Showing 111001 words to 114000 words out of 186400 words
Chapter 38 - ATSAKANIN SOYAYYA COMPLETE By Maman Shakur .txt
sama, saiga wata yar wuka ta bayyana acikin bakar safar dake kafanta dake cikin kumbos din kafarta na prison, ciro wukantayi tawani irin tashi zaune tamike tsaye tadane bayan kujeran driver kaman wata yar biri takama kan Dr tadaura wukan akan wuyanshi cikin wani irin murya kaman ta rikakkiyar yar daba tace "waye kai? Me nakeyi a motar ka? Ina zaka kaini? Kasan waka dauko kuwa?" tai maganan tana kara rike kanshi gam ko motsi baya iyayi takara danna wukar akan makogoronshi kaman wacce ke shirin yanka rago motarsu a kwana kwana kaman zasuyi hatsari amma ko dar.
[09/04, 07:29] Aishat Muhammad: _*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_
_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤
_✍🏿M Shakur_
5️⃣3️⃣
Cikin wani irin yanayi na wanda ke kokarin kwatan kanshi yadan bugi hannunta dake wuyanshi trying to free kanshi da kyar yace "a....am..a..." baikai ga karasa maganan ba motar nasu tawani irin yin gefen hanya ta doshi wani babban bishiyar mango zai daki bishiyan dakenan gefen titi cikeda karfin hali irin na kwararren namijin daya iya tukin mota ya take burki da duka karfinshi hakan yasa tayoyin motar suka wani irin yin kara motar ta tsaya bayan sunyi kaman zasu fadi, hannun Aneesan yarike da kyar yanaja daga wuyanshi da kyar yace "pls....am....a....Doctor, likit....." ganin yana shirin mutuwa yasa ta janye hannun nata daga wuyanshi ya shiga tari kafin ta zagayo tadan hanyan dake in between kujerun gaban, tawani irin tsugunna kan wajen tai pointing mishi wukan hanun nata tana kallon yanda yake tari, ganin tarin yaki tsayawa yasa tadau goran ruwan datagani a motar ta bude tamikamai ahankali yasa hannu yakarba batare daya kalleta ba yakafa abaki saida ya shanye ruwan tass sanan ya cillar da goran kasa, saida yaji dama dama, tarin yadan natsu kafin ahankali yadago kanshi tareda juyowa ya kalleta hada ido yayi da Aneesan data tsugunna tana mai pointing yar wukan hannunta ko kyafta ido batayi kaman yay gamo da yar aljanna, saida gabanshi yafadi, gabaki daya sorrounding din idanunta sunji bakin lalle kwayar idanunta ne kawai fari, gashinan nata yay daka daka ya barbaje akan fuskanta ya sauka har kafadarta ya rurufe mata kunnuwa, cikin wani irin yanayi na mugun jin haushin ta yace "are you mad?" gyadamai kai tayi tace "yes" cikeda masifa yace "are you mad kasheni kikeso kiyi ne?" ko gezau batayiba da tambayanshi cikin dakewan murya tace "ba kashe ka zanyi ba, but zan kasheka yanzu in baka bani amsar tambayata ba, nace waye kai? Me nakeyi acikin motarnan" cikida fushi yace "naga some guards sun fitoda ke wai a sakeki suka yardake, they dumb u like a piece of gabbage, you don't look good bamakisan inda kanki yakeba shine I took you to drop you at any nearby clinic abaki taimakon dakike bukata, inhar kika tashi saiki tafi gida kokuma kisa akira iyayen ki suzo su dauke ki, but ni ba mugu bane and banda anybad intention akanki" tunda yake maganan take kallonshi saikuma takoma kan kujeran gefenshi ta zauna da kyau tana linke wukanta tace "yau wata daya da sati biyu kenan rabon da wani ko wata yamin mutunci kokuma yamin taimako, hahahaha" ta kyalkyace da dariya saikuma ta tsayar da dariyan tadan tashi tazo wajenshi da sauri yay baya yana kallonta adan tsorace yace "wai me haka? Kinga fita daga motana tunda dai kin farka kinemi gidanku, jibeki as small as ur are but u are so violence g......" hannunta data daura ahankali kan aljihun riganshi ko alamun tsoro batadashi tana kallon fuskanshi yasa yay shiru shima yana kallonta jidayayi hannunta zafi sosai alamun she's running temperature, wayarshi tazaro daga aljihun gaban rigan ahankali kirar iPhone ce wayar tarike a hannu takoma kan kujeran gefenshi ta zauna.
Yanda yabita da kallo yasa tace "relax, am not going to spoil your expensive phone" tana maganan tana saka number Ammi kafin tai dialing number takara wayan kan kunenta, saida wayar ta gama kuka ta katse Ammi bata dagaba, akaro na uku ne Ammi tai picking takai wayar kunne tareda sallama. "Assalamu Alaykum" wani irin lumshe ido Aneesa tayi heart dinta na girgixa after couple of days da aka kawota prison dinan tadinga kuka tanajin bakin ciki daga baya tazo ta hakura, this is the second time dataji wanan kukan bakin cikin na zuwan mata, she promised her self bazata kara kuka ba, she's a fighter, a strong girl, her mother's daughter da with or without Ammi she can live anywhere and survive.
"Hello waye banaji, helloooo waye?" wani irin ajiyan zuciya Aneesa ta sauke tana danne kukan datakeji yana tasomata da duka karfinta rabon dataji muryan Ammin ta harta manta, karan ajiyan zuciyanta da Ammi taji har cikin zuciyanta yasa kirjinta yawani irin buga, da sauri ta nemi gefen gado ta lallaba ta zauna kirjinta nabugawa sama da da, bakinta har rawa yake tace "A....Anee....s....sah.....na!" lumshe ido Aneesah tayi da sauri jin yanda Ammi ta takirata, cikin wani irin murya kaman na wacce ke shirin kuka Ammi tace "Aneesa talk to me, kece? Fateema na?" bude idanu Aneesa tayi ahankali kafin cikin dakewa da taurin zuciya da wanan muryan nata daya dawo kaman na wata rikakkiyar yar daba tace "Ammi!" wani irin fashewa da kuka sosai Ammi tayi ta wayan jin muryan Aneesan tace "Aneesah meya sami muryan ki? Me suka miki mutanen nan eh, mesa kike magana haka? Innalillahi wa innailaihi raji'un, Ya Allah gani gareka ka karemin yarinyar nan, Aneesah na what happens to you are you okay my baby?" lema leman dataji akan idanunta yasa ta sauri ta taba fuskanta hawaye taji da batasan tayaya ta fitar dasuba, da sauri ta goge fuskan cikin dakewa da wanan muryan nata tace "lafiyata kalau Ammi, kefa? Bakida lafiya ne? Kinyi wani iri menene Am....." bata karasa maganan ba Ammi tasake fashewa da kuka, bata ganin Aneesa amma hakanan tasan tanada babban aiki a gabanta, hankalinta yatashi wanan ba Aneesan ta data bama tarbiya mai kyau bace, this is anew Aneesa, yanda taji tana magana yasa taji zuciyarta ta tsinke kawai kiran sunayen Allah takeyi a zuci, da kyar ta daure ta share hawaye ta tareda tashi da sauri ta kulle kofar bedroom dinta da key sanan tadawo ta zauna ta share fuskanta tass, anatse tace "Aneesah na?" "uhm" ta amsata ahankali, sake daurewa Ammi tayi ta hana kanta kuka tace "kina ina yanzu haka a ina kika samo wanan wayar dakike kirana da ita? Tuntuni kina inane eh? Ina polisawan nan suka kaiki?" dan shiru tayi kaman bazata ce komiba saikuma ta dake zuciyarta nawani irin tafarfasa tace "prison! Ina gidan yari Ammi!" wani irin kuka dayazo ma Ammi yasa da sauri tadau pillow gefen gadon ta taushe bakinta tana kuka sosai, yarta ne Alhaji zaikai gidan yari? 20yrs old mace Alhaji zai aika prison? Me Aneesa tamai? Mai Aneesa tamai? Jibi yanda gidan yari yadawo mata da y'a? Dudda bata ganinta amma jibi muryan yarta, Alhaji ya cuceta bazata taba yafemai ba, Aneesan ta ce yanzu tai rayuwa a gidan yari? Tai wahala taga ukubobi na rayuwa haka? Ko hanyar gidan yari batasani ba amma tanajin labarin gidan yari tunko tana Amarya. Takai almost one minute ba tace komiba kafin ahankali ta janye pillow ta ijiye cikin wani irin muryan ban tausayi Ammi tana girgiza kai tace "how are you Aneesah na? Are you fine? Are you okay? Me suka miki achan? Sun wahalar dake?" gyadama Ammi kai tayi kaman tana gabanta cikeda dakewa tace "lafiyata kalau karki damu Ammi" gyadamata kai Ammi kawai tayi kaman tana ganinta tana mugun mamakin Aneesan, tasan she's just forming tasan karya take mata, tanaji a jikinta yarta ta wahala, tasha azaba, murya chan kasa tace "kina ina yanzu?" kallon hanya tayi tace "ina hanya ansakeni daga gidan yarin suka jefar dani wani mutumi yadaukeni zai kaini asibiti saikuma na farka yanzun nan" da sauri Ammi tace "kika farka? Suma kikayi?" girgixa kai tayi tace "Ammi karki damu, lafiyata kalau" "innalillahi wa innailaihi raji'un Aneesah, Aneesah, Aneesah wayyo Allah na zuciyata zan mutu" Ammi tama rasa natsuwarta sai sambatu kawai take tana kuka sosai da sauri Aneesa ta katse wayar dan inta cigaba da sauraron yanda Ammi ke kuka Ammi will just break her heart ne, kifa kanta tayi ahankali kan cinyoyinta mutumin nan nabinta da kallo, dudda wayan ba'a speaker takeba yana tsintar some maganganun Ammi cikima harda yanda Ammi ke kuka tana tambayanta meya sameta sosai yaji sun mugun bashi tausayi dudda baisan wacece itaba but hakanan yaji ajikinshi something da kuma situation ne yadawo da ita wanan yar daban.
Ringing da wayar ya shiga yi Aneesan taki dagokai balle ta dauka yasa ahankali yace "answer the call, ur Mum is calling again" katsewa wayar tasake yi wani wayan yakara shigowa ganin batada niyyan dauka yasa ya matzo ahankali ya karbe wayan daga hannunta ya kalli screen din kafin yay picking yakara a kunne. Cikin kuka sosai Ammi tace "Anee....sah na" ahankali guy din yace "Assalamu Alaykum" da sauri Ammi tace "bawan Allah waye kai? Ina y'ata?" ganin yanda duk Ammi ta daburce yasa yace "calm down Mum relax, sunana Dr Zaid, a per-term Dr prison din da yarki take, I only come idan akwai any surgical issues daza'ama prisoners, yau na shigo nai surgery bayan nagama naga anyi releasing yarki a sume, I could not leave her that way is against my professional code of ethics shine na dauketa with the hope nakaita asibiti aka dubata tana farfadowa saita nemi iyayen ta but kafin nakai saita farka, relax am not a bad person bazan taba cutar yarki ba dan nima inada kanwa mace sanan inada y'a mace shekarunta biyar aduniya bazan so wani ya cutanmini su ba, yanzu tell me kina ina nakaiwo miki ita nasan Abuja sosai dan wurin zuwana ne" ajiyan zuciya Ammi tasauke ta goge fuskarta tace "bawan Allah nagode maka, yanzu taimako daya nakeso kamin so nake ka tayani kaita Park, kasata a motar kaduna gidan kanin babanta zata" da sauri yace "kaduna Mum, ai am going back to kaduna yanzu haka, kin yarda dani natafi da ita kokuma na kaimiki ita Park din?" dan shiru Ammi tayi kafin ahankali ta nisa tace "na yarda dakai kodan diyarka dakacemin kanada, ka kaimini ita kaduna zan sanar da Baffan ta zai sameku ya karbeta ahanya" ahankali yace "to shikenan" zai katse wayar Aneesa tadago kai ta fizge wayar daga hannunshi ta kara akunne cikin wani irin murya tace "nace miki inaso naje kaduna ne Ammi?" shiru Ammi tayi kafin tace "keda gidan nan har abada Aneesa, ki tafi wurin Baffan ki nima zanzo nasame ki a wajen, duk wanda ya cutar mini dake nabarsu da Allah, Allah baya bacci no need for you to come back here and cause issues nasanki, ki barsu da halinsu, watarana sai labari kinji, kiyakuri, kije wurin Baffan ki kijirani anan, am coming for you okay" gyadamata kai tayi ta katse wayar ahankali tana huci. Kunna motar yayi yaja ta gefen ido yake kallonta ta mugun bashi tausayi ganin yanda take goge kwalla tana fighter tahana kanta kukan amma takasa, ganin yanajin tausayinta over yasa ya maida hankalinshi kan tukin dayake yi baisake kallonta ba.
Number Baffa Ammi ta nemo ta kira, ringing daya ya dauka, ahankali Ammi tace "barka da warhaka Baffa" "barkan mu dai Maman Aneesa" dan shiru Ammi tayi kafin ahankali tace "Baffa ansaki Aneesa yau tana hanyar zuwa kaduna, zan turama number mutumin daya dauketa, Baffa ka kulamin da Aneesah, Baffa Aneesa need strick care gidan yari Alhaji yaturata, zadaika ganta dakanka, Baffa rayuwata nacikin kunc....." takasa magana sabida yanda kuka yaci karfinta, haushin ta sosai Baffa yakeji amma ayanda Ammi ke kuka sai jikinshi yamai sanyi yasan koshi baikai Ammi jin bakinciki faruwan komiba, murya chan kasa cikeda lallashi yace "kinga, kinga Maman Aneesa, calm down komi yay tsanani maganin shi Allah, wanan jarabawa ce da yardan ubangiji kuma zamuci, dan haka kiyihakuri, kuma karkiji komi akan Aneesa Allah yakawo ta lafiya koma me tadawo yarmuce ahaka zamu rungume ta da hannu bibbiyu sanan we will shape her to our like, addu'a kawai zakiyi tamata kinajina, kul karna karaji kinyi kuka kan zancen nan tunda ansakota Alhamdulillah, duk wata matsala da sauki ce da yardan Lillahi, share hawayenki" ahankali Ammi tasa hannu ta share hawayen tass ta sauke ajiyan zuciya, murya chan kasa tace "Baffa sai magana ta biyu" da sauri Baffa yace "oho ina jinki" ajiyan zuciya tasake saukewa tace "Baffa alfarma nakeso, inaso ka saidamin da shanayen Aneesa guda biyu so nake kabani dubu dari sauran kudin inaso kayi amfani dasu ka shigarmin da kara kotun musulunci anan kaduna, inaso araba aurena da Alhaji, dubu darin zan biyashi kudin sadakinshi dasu" shiru Baffa yayi tunda tafara maganan harta gama saida tace "kanajina Baffa" da sauri yace "inajinki" anatse yakira sunanta. "Rukayya" yanda yakira sunanta kai tsaye yasa Ammi tagane he's so serious dan he hardly call her name direct. Anatse Baffa yafara magana. "Rukayya na isa dake, sanan inada iko dake, kinada wani irin matsayi na yar uwata najini dabazan iya tsayawa ina ganin zakiyi shireba na barki, nasan kin tsani Alhaji sabida abinda yama Aneesa, bari kiji wata magana aduk lamarin nan laifin Alhaji guda nake gani, shine dabai tsaya yasaurare muba, kisaka kanki atakalmin shi, daga ke har Alhaji kunyi boko, yan boko kuma mutanene dasun yarda da technology, babu yanda za'ayi mutum kaman Alhaji yaga camera yakama abu haka bayan ya kalla kuma yace bahaka bane, tunda har yagani da idanunshi ga Aneesa nasaka poison bazai taba yarda ba itabace dole kuma ya hukunta ta, kar abin nan yasa kice zaki nemi saki, babu kyau saki, kin riga kinsa Aneesa tadawo wajena hakan dakikayi kin kyauta tabarmai gidanshi, Ke kiyi zamanki kicigaba da rayuwan aurenki, ki rubuta ki ijiye nina fadamiki wata rana Alhaji saiyazo yasa guiwanshi akasa yabaki hakuri, gaskiya bata boyuwa fa da dadewa, komujima komu dada gaskiya zata bayyana, Allah zai warwaremuku komi, zai wanke Aneesa dake, bama ke kadaiba, Alhaji harnan kaduna saiyazo ya roki Aneesa gafara, nidake bamusan gaskiyaba Allah zai bayyana mana gaskiya, kiyi hakuri bazan taba baki goyan bayan ki kashe auren nan kifito ba, amma kiyakuri dan ke wacce aka cutace, Allah zai bimiki hakkin ki kowaye awanan lamarin sai Allah yatona musu asiri dai dai, daya bayan daya namiki alkawari, Aneesa kiyita mata addu'a, kimata fatan samin miji nagari na aurar da ita muhuta kinji Rukayya kiyahakuri" hawaye Ammi ta share bataso tama Baffa gardama hakan yasa tace "shikenan Baffa nagode" "yauwa, Allah yamiki albarka, kituramin number kinji" to.
[09/04, 07:33] Aishat Muhammad: _*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_
_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤
_✍🏿M Shakur_
5️⃣4️⃣
_07012181461 chat me up in kinason wanan book din_
.........
Dady yakai almost 20min awurin a tsaye yana mamakin what just happen yanzunan tsakanin shida Aliyu, inda yabari Aliyu ya kona kanshi da yaya zaiyi? Da ina zaisa ranshi, dagokai yayi ahankali ya kalli ma'aikatan wajen cikeda sanyi jiki yace "agyara wajen nan dan petir nada hatsari sosai" sanan yawuce yana tafiya ahankali ahankali duk jikinshi yay sanyi sosai yana kallon yanda matayenshi ke tashi daga window dasuke leke suna komawa ciki yadauke kai yawuce shashin shi yafada kan kujera.
Agurguje Aliyu yay wanka kusan sabi uku sabida yadena warin petir din sanan yafito, agurguje yake shirya wa dan baiso yabata lokaci, 3quater na gucci yasaka da wata dark brown paco robbani logo print shirt daya haska fatar shi yafito da kyanshi, fesa turare yayi yasa takalmin shi na prada sanan yadau car key dinshi yana dingishi yafito yay flat din Dady babu alamun wasa akan fuskanshi, ahankali yatura kofan dakin da sauri Dady dake kishingide kan kujera yatashi yazauna da kyau yana kallon Aliyun kaman yau yafara ganinshi, har gabanshi Aliyu yakaraso ba yabo ba fallasa yace "Wani prison ka kaita Dad?" yadanyi shiru yana kallon Dady kafin ahankali yace "zanje nadauko tane" sosai Dady ke mamakin shi dansai yanzu yakara ganin son Aneesan akwance kan fuskar Aliyun, ahankali Dady yanisa yana kallon fuskanshi dasaiyau ya yarda da maganan manya cewa abinda kafiso shiyafi baka matsala banda haka ace duk wanan abin dayake ma Aliyu bayagani, yazaci in Aliyu ya warke yaji meyayi he will be proud of him yarungumeshi yace I love you Dad, you are the best saidai yaga akasin hakan, sabida shine fa ya kulle Aneesa amma duk bayagani, yarinyar dataso aikashi lahira saima haushin shi dayake ji, ahankali yace "Zilanious prison take" dago idanu Aliyu yayi ya kallai irin kallon nan na Dady zaka iya aikata haka kafin ahankali yajuya kawai yafita daga flat din Dady na binshi da kallo yawuce yafita abinshi batare daya waigoba koya juyoba.
Yayi tafiyan almost 30min sanan yakai prison din shima da taimakon Google map, parking yayi yafito yana zare bakin glases din idanunshi kafin ya shiga ciki hargaban kanta inda wata guard take ga katon book din rubuta name of visitors a gabanta, tun kafin Aliyu yakaraso inda take take wani irin jarababben kallonshi wani irin dan gayune yau haka yazo prison dinsu, turaren shi daya fara mata sallama yasa tadawo daga yar gajeran tunanin datake, tace "Well done Sir, barka da zuwa yallabai, wakazo gani?" girgiza mata hannu yayi alamun he's not here to visit anyone, cikin kwantacciyar muryanshi yace "am here to pick up someone da akai releasing" da sauri tace "what's her name sir?" "Aneesah is her name" zaro ido tayi ta kallai tace "Aneesah barkono? Ai indai