Showing 147001 words to 150000 words out of 260204 words
Chapter 50 - Sannu Sannu Complete Hausa Novel By Billy S Fari.txt
uku sannan suka fara maganar komawarsu tunda anyi masa addu'ar uku, lokacin da sukaje wajen dady yimasa sallama akan zasu tafi kuma suna son suwuce da iyalan marigayin tunda dama shine jigonsu nazama garin kuma ALLAH yakarb'i abunsa sai dady yayi gyaran murya had'e da sake yimasu gaisuwar rashin d'an uwan nasu akaro na ba adadi sannan yace.
"Malan balarabe Ina son in roqeki wata alfarma awajenku idan zaku iya"
"Munaji alhaji ALLAH yasa batafi qarfinmu ba."
"Eh to! Banace haka ba amma Ina son ne idan har kun amince kubar iyalan marigayi anan har zuwa lokacin da zata gama takaba, nayi maku alqawarin cewa zan kula maku dasu bisa amana har zuwa lokacin idan ALLAH yabamu aron rayuwa."
Shiru baba balarabe yayi kafin yace to yabari sud'an shawarta tsakaninsa da sauran 'yan uwansa da suka zo tare, hakan yasa dady miqewa shida dr sukabar d'akin, bayan sun fita baba balarabe ya tambayi 'yan uwan nasa had'e da kirawo Yaya Maryam da aunty marwiyya dake can shiyar ammie da yake suma wan saheken rasuwar suka iso suda matan baba balarabe sannan yasa aka kirawo suma su umma sukayi shawara, nan take kowa ya amince da hakan don alkhairin da yayi masu bazasu iya hanasa wannan 'yar qanqanuwar alfarmar ba, umma kuwa dama cewa tayi duk shawarar da suka yanke akai tayi daidai batada ja, don haka koda suka nuna amincewar tazauna d'in batayi musu akaiba asalima yanzu tafijin garin aranta saboda mijinta dake ciki fiye da wancan garin da suka baro, gaba d'aya yafice mata arai batada sauran sha'awar komawa cikinsa.
Sosai dady yaji dad'in amincewarsu da buqatarsa yayita yimasu godiya tare da fatan ALLAH ya saukesu lafiya, har bakin motocinsu gida biyu dake wajen gate yarakasu sannan suka wuce shi kuma yadawo gida yana mai jinjinawa qoqarinsu akan amincin da suka bashi.
••• ••• •••
Baffa da baffa Usman kuwa basusan abunda kefaruwa ba har akayi zaman ukkun baba basuda labari akan rasuwar tasa sai bayan kusan sati biyu sannan suka sani, baffa yayi kuka sosai akan mutuwar aminin nasa wanda d'an uwansa yakasa sanar dashi saboda wata 'yar rashin fahimta data shiga tsakaninsu, babu abunda yafi qona masa rai irin ace ALLAH yasa har ansan inda suka tafi amma akaqi sanar dashi har ta ALLAH ta faru akansa, yamatuqar jin zafi da Kuma rad'ad'i azuciyarsa fiye da abubuwan da suka faru abaya, hakan yasa yaqudurce aransa bazaya koma waiwayarsu baba balarabe ba akan maganar da tasa suka yanke ganawa tsakaninsa da aminin nasa idan har suna tunanin hakan tafarune da son ransa ko kuma da had'in bakinsa har sai lokacin da ubangiji yatashi bayyanar da gaskiyar al-amarin, duk da wannan matakin daya d'auka hakan bai hanashi had'a waau daga cikin 'yan uwansa mata ba da wasu abokanansa da 'yan uwansa maza kusan mota biyu sukaje har gida suka yowa baba balarabe gaisuwa, aranar baba balarabe yaji kunyar da bai tab'a jiba aduniya, so yake yakeb'ance da baffa suyi magana amma tsananin b'acin ran dake zuciyar baffa yasa ko bari bayayi su had'a ido dashi balle suyi wata magana, gaisuwa dai ce takawosa kuma yayi masa fatanshi d'aya ALLAH yajiqan aminin nasa kuma ya lullub'esa da rahama, haka sukabar gidan batare daya samu keb'ewa dashi ba ko kad'an, wannan abun yaqara saka baba balarabe cikin nadama da dana sanin abunda yayi don yatabbata shima baffa yayi fushi akan zancen rasuwar da ba'a sanar dasu ba,
Su baffa nafita nan suka nufi gidan Yaya Maryam da aunty marwiyya suka yomasu gaisuwa, nanma baffa bai nuna masu komaiba banda gaisuwar da sukaje yimasu ba sannan suka koma gida.
Suna isa gida baffa yanemi waje yakwanta sboda wani irin zazzab'i daya rufesa, kallonsa matarsa nusaiba tayi had'e da cewa.
"Baffa don ALLAH kafidda damuwar wannan abun aranka, karka manta duka mai rai mamacine, koda kasan da maganar ganinsu bazaka iya hana mutuwarsa ba tunda lokaci yayi, haka kuma koda ansanar dakai zancen rasuwarsa dawuri bazaka iya canza komai ba akan abunda yafaru, don haka kayi haquri muma nan duk ita muke jira, babu wanda kezuwa har sai lokacinsa yayi, su day suka tafi basuyi gaggawa ba mukuma da bamu tafi ba bamuyi jinkiri ba, ubangiji ALLAH kasa muyi kyakkyawan qarshe."
"Amin." baffa yafad'a yana kallon d'an qaramin cikin dake jikinta yataso kad'an, murmushin da yafi kuka ciwo yayi yanajin wani irin zugi aransa, anan yaqudurta azuciyarsa idan ALLAH yasauketa lafiya matuqar namiji tahaifa zaiyiwa aminin nasa takwara, ganin yanda takafesa da idanuwa kamar zatayi kuka tana fad'in.
"Baffa kayi haquri kaji." Don haka take kiransa har yanzu, yayi yayi da ita tadena amma taqi, hakan yasa yaqaqaro murmushin qarfin hali had'e da cewa.
"Nusaiba to me akayi naga kina b'ata fuska, ai dole nahaqura tunda yariga ya tafiyarsa, amma inajin rad'ad'in rabuwata dashi sosai,"
"To kayi masa addu'a,"
"Zanyi masa nusaiba amma kema zakiyi masa takwara idan kika haifi namiji?"
Cike da yarinta tasa hannuwa tarufe fuskarta, don har lokacin bata cika shekaru goma sha shida ba aduniya kuma ALLAH ya albarkaceta da samun ciki wata hud'u kenan ynzu da kwanaki, yana matuqar jin dad'in zama da ita duk da zamowarta yarinya da mafiya al-amurranta shirme sunfi yawa, amma takan nuna damuwarta aduk lokacin data ganesa cikin damuwa kuma tana bashi kulawa daidai iya qarfinta naqaramar yarinya dad'in dad'awa ma ladabi da biyayyar da take yimasa badon 'yan matsalolin dake tattare dashiba dake hanasa samun cikakkiyara natsuwa da yace gaba d'aya bai tab'ajin dad'in rayuwar aure ba sai yanzu, qaramar yarinyace mma tanada kiyayewa sosai wajen iya zama da miji bisa turbar da yake koyar da ita, hakan yasa duk yanda damuwa tayi masa yawa idan yaga hakan zai haifar da tasirinta wajen cutar da yarinyar yake dannewa, hakan yayiko yanzu yadanne duk abunda yakeji yashiga zolayarta tana dariya.
Bayan kwana biyu baffa yaje can gidansu baffa Usman ya isko 'yan sanda sunyi cirko cirko aqofar gidan wai zasu kama muneera akan tafasama wani saurayi dutsi a ijiya har saida ta tsiyaye gaba d'aya.
Inspector najida yagani a tsaye jikin motar fuskarta ba walwala tana jira ashiga akamo muneerar, wajenta yanufa tana ganinsa tasaki fuskarta had'e da qarasawa wajensa kafin ya iso, d'an russuna kai tayi tagaishesa had'e da cewa.
"Baba ya gida ya kwana biyu?"
"Alhamdulillah 'yata injin dai ko lafiya?."
"Lafiya lau baba, yaron kune yafasawa wani ijiya shine aka kaimana qararsa."
"Subhanallahi wakenan."
"Muneera baba, yarinyar nan batajin magana sau biyu kenan ana kaimana case d'inta amma saboda kai sai nasa asulhunta abun, amma awannan karon dole mukai case d'in kotu."
"Haba 'yatah, don ALLAH karkice haka ai shi taimako ba'a gajiya dayinsa."
"A'a baba! Haka ya isa batajin magana da yawa, koda zamuyi wani abun dole sai munje kotu da ita."
"Shikenan!, 'yatah ALLAH ya kyauta, zamu biyo bayanku in Sha ALLAH muji yanda za'ayi."
Har inspector najida tajuya zata tafi sai kuma tasake juyowa ta tsaida baffa tana fad'in.
"Baba nikam nace wai yabatun tsohuwar matarnan taka Yaya hawwa, injin tasamu sauqi?."
Saida Baffa ya sinne kai yana d'an sosa qeyarsa saboda nauyin maganar da yaji sannan yace.
"Ehmm! Da sauqi zamuce, Amma har yanzu tana kware anaci gaba da bata kulawa aqarqashin jami'an lafiya."
"ALLAH sarki, ALLAH yabata lafiya, kwanakima nayita neman lambarka awayata narasa lokacin da naga ana nuno yanayin da take ciki a tv, abun yabani tausayi sosai sai natuna da zancen bokan da take zuwa wajensa dake asibiti, shaf namanta nakiraka na sanar dakai cewa bayan angama bashi treatment yafarajin sauqi da sati d'aya ashe shima yasamu matsala aqwaqwalwarsa, abun mamaki koda akayi masa gwaje gwaje sai aka samu qwaqwalwarsa lafiya take Amma yanayin abubuwa irin na miyagun mahaukata dake iya illata kowa, asibitin na shirin sallamarsa sai aka samu ya gudu, yanzu haka zaka ganesa akan tituna tsirara haihuwar uwarsa ko akan juji yanacin lalataccen abinci marasa kyau kamar yanda mahaukata keyi a wani lokacin kuma sai kagansa da sutura ajiki yana bin mutane yana bara abashi abincin da zaici, rayuwa yakeyi gatanan dai, shi ba dabba ba kuma ba cikakken mutum ba, hakan yasa nayi tunanin cewa wataqila matsalarsu d'aya da tsohuwar matarka, Ina nufin qwaqwalwarsu lafiya klw take saidai suna azabtuwane ta dalilin miyagun aljanun da suka shiga jikinsu su sukesa sunayin wud'annan abubuwan dakesa anayi masu kallon mahaukata, shine nayi tunanin kiranka nafad'a maka ko zaku koma gwada maganin musuluncine tunda yanzu kusan shekara d'aya da watanni kenan ana fama dana asibitin ba'a dace ba."
Shiru baffa yayi yana maimaita kalaman inspector najida a qwaqwalwarsa, tabbas maganarta akwai qamshin gaskiya aciki dole yayi nazari akanta sosai ko ALLAH zaisa adace.
"Shikenan 'yata in Sha ALLAH zamuyi tunani akan haka nida 'yan uwana, dama qarfina yafara qarewa akan wannan matsalar tata, kullum cikin kashin kud'i ake, kuma duk da binciken da sukayi akanta suka yad'a aduniya ankasa samun tallafi daga ko ina."
"ALLAH yasawaqe baba, har yanzu ita matar d'an naka ba'a ganta ba ko?"
Saida Baffa yayi ajiyar zuciya sannan yace. "ALLAH kad'ai yasani 'yatah.."
Ananma yake bata labarin rasuwar aminin nasa wato mahaifin matar d'ansa, tamatuqar tausayawa tare da yimasa addu'ar ALLAH yajiqansa da rahama, suna tsaye 'yan sanda suka fito da muneera duk anbubbuge mata fuska saboda taurin kan da tasa wajen kamota, su kansu 'yan sandan sai nishi sukeyi saboda wahalar dasu da tayi suna sake jibgarta da kulaken dake hannuwansu Inna ruqayya nabiye dasu tana d'ura masu zagi, juyowa inspector najida tayi da qarfi jin zagin da takeyi masu, Inna ruqayya naganin haka ta arta dana kare don bata manta irin azabar da tasha ahannun taba, ana qoqarin tura muneera mota tarugo da gudu ta lab'e bayan baffa da yayi tsaye yana kallon ikon ALLAH tana fad'in.
"Wayyo baffa ka ceceni, wlh ba laifina bane, innace tace naje wajen salele na karb'o mata saqo ashe wai iskanci zaiyi dani ya bata kud'i, shine ni kuma na doka masa wani qarfe yafad'a akan wani abu nasamu nayi guduwata, shine akace wai nafasa masa ijiya, don Allah baffa kataimakeni bana son zuwa."
"Yi haquri munneera jeki ku tafi yanzu nida Usman zamu biyo bayanku, Ina shi baffan naki yake?"
"Ya gudu baffa, kuma wlh har dashi ke karb'ewa salele kud'i wai zaya aura mani shi ni kuma bana sonsa, kuma baffa ya..."
"Ashsha muneera yishiru haka jeki kinji zamuzo yanzunnan?"
'Bare baki tayi tana kuka had'e da susar kai 'yan sandan sukazo suka cakumeta tanata tsalle tsalle da ihu suka sakata aciki, yaran anguwa da suka taru sai faman dariya sukeyi, girgiza kai baffa yayi sannan yabar wajen don ya tabbata Usman baya cikin gidan shi Kuma mahaifin nata sakaran wofi da rashin kunyarsa akansu kad'ai ta tsaya yayi guduwarsa...
Daqyar baffa Usman da baffa suka samu sukayo belin muneera batare da anje kotu ba saboda ijiyar yaron batayi komai ba amma yace sai ambiyasa kud'insa.
Don haka sukaje suka kama d'aya daga cikin shanun baffa Ali suka sayar batare da yasani ba aka biya salele kud'insa sannan akayi masu tsakani da ita, sauran kud'in kuma baffa yakai masa, baffa Ali sai faman wasar baki yakeyi duk d'aukarsa a banza aka bashi kud'in, Saida yagama murnarsa sannan baffa Usman yafad'a masa yanda aka samu kud'in, wayyo ranar yini baffa Ali yayi yana d'ebe masu albarka tare da zunduma masu zagi, yaran gida duk Wanda ya matsosa saidai yaji ya falla masa mari yana d'ura masa ashar, daga qarshe da yaji rad'ad'in yaqi d'ebe masa yasa muneera d'aki yasata yayita jibgarta yana tsina yana fad'in sai yafidda kud'in naggensa ajikinta.
Baffa Usman dake zaune yana shan fura yayi dariya had'e da cewa
"Oho dai, inma kasheta zakayi ka kashe ai 'yarka ce, ayanda kake marar hankalin nan da tunani babu abunda yakamata ace kayi illa kanunawa duniya cewa nagge tafi 'yarka muneera awajenka, shasha kawai, mudai bazamu doku ba awajenka, ubangiji ALLAH kashiryar mana dakai kada baqincikinka yasa murasa rayukanmu
*BAYAN SHEKARU ASHIRIN DA BIYAR*
Abubuwa da dama sunfaru wud'anda duk wani mumuni ya ishesa d'aukar darasin duniya matuqar babu ta'bewa da 'bata acikin rayuwarsa....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___67💎
Da gudu Rashida tashiga part d'in ammie tana kiran fatima.
"Aunty, aunty.." da kad'an sunyi karo da ammie dake qoqarin shiga kitchen, d'an ja da baya tayi cike da farinciki kafin tasake matsowa kusa da ita tarungumeta tana fad'in,
"Ammie kitayamu murna auntynah zata haihu."
Murmushi ammie tayi cike da mamakin irin sakewar da Rashida tayi dasu tsakanin jiya da yau sab'anin yanayin da take ganinta abaya, tabbasa iyaye wani jigone da rashinsu kan kawowa 'ya'ya tawaya maigirma arayuwa,
"Iyyeeeeee....to ina tayaku murana kice little yakusa zama big zai samu d'an qane.."
Ko qarasa maganar ammie batayi ba Rashida ta saketa tanufi bedroom d'in ummie don tasan tana ciki tunda bata ganeta a falo ba, girgiza kai ammie tayi tana kallon Dr nura da yabi Rashida da kallo cike da mamakin tsantsar farincikin da yaga tashiga, juyowa yayi suka had'a ido da ammie yace.
"Gaba d'aya ta canza tsakanin jiya da yau, kinga farincikin dake tattare da ita ammie sai kace wacce aa biyawa makka."
"Haba son!, ai dole tayi farinciki, iyaye fa rahamana sosai ga kuma wannan batun data tsinta alokaci d'aya, matuqar ita d'in masoyiyar kuce dole kaga fiye da wannan farincikin atattare da ita, ni yarinyar na burgeni sosai saboda sanin yakamatar ta"
"Ehm..gaskiya hakane, Rashida kam akwai hankali."
Da gudunta taqarasa shiga cikin d'akin tafad'a jikin fatima dake zaune bakin gado ta tallafe fuskarta da tafin hannuwanta guiwowinsu na akan cinainanta.
"Yeeew...auntay na congrat, agaskiya Ina cikin farinciki marar misaltuwa ayau, bayan duk wasu fad'i tashi da suruttan mutane yau ALLAH zai bamu namu d'an, Ina farinciki sosai auntynah ALLAH ya inganta yaraba lafiya."
Duk wannan surutun da Rashida keyi cikin farinciki Babu abunda Fatima keyi in banda kallonta, d'aga mata idanuwa Rashida tayi tana juya hannunta had'e da cewa.
"Me akayi ne aunty?"
Rungumeta tayi tajawo hannunta ta d'ora akan cikinta tana fad'in.
"Maman boy I can't believe so soon zan haifa maki baby, thank you so much for supporting me, haqiqa babu abunda yakai qarfin addu'a tasiri arayuwa, nagode bisa addu'o'in da kika d'orani akai da kuma wud'anda kikeyi mani ba dare ba rana, tabbas anasamun warakar kowace irin matsala tahanyar jajir cewa dayin addu'a, ALLAH ne yace anemi maganin kowace irin matsala amma ana samun warakane bisa qarfin addu'o'inmu agaresa, maman boy kinzamo wani haske acikin rayuwarmu da bazamu tab'a iya mantawa dake ba, yanda kika faranta mana kema ina roqon ALLAH daya faranta maki acikin dukkanin lamurrank, Ina miki albishir da cewa idan ALLAH ya saukeni lafiya zamuyi maki takwara da yardar ALLAH idan aka samu macce, wannan shine tukuicin zamowarki sila wajen tsaida hawayen da muka dad'e suna yimana kwaranya a idanuwa." Taqarasa maganar had'e da riqo hannayen Rashida ta d'ora saman idanuwanta dake fitar da qwalla.
"Kai aunty meye haka kikeyi?, Haba ya isa kidena wud'an maganganun don ALLAH, dukkaninmu ALLAH yakamata mumiqa godiyarmu agaresa, inada tabbin dama lokacin da zaki haihu yayi koda kuwa banbaki wud'an nan addu'o'inba, kawai sun zamo silane bisa wanzuwar qudurar ALLAH agareki, don haka kidena damuwa akan wannan, koda babuni acikin rayuwarku zaki haihu kamar yanda ALLAH ya tsaro, ita addu'a da kike gani ai makami ce babba da idan bawa yariqa duk nisan lokaci zai riskesa da yardar ALLAH."
"Zancen yimani takwara kuwa ALLAH ban yarda ba, sunan yazama local, ni kaina dariyarsa nakeyi wani lokaci."
"Commonnnn..." Fatima tafad'a tare dakai mata d'an duka agefen hannu tanaci gaba da cewa.
"Waya fad'a maki sunanki local name ne, ai sunan Rashida da kike gani sunane mai girma, is drive from the one names of ALLAH dt's (AL-RASHID), Ma'ana mai shiryarwa, asalin sunan ubangijine sai akayi amfani dashi ta hanyar qara harafin (a) yazama (RASHIDA) sai ma'anarsa ta tashi daga Mai shiryarwa zuwa shiryayyiya, don haka kiyi alfahari da sunnki akoda yaushe, domin sunane da bazai kusuba ga wud'anda sukasan asalin ma'anar inda aka ciro sunan, hikimace kansa iyaye nasakawa 'ya'yayensu ire iren wud'annan sunayen saboda fatan ma'anar dake tattare dasu tad'ore akan 'ya'yan masu."
"Laaa...kinsan ALLAH aunty! Hankalina bai tab'a kawomun wannan tunanin araina ba, atak'aice ma mantawa nakeyi da akwai sunan acikin jerin sunayen ALLAH da har zan iya tsinkayo ma'anar dake tattare da sunan nawa, kawai nidai tunda banji ana yayin sakawa jarirai sunan ba to sunan dane agurina, d'ai d'ai kune acikin yaran dake tasowa nake ji da irin wannan sunan, amma yanzu tunda kinfahimtar dani ma'anarsa da inda aka samo asalinsa Ina alfaharin kasantuwa ta da sunanan RASHIDA."
Gyaran murya ammie tayi abkin qofa tana fad'in.
"Agaida qanwar aunty, dama aikoki baban naki yayi shine kikazo kikayi zaunenki?"
"Laaa.... ALLAH na manta ammie, bari naje nafad'a ma uncle."
"Zauna abunki, ai ummanki data shigo tayamu murna tafad'a masa gashican har yafita."
"ALLAH shaf ni namanta sai yanzu bari naje nabashi haquri daga nan nayi masa ALLAH yakiyaye."
Tana gama fad'ar haka tamiqe tafita, ammie tace,
"Kinga mutuniyarki tasaki jikinta sosai yanzu ko?"
"Eh wlh ammie kuma naji dad'in hakan sosai, kinga kafin sutafi zata qara koyamun wasu addu'o'i sosai."
"Wlh ammie tun watan da kika aikamun da wannan ganyen guava kikace mudinga sakawa cikin ruwan tea muna tafasawa muna sha kafin muci komai da safe tun alokacin nafara jin canji da kaina ajikina, ranar muna zaune nida ita sai take cemun akwai wasu addu'o'i acikin alqaur'ani da yakamata na dingayi wud'an annabawan ALLAH sukayi da bai basu haihuwa ba kuma daga baya yabasu, hakan zai taimaka wajen sanya maganin duk da nake amfani dashi yayi tasiri ajikina sosai saboda qarfin addu'a, ammie kamar da wasa ta nunnuna manisu acikin alqur'ani nafarayi, yanzu kimanin watanni biyar inyinsu kenan sai gashi cikin yardar ALLAH ijaba tasauka, tabbas ammie ilimi nada dad'i aduniya kuma yawane dashi da bazaya tab'a qarewa ba sai randa bawa yakoma ga mahaliccinsa, Kuma duk yanda kake taqama dashi sai kaga wanda yafika shi."
"Dama hakane 'yata, koda kuwa wanda baikai darajarka bane ko kuma yafika zakaga yasan wani abun dakai baka sani ba, duk da nasan wasu daga cikin addu'o'in 'yata kifad'a mani sauran naji domin inada wata qawa yanzu kusan shekaru talatin kenan bta haihu ba, kuma