Showing 57001 words to 60000 words out of 260204 words

Chapter 20 - Sannu Sannu Complete Hausa Novel By Billy S Fari.txt

yakeyi saboda yanda k'wayar idanuwansa ke rawa, qasan carpet a bakin kujerar da yake kwance ta zauna tana cigaba da cin abincinta hannu baka hannu akushi, a hankali ya jaye hannusa dake saman goshinsa yana kallonta fuskarta a sake tamkar babu abunda yafaru, abincin dake gabanta ya kalla sannan ya kalleta cike da tambaya, saboda iya saninsa tunda tazo gidan tare suke cin abinci yazu ko kimanin tsawon watanni hud'u kenan, to meye dalilinta nayin haka kenan ko haushinsa takeji ya tambayi kansa had'e da tashi zaunne yana kallonta.
'Dago kai tayi ta kallesa tare da sakin murmushi daga haka Bata cemasa qanzil ba Kuma shima bai cemata ba sai data canye abincin tas had'e dayin gyatsa.
"Alhamdulillah" tafad'a tana lashe yatsun hannuwanta har lokacin idanuwansa nakanta, turo baki tayi yasakar mata murmushi tare da miqewa ya d'auko mata ruwa a fridge ya miqa mata, karb'a tayi tasha sannan tamiqe tare da d'auke plate d'in takai kitchen, tray d'in data had'a abincinsu akai ta d'auko takawo agabansa ta ajiye sannan takoma saman kujerar kusa dashi ta zauna had'e da d'ora kanta saman kafad'arsa. "Malamina ka sauko kaci abinci, nabarka da yunwa ko?." Seda yad'an harareta sannan yace. "Bazanci ba!."

'Dan turo idanuwanta tayi awaje tana qyaqqyaf tasu had'e da cewa, "meyasa?. Abincin da kafiso ne nayifa!"

Taqarasa maganar tana b'ata rai tare da nad'e hannuwanta saman qirjinta, mintsili ya kaimata a kumatu had'e da cewa. "Saboda bakya son naci shiyasa kikaci naki bayan kinsan tare mukeci ko fushi kikeyi da nine akan abunda yafaru."
"Laaaa...wlh ba haka bane malamina, kawai yunwa nakeji sosai shiyasa na fara ci, atunanina ma bacci kkeyi, kayi hak'uri nazuba maka kaci nasan kana jin yunwa kaima."

"E.ehm bazanci ba." Yasake fad'a yana nad'e hannayensa akan k'irji kamar yanda tayi d'azu ya juya mata baya, saqalo hannayenta tayi ga wuyansa ta rad'a masa akunne, "afuwan habibyyy.." taja qarshen cikin wani salo daya sashi juyowar da bai tashiba cike da mamaki don bai tab'a jin takirasa da wani suna ba inba malaminta ba, "me kikace habibty?, Pls sake fad'a naji."

Maqe kafad'a tayi had'e da cewa, "o'oh sai in kaci abincin tukuna zan fad'a har sai kace ya isa" zamewa tayi daga kan kujerar tana dariya ta zubo masa abincin a plate, jallop rice ce tasha kayan ciki da kifi dasu irin baqin kifinnan gasashshe mai d'an karen dad'i, saman kujerar tadawo tana riqe da plate d'in abincin da cokali aciki, d'ebowa tayi a spoon takai masa abakinsa ya juyar da kai gefe,

"Meye?"

"Kifad'a mana." Yafad'a had'e da d'an d'aure fuska, dariya tayi sannan tace, "Shikenan! Nafad'a habiby, habiby, habibyyy.." bud'e baki yayi zaiyi magana ta tura masa cokalin abincin abaki had'e da sakin dariya, murmushi yayi tare da nunata da yatsa. "Ke ko?"

Haka tadinga bashi abaki yanaci har yaqoshi ta tattara kayan takai kitchen ta dawo, miqa mata hannu yayi ya zaunar da ita a tsakankanin kafafuwansa ya turo kansa tagefen wuyanta.
"Habibty!" Yafad'a cikin wata irin kasalalliyar murya, "uhmm, habibyn habibty!." Shiru yayi na wasu mintota yana nazarin irin kalaman da zaiyi amfani dasu wajen bata hak'uri akan abunda yafaru, juyo fuskarta yayi yayi mata kiss saiti inda ya d'an kumburo a goshinta sannan ya sake maida kansa agefen wuyanta yace, "kiyi hak'uri, kiyi hak'uri, kiyi hak'uri bisa abubuwan dake faruwa, nasan cewa ba kad'an kike kauda kanki ga abubuwan da mahaifiyat da kuma wasu 'yan uwan keyi maki ba, kwata kwata banajin dad'insu har ga ALLAH domin ke amanace agareni, nakan tsinci kaina cikin damuwa mai tsanani aduk lokacin da naga ana cutar mani dake, zuciyata na quna inajin wani d'aci a maqoshi domin babu abunda nake so araina duniya fiye da inganki cikin farinciki, zallar hak'urinki da tarbiyarki suke galaba akaina wajen kawar mani da damuwa badon haka ba inada tabbaci akan da tuni zuciyata da kuma rouhina sun daina aiki ajikina saboda kasa jurewa ganin duk wani abu da zai cutar dake, nayarda cewa shi so sa'ane kuma dacene tun a ranar dana had'u dake, domin kin zame mani gwana takowane fanni, a kyau kece gwanata, a hak'uri Banda yake, a iya kula da tarairayar miji kinfi mata dubu, girki tsafta da kawaici sai dai nace Masha ALLAH, Alhamdulillah domin duka nasamu awajenki, na tabbata kece alkhairina na duniya da kuma lahira don haka Ina mai sake baki haquri ga yanayin da muka tsinci kanmu aciki, natabbata wata rana zai zamo labari."
Tunda abubuwannan kefaruwa bata tab'a zaunawa ta zubar masu da hawaye ba sai yau, koshi saboda wani nauyine da takeji azuciyarta taji ya sauka saboda dad'ad'an kalaman daya fad'a mata hakan shine yayi silar zubowar hawayenta batare data shirya ba, wud'anda batasan da wace kalma zata fassarasu ba, na bak'in cikin abubuwan da suke faruwa da itane ko kuma na farincikin soyayyar mijinta dake lunkuwa azuciyarta. hannu yasa ya juyo da ita gaba d'aya suna kallon juna tare da tallabo fuskarta yana kallon kyawawan idanuwanta dake zubar da hawaye, bakinsa ya nufo dashi wajen fuskarta tayi saurin rufe idanuwanta hawayen dake maqale aciki suka samu damar gangaro, jira takeyi taji saukarsa akan nata amma sai taji akalarta sauya saboda harshensa da taji saman fuskarta yana lashe hawayen, sannan yadawo ga bakinta ya sakar mata wani irin french kiss daya sa ta sake lumshe idanuwa tana mayarnmasa da martani.
Sunfi tsawon mintuna biyar ahaka kafin ya zare bakinsa daga nata had'e dasa hannuwa yariqe fuskarta yana kallon idanuwanta d'aya bayan d'aya,

"Habibty kidena zubar da hawayenki domin duk d'igar da zasuyi suna yintane tamkar d'igar ruwan wuta abisa zuciyata, nasan ke jarumace kuma akoda yaushe nasara natare dake don haka kikara hak'uri kafin ALLAH ya yalwata mana mutashi nan kinji ko?"

"Habiby ba Ina zubar hawayene akan abubuwan dake faruwane ba, hawayena na zubane adalilin samun nagartaccen miji kamarka, kalamanka nada matuqar tasiri agareni domin ako yaushe d'auke suke da saqonni masu ma'anar dake gamsar dani irin soyayyar da kake yimani Wanda hakan shine babban burina arayu, bana son wannan haqurin da kake bani domin mahaifiyarka ai mahaifiyatace hakama 'yan uwanka nawane don haka duk runtsi zai jure komai akanka matuqar kana tare dani."

"Habibty bakyajin zafin abubuwan da ake yimaki ne?."

"Inaji mana amma girman soyayyarka bata barin hakan yayi tasiri azuciyata." Tafad'a tare da rungumesa. Rungumeta shima yayi sosai tamkar wanda za'a k'wacewa ita yace.

"I dont want to miss you in my life..., I love you for ever and ever and ever.."
Rashida da wasu kalaman tafahimta wasu kuma bata fahimcesu ba tayi murmushi itama tace "Nima haka." dariya yayi don yanada tabbacin ba duka ta fahimci meya ce ba amma tace itama haka duk da dai dad'ad'an kalamaine yayi bamasu illa ba.

"Habibty kema me?" Yafad'a yana sake shigar da ita ajikinsa sosai.

"Yanda kace mana."
Tabashi amsa atak'aice itama tana dariya,

"Tom nagode gobe kishirya zamu fara lesson in sha ALLAH."

"Ni bana so."

"Ai baki isa ba."

Nuraddeen yafad'a had'e da sakinta yana yimata cakulkuli, cikin mintuna qalilan ya mantar da ita duk wani b'acin rai da takeji azuciyarta.

Rayuwa kenan haka ALLAH ke jarabtar bayinsa da sukayi imani dashi akoda yaushe, baffa dai gashi da rai amma wasu abubuwan sun buwayesa, duk fitinar da akeyi yanaji Amma Babu halin tashi, ahankali yaji damuwa naneman tayar masa da ciwonsa yayi saurin jawo hisnul muslim d'insa yana karanta addu'o'in hammu wal hazan (damuwa da baqinciki) cikin ikon ALLAH yaji komai na gushe masa, Saida yaji yasamu sassauci da salama acikin ransa sannan ya ajiye yaci gaba da ambaton ALLAH.

Bayan sallar magrib su baffa Ali sun dawo don basu shigo gidan ba saida suka gama sallah, baffa ya zayyane masu duk abunda yafaru agidan wud'anda kunnuwansa suka jiyo masa, sosai baffa Usman yaji ba dad'i sab'anin baffa Ali da yace.

"Ni wlh Yaya nazata wani abun mai muhimmancin ne yasa ka tsaidamu gashi tun d'azu yunwa nakeji, ai indai muneera ce da uwarta abunda ma yafi haka zakaji, ni bari inje inci abinci inaga yafimun."
Yana gama fad'a yamik'e ya wuce sashensa, cike da mamaki suka bishi da kallo kafin su ahiga tunanin nemo mafita,

Baffa Ali na shiga ko sannuda zuwa babu inna ruqayya da tun d'azu take zaman dakon isowarsa tace.

"Alhamdulillah muje malan, wlh yau saika qwatarwa 'yata haqqinta akan cin zalun da aka yimata."

"Ke ruqayya fara bani abinci tukuna yunwa nakeji." Yafad'a yana zaunawa saman tabarmar dake shimfid'e abakin qofar d'akin, sanin zai iya birkice mata idan tamatsa masa da zancen yasa taje takawo masa abincin ta ajiye agabansa, ruwa taje ta d'ebo takawo masa jikinta har tsima yakeyi ta zauna tabasa labari,

Yana gamawa tashiga bashi labarin qarya da gaskiya ya mik'e cikin b'acin rai yanufi shiyar Yaya hawwa yana k'walla mata kira, iskota yayi zaune tana cin abinci bisa 'yar barandar dake cikin rumfarta akan kujerar tsugunno ta tsakar gida shima yanemi waje ya zauna.

Saida takai loma abaki ta had'iye sannan yace.

"Ina jinka Ali mike faruwa?"

Cikin kwantar da kai yace. "Haba Yaya hawwa yanzu ace agabanki yaron nan zai kama 'yar uwarsa yayi mata mugun duka baki d'au mataki ba."

"Uwarta taja mata." tabashi amsa atak'aice tanaci gaba da tura lomar tuwonta hankali kwance.
"Koma dai meye ai kamata yayi ace kin hanasa tunda 'yar tawa ba jaka bace kuma ko meye ai kece kika jamata, babban abunda kebani takaici shine keda kikace bakyason yarinyar nan kin tsaneta meye na wuni kullum a d'akinta? Kodai yanzu kin fara amincewa da zab'in barene."

"Hmmm! Ali kenan, wai ku atunaninku zuwa d'akinta da nakeyi na ALLAH ne? Yaro man kaza ai duk wanda yace baya sonka to tabbas har amutu bazai tab'a sonka ba, ai tsuntsu biyune nake jifa da dutsi d'aya don haka ka kwantar da hankalinka, wannan shashashar 'yar taka ita nakeyiwa yaqi amma ita da mahaifiyarta suna neman b'atawa shiyasa na zura idanuwa saboda kada ad'agoni, duk wani shiri nawa ya kammala don gaba d'aya nagama aiwatar da abunda na karb'o wajen malan bakada imani, k'waya d'aya yarage ina kammalasa zakaga aiki da cikawa.."
Yaya hawwa taqarasa maganar had'e da miqewa tana d'auraye hannunta agefen d'akin. dashe hauru baffa yayi had'e da cewa.

"ALLAH yaya hawwa?"

"Naka wasane Ali, an fad'a maka ja da baya tsorone, ai tuni nashirya maka maina tsaf da zan yaqi waccan yarinyar mai kama da miyagun mayu, yanda nakejin natsaneta yanzu bana tunani zan iya d'aga mata qafa har sai tabar gidannan don haka idan harkana son gurinka yacika dole kadakatar da uwar iyayin nan da muneera daga shiga sha'anin Nuraddeen, inba haka ba kuwa to dasu b'ata mun aiki k'wanda na tabbatar na dakatar dasu nida kaina."...












*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*πŸ‘πŸ˜­
[8/17, 10:19] Billy S Fari: πŸšΆβ€β™€οΈπŸšΆπŸ»β€β™‚οΈ *SANNU SANNU*πŸšΆπŸ»β€β™‚οΈπŸšΆβ€β™€οΈ
πŸ’Ž _Bata hana zuwa..._πŸ’Ž


_WRITTING BY:_ *BILLY S FARIπŸ’Ž*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*πŸ’‹

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*πŸ’ž

*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*πŸ’–

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❀️

Page___28πŸ’Ž

To shikenan Yaya hawwa yanzu nai magana, amma tuntuni sai zuba idanuwa nakeyi naga matakin da kikace zaki d'auka amma shiru yau gshi kimanin watanni hud'u kenan da kawota. "Kaji dai abunda nafad'a maka koma meye kawai kazuba idanuwa kagani."
Tafad'a tana qoqarin shigewarta d'aki, seda safe yayi mata sannan ya wucewarsa yana ayyana abubuwan da zasu faru idan burinsa ya cika.
Yana fita Kai tsaye waje yayi sai bayan sallar isha'i lokacin har karfe 9 tawuce, yana shiga sashensa inna ruqayya ta sake tarbarsa da maganar cewa yayi "Kai ruqayya matsalata dake rashin hak'uri, yanzu dai ki kwantar da hankalinki munyi magana da Yaya hawwa kuma tace tana nan ta d'aukar mataki akan al-amarin."
"Hmm wane mataki zata iya d'auka akai bayan duk abunda yafaru dasa hannunta itace ummul aba isu tana kallo ya narkarmun yarinya agabanta batace komai ba, Kai nifa wlh nagama gano bata son auren yarinyar nan da yaronta, kaduba yanda take kashe wuni ashiyarta kuma wai don ta Rena mana da hankali tace bata sonta."

"Ashsha ana baki kina roqo, Bari in fad'a maki wlh yarinyar nan Yaya hawwa bata qaunarta tuni taje takarb'o magani wajen malan bakada imani..." Nan ya kwashe duk yanda sukayi da Yaya hawwa ya sanar da ita, lokacin muneera na kwance can acan gefen gado kafin takoma d'an d'akin da take kwana, Inna ruqayyace tace tabari har mahaifinta yadawo taji matakin da aka d'aukar masa na dukan daya yimata, wannan dalilin yasa tayi kwancenta nan ita da qannenta maza su uku ciki harda yusuf tana jiran dawowarsa.

Baffa Ali daya saki baki yanata bata labari kawai sai yaga muneera ta taso tana susar kai tanufo inda suke zaune gefen gado tana fad'in.

"Baffa ni babu ruwana da matarsa kawai so nake ku a auramun shi, wlh baffa Ina son ya nura sosai." Zarar idanuwa baffa Ali yafarayi don bai zata muneera na cikin d'akinba da ko kad'an bazaiyi wannan maganar agabanta ba,

"Yi haquri muneera, ai zancen yanda za'ayi aurenne muke tattaunawa." Inna ruqayya tafad'a had'e da riqo hannunta, turo manyan lab'b'anta tayi cike da rashin iya magana tace,

"Wallahi Inna qaryane, ai duk Ina jinku maganine zakuyi ko korar masa mata, yo a maimakon haka kuyi mani magani na auresa kurum.." da sauri tajawota had'e da toshe mata baki shi kuma baffa Ali ya dafe kai don yasan ALLAH kad'ai ke hana muneera taje ta watsa wannan magana, abunda basu sani ba hatta Yusuf idanuwansa biyu basuyi bacci ba qannensa ne kawai baccin ya d'auka. "Shiii muneera kirufa mana asiri kidena wannan zancen kada wani yajiki, yanzu da kike wannan maganar mu ba yarinyar mukeso tafara fita ba sai ke kuma ki auresa, kinjimun shashashar yarinya."
Inna ruqayya tafad'i hakan tana murgud'e mata bakin da hannu data toshe mata shi.

"Kai Inna da zafi." Muneer tafad'a itama tana jaye mata hannun sannan taci gaba da cewa, "ni ku aura munshi a haka ko mata dubu garesa ALLAH zan auresa balle d'aya, so kukeyi sai na sake shekarewa aci gaba da cemun kwancen gidansu nura wlh ALLAH ni nagaji da jira."
Taqarasa maganar tana fashewa da kuka, takaici ne yarufe baffa Ali kamar yatashi ya rufeta da duka shima, Amma yasan hakan na iyasa tafallasa komai don ba qaramar sakarya bace, lallashinta suka shigayi tare da tabbatar mata da cewa itama wannan shekarar kota halin qaqa saita auri masoyinta ya nura sannan suka samu tawuce d'akinta takwanta, fad'a baffa Ali ya shiga yiwa Inna ruqayya akan meyasa bata sanar masa da muneera na d'akinba ai da bai d'auko zancenba agabanta.

"Yo kukan da taci yau ai sanin matakin da aka d'auka akansa kad'ai zaisa taji sanyi azuciyarta shiyasa nace ta zauna har kadawo."
Tsaki yayi had'e da juyawarsa ya kwanta cike da takaicinta da ita har 'yar tata.

A 'bangaren su Nuraddeen kuwa ana gama sallar isha'i yadawo gida, d'akin baffa ya shiga ya gaishesa tare da yimasa ya jiki lokacin suna zaune shida Rashida tagama b'ab'balla masa maganinsa yasha bayan tazuba masa abinci yaci tana karanta masa wasu addu'o'in dake cikin littafin (adda'u wad dawab) littafin daya qunshi nau'o'in cutuka da kuma kalolin maganukkan da za'asha ayi amfani dasu don samun waraka, d'aya daga cikinsu take fad'awa baffa alokacin, wuri yanema a gefe ya zauna yan sauraren bayanin da take yiwa baffa. "Baffa kaga wannan addu'ar ana karantata ga duk wanda ciwo yayi masa tsanani kuma aka rasa gano kowane irin ciwone ke damunsa, sai a nemi ruwa masu kyau acikin madaidaicin kwanon shan ruwa, sai a nemo kanwa da gishiri a zuba aciki, anemo albasa itama a yayyanka ta aciki sai marar lafiyar yasa duka hannayensa acikin ruwan bayan ya saka duk wud'ancan abubuwan da aka buqata sai ya karanta qula quzzai (falaq, nasi da kuma ikhlas) kenan, sannan yakaranta ayatul kursiyu karatun na sauka acikin ruwan da hannayensa ke ciki, sannan sai ya karanta wannan addu'ar kamar haka
( _Bismillahi arqiq, wallahu yashfik, min kulli da'in mardud, wamin kulli aynin au aynil hak'k'imu ALLAHU yashfik, allahummah rabbannas, ashfi bil ba'as washfi antashshafi'i laa shifa'a illa shifa'uka, shifaa'allahu laa yugadirus saqama_).
sai atofa acikin ruwan acire hannayen daga ciki, sai a d'ebi ruwan marar lafiyar yasha sannan ya tauna albasar dake ciki, asake d'iba yayo wanka dasu sauran sai a dinga watsawa ko ina a cikin d'akin da yake ciki ana fad'in ( _ikhrij aduwwallah_) har ruwan su qare, to da yardar ALLAH duk marar lafiyar da aka dage anayi masa haka ko ya dage da kansa yanayi zai samu sauqi da ikon ALLAH, kaga zuwa gobe idan ALLAH yakai ranmu sai mufara baffa saboda ba'asan in da dace yake ba ko ba haka ba."

Cike da farinciki baffa ya dafa kanta had'e da cewa. "Hakane 'yata, ALLAH yayi maki albarka kuma yasa adace."

"Amin baffa."

Tafad'a tana rufe littafin fuskarta d'auke da murmushi, juyowa tayi gefen da Nuraddeen ke zaune ta gaishesa had'e da yimasa sannu da zuwa sannan tamik'e tabar d'akin tana yiwa baffa seda safe.

Bin bayanta da kallo baffa yayi kafin yayi ajiyar zuciya yace. "Alhamdulillahillazi bini'imatihi tatimmusswalihat, haqiqi Nuraddeen Ina tayaka murna da kuma alfaharin zab'in da kayowa 'ya'yanka, banida shakku akan cewa ALLAH yagama mallaka maka rabin addininka yanzu yarage wajenka kanemi rabin don samun kyakkyawar makoma, Ina roqon ALLAH nima daya dubi zuciyata ya shirya mani mahifiyarka, bansan meyake damunta ba da har zata d'auki karan tsana ta azawa wannan nagartacciyar yarinya wacce samunta tamkar samun zinarine acikin qasa, narasa wane irin zunubi na aikata da har iyalina ta kasance ahaka, ubangiji ALLAH kaganar da ita tun aduniya basai ranar da nadama baza tayi amfani ba." Nisawa nuraddin yayi yana d'an muskutawa sannan yace, "Amin baffa."
Sun d'an jima kad'an suna fira kafin yayi masa saida safe snadiyar baffa Usman daya shigo d'akin riqe da 'yar ledarsa wacce tazamo masa jiki duk daren ALLAH sai ya riqowa baffa ita, wani lokaci gasashshen nama ne aciki, wani lokaci kuma kifi ko kuma sharare (had'in dankali da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login