidan nan dake cike da mata kazo cin abinci eh Auta to bazakaci abincin ba" turo baki yasake yi ya bubbuga kafa akasa kaman zai fashe da kuka yace "wlh ni saikin bani abinci na" murmushi Ammi da kanta ke masifan ciwo tayi tace "kaji jeka kiramin Aneesah kuzo tare kafin kadawo zaka tarar da abincin ka na zuba maka harda nama" tsalle yayi yafita da gudu dan zuwa kiran Aneesah, da sauri Inna ta kalleta tace "Aneesah dake wajen kawayenta kuma kike nema? Ba dazun nan kukabar wurin ba, bazaki bar yarinya ta shakata da kawayenta ba yau bikinta" lumshe ido Ammi tayi tana wurga paracetamol abaki ta kurbi ruwa tace "Inna gabana ke faduwa sosai, kuma sai fadomin take arai, sabida kaina dake ciwone dani dakaina naje naganta amma bazan iyaba saisa nace a kiramini ita" dan dariya Inna tayi tace "kinada abin mamaki Maman Aneesah, banda abinki yau zaki aurar da yarki yau zaku rabu na dindindin saidai intazo wajenki ziyara ko tunanin wanan kadai ya isa yasa gabaki yafadi, mudai yau zamusha kallo in akazo kai Aneesah gidan mijinta" murmushi dukansu sukayi atare daidai Mubarak din ya shigo da gudu yace "Ammi Salamatu tace bakin aiko akirata ba wai tana wurinki, cewama tayi karya nake dan Aneesah na wurinki tundazu kika aiko akirata" da sauri Ammi ta tashi tazauna kafin ma tai magana Inna tace "wani irin shirme Salamatu ke fada kuma tun dazu ina tare da Ammi yaushe muka aiko a kira Aneesan" da sauri Mubarak yace "to wlh batanan Inna, su Salamatu kadai ne da kawayenta keta rawa agidan hartana cewa inna koma nace mata tayo sauri tadawo suna jiranta" wani irin faduwa gaban Ammi tayi da sauri ta tashi daga gadon tadau hijabinta Inna tace "tsaya ina zaki keda kanki keciwo karkije kifadi fa ga ko ina chabali" da sauri Ammi tace "ban gane me Mubarak kefadi ba gwara naje naji dakaina" tai hanyar fita da sauri Inna tace "bani hijabina Mubarak bari na biki" Hijabin Inna Mubarak yabata ta karba tasaka duk suka fito wajen yacika da maza sosai ganin Ammi da Inna harda Mubarak yasa Baffa da isowan shi kenan yana gaisawa da Mahaifin Hafiz yace "ina zuwa Alhaji" da sauri shida Na Sani suka karasa wajen su Ammi dasuka fito taresu yayi yace "me haka ina zaku maza duk sun cika waje yanzu fa za'a daura auren" da sauri Inna tace "Baban Hamma Aneesah ce wai aka aiko agidan patin su wai Ammi nakiranta suka tafi nikuma bamu muka kirata ba to yanzu bata gidan shine zamuje muduba da kanmu" da sauri Baffa yace "mene" arude Inna tace "bari muje mugani" gidan su Salamatun suka shiga shima Baffa kasa hakuri yayi yabisu ciki shida Na Sani suka tsaya wajen jikin Gate.
In baki da dari uku karma ki karanta dan wlh banyafe mikiba
Da Salamatun suka hadu daidai tafito da kwanukan dawasu kawayensu suka gamacin abinci, ganin Ammi da Inna yasa tace "Ammi kinga Mubarak kwar kwar yazo wai kina kiran Aneesah bayan tun dazu Aneesah na wurinki" kafin ma Ammi tai magana Baffa daya kasa hakura ya karaso tsakar gidan yace "ke Salamatu kaman ya Aneesah na wurin su, su tuntuni suna gida basu aiko a kira Aneesah ba" cikeda mamaki Salamatu ta zaro ido tace "ha'a amma dazu wata doguwar mata mai jiki tasaka bakin hijabi har kasa da nikabi da glass ta shigo duk kawayen muma sun ganta, dan Summaya ma ta tambaya inane dakin da Aneesah take tanuna mata dakinmu, ta shigo tace wai Ammi kince ta taho tareda Aneesah yanzun nan sutaho tare, shine ta tashi tasaka hijabi, tace nazo muje natare nace mata Inna bita wazai bama kawayen mu abinci saisa ban bitaba" arude Ammi tace "innalillahi wa innailaihi raji'un saisa gabana keta faduwa, wlh niban aiko wata mai nikabi tazo kiran Aneesah ba, munada ma mai nikabi acikin mutanen dasuka zo bikine?" da sauri Inna tace "wlh ko daya, ko mutum daya babu mai nikabi,