Showing 105001 words to 108000 words out of 260204 words
Chapter 36 - Sannu Sannu Complete Hausa Novel By Billy S Fari.txt
inspector najida d'in dake yawo a screen d'in wayar sannan yakara akunne, gaisawa sukayi kafin tashiga yimasa bayanin dalilin kiran data yimasa,
Nan take yace mata tabashi mintuna gashinan zuwa yanzu yanzu, binsa da kallo sukayi lokacin daya gama wayar yana kallon drip d'in da ake qara masa saura kad'an suqare yace,
"Usman taimaka ka qara gudun ruwannan su ida shigewa ko kuma kaciremun haka."
"Amma yaya ina zakaje haka kai da bakada lafiya."
"Ai Alhamdulillah nasamu sauqi, wannan la'anannen ALLAHn ne 'yan sanda sukayi nasarar kamowa, Ina so inje inji inda suka kai yarinyar mutane, Usman aduk lokacin Dana tuna da kalaman iyayen yarinyar nan nakanji wani qunci azuciyata, nakanji damuwa tasa idanuwana gaba d'aya rufewa saboda tsananin kunyarsu, mutanene masu tsananin karamci da halaccin dabai kamata nafita batun wannan al-amarin na 'yarsu ba."
"Hakane Yaya, Amma kabari har kaqara samun sauqi."
"A'a Usman kai dai ciremani mutashi mutafi."
Ko kad'an baffa Usman baya son jayayya da d'an uwan nasa shiyasa ya cire masa qarin ruwan, abincinci Nuraddeen ya fara zuwa ya siyo masa kafin yafito wanka, yana fitowa ya zuba masa yaci sannan gaba d'ayansu su ukun suka nufi Police station d'in,
Tun daga bakin shiga wajen suka jiyo tashin sautin qarar Yaya hawwa, sosai baffa yagano muryar tata Amma yabasar yanufi office d'in inspector najida yanajin wani Abu na tokare masa maqoshi, Nuraddeen kuwa yawo yafarayi cikin wajen yana neman inda sautin ketasowa don yatabbata sautin qarar na mahaifiyar sane, inda suka ajiyeta wajene da ba'a fiye ajiye masu laifi awajen ba,hakan yasa yakasa gano ko inda take, hakan yasa aguje yadawo baya yashiga office d'in da yaga mahaifin nasa yashiga, yana shiga ya tarar da baffa Ali da Inna ruqayya anfiddosu dduk sunyi baqi sun rame sun lalace, baffa Ali kuwa yayi laushi tamkar ganyen daya kasa samun kulawar ban ruwa, Saida Baffa yasa hannu ga wata takardar dake tabbatar da sakinsu baffa Ali d'in sannan inspector najida tafara qoqarin yimasa bayanin halin da Yaya hawwa keciki, da sauri Nuraddeen daya shigo yace.
"Inspector najida ina kuka kaimun mahaifiyata? Me kuka yimata ne take wannan qara marar dad'in ji?" d'aga masa hannu tayi had'e da cewa "pls Nuraddeen calm down, ka zauna kaji abunda zanfad'a inaga anan ne zaka samu amsoshin wud'annan tambayoyin naka."
Riqo hannunsa baffa Usman yayi had'e da zaunar dashi akan kujerar dake kallon wacce baffa ke zaune shi kuma yana gefensa tsaye, gaba d'aya Nuraddeen yagama rud'ewa da fita hayyacinsa qarar mahaifiyarsa dake yimasa amo a kunne, wacce ba ko shakka yatabbatar bata lafiya bace.
Gyaran murya inspector najida tayi bayan ta d'auke idanuwanta daga kallonsa da takeyi had'e da cigaba da cewa.
"Baba kamar yanda muka fad'a maka cewa da bakinta tasanar damu cewa ita takai matar d'anta wajen boka akayi mata asirin data bar gidan d'an nata, Wanda wannan dalilin ne yasa yau da safe muka tasata agaba zuwa jejin da bokan yake, ba qaramar wahala muka sha ba damu har ita wajen kamo shi wannan bokan, a hanyarmu ta isa wajen ne wani iska mai qarfin gaske ya tunkaro wajen had'e da turniqemu, bayan wasu mintuna qalilan kuma sai iskan yakoma ta inda yafito wanda ananne muka nemi ita Inna hawwar muka rasa, bayan mun gamo artabu da bokan had'e da kamasa muka bazama nemanta ajejin Amma bamu sameta ba sai akan hanyarmu tafitowa mukaci karo da ita ayanayin da zamu iya kiransa da kamar tab'in hankali, wanda nan take muka kwasosu mukayo nan dasu, Amma saka makon tirjiyar da boka yayi mana yasa muka kai masa harbi har sau biyu yanzu haka shi yana asibiti mun ajiyesa don ayi treating d'insa, wannan shine abunda yafaru zuwa anjima zamuje muyi masa tambayoyin daya kamata kafin mu hannuntasu ga hukuma".
Mutuwar zaune Nuraddeen yayi, domin idan ya fahimta mahaifiyarsa tana mu'amala da bokaye wanda yanzu haka ake tsammanin tasamu tab'in hankali ta sanadiyar hakan,
"Innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun" ya furta yana dafe kansa.
Ajiyar zuciya baffa yayi had'e da tambayar inspector najida ko zasu iya ganin Yaya hawwa don tabbatar da abunda tasanar dasu yanzu,
"Mezai hana." tafad'a tare da miqewa tawuce gaba had'e da cewa su biyo bayanta, jikinsu ba qwari sukabi bayanta har suka isa cell d'in da take ciki arufe,
Tsaye suka hangota tana surattai ita kad'ai kafin can suga an d'agata sama anbuga qasa kuma ko kad'an basuga wanda ya aikata mata hakanba nan take suka ga anfara lallanqwashe mata qafafuwa had'e da mummurd'e hannuwanta waje d'aya, juyar da kanta sukaga ansake fuskarta na kallon sama, kan kace me anmaidata wata iriyar halitta marar misaltuwa sai gumza takeyi tana wani irin gurnani, nan take hankulansu suka tashi don gaba d'aya basu tab'a ganin hauka irin nataba, kuka Nuraddeen yafashe dashi yana istigfari tare da duqewa qasa yana nemawa mahaifiyar tasa sauqi awajen ALLAH, juyowa inspector najida tayi tana kallon baffa had'e da cewa.
"Ya kamata kajaye case d'innan kuje gida da ita anema mata magani, domin ahalin da take yanzu ba abunda zata iya kuma batada sauran anfani acikin wannan case d'in baba, Amma kafinnan kabari sai nan da kwana biyu mungama tara suran bayanan daga wajen bokan zuwa lokacin kima kagama yanke shawarar abunda ya dace, don kasan ko kotu mukaje baza'a sauraremu ba tunda ba'a shari'a da mahaukaci?"
Jinjina kai kawai baffa yayi yana mamakin yanda Allah ya fara saukarwa da yaya hawwa hukuncinta tun ba'aje ko inaba, shikuwa Nuraddeen banda kukan da yakeyi na ganin halin da mahaifiyarsa ke ciki Babu abunda yakeyi, riqosa baffa Usman yayi ya riqe qarafunan dake jikin qofar shiga cell d'in yanaci gaba da rere kuka, tabbas uwa da d'a sai Allah, duk wanda yaga irin tashin hankalin da Nuraddeen keciki dole ya zubar masa da hawaye, gb d'aya yarud'e ya fita hayyacinsa yanda yaga mahaifiyar tasa takoma, duk munin halinta shi yana son abursa, yana sonta ahaka kuma dolene yashiga tashin hankali ayanayin da yaga halinda mahaifiyarsa keciki.
••• ••• •••
Su umma kuwa kasa kwana sukayi adaren da labari ya riskesu cewa asirine akayiwa 'yarsu, kuka umma keyi sosai tana tausayin awane irin hali 'yarta keciki Wanda shine ke qara haifar mata da zubar hawayen nata, baba kuwa gaba d'aya yasawa ransa dangana, damuwarsa d'aya halinda umma keciki wanda yana tsoron asanadiyarsa wani abu yasameta, ko kad'an bazai iya jure hakan ba kuma adalilin haka shima zai iya sake komawa cikin yanayin da bai dad'e da fitowa daga cikiba.
Kallonta yayi cike da tausayi kafin yace.
"Mmn Rashida yakamata kitsaida kukan nan haka kada wani abun yazo ya sameki, muyi haquri ALLAHn daya bamu Rashida shine ya d'oro mana wannan jarabawar damu har ita, mubita da addu'a idan har tana raye Allah ya bayyana mana ita, idan kuma ya amshi abursa, to ALLAH kasa tayi shahada kuma yasa tadace da aljannah fiddausi."
"Amin malan, Amma bana tunanin zan iya dakatar da wud'annan hawayen zuba bayan narasa 'yata tilo aduniya, wacce dukkanin burina da kufa farincikina aduniya ya tattarane akanta, musamman idan ina ganin abubuwan da zasusa dole nariqa tunawa da ita, sai nadingaji tamkar lumfashin zai d'auke, wlh ba mutuwa nakewa Rashida gudu ba domin dolece akan kowane mai rai, wahalar da nake tsoratar mata ita da abunda ke cikinta shikesani zubar da wud'annan hawayen."
Shiru baba yayi kafin ya dafata had'e da cewa, "nikaina idan nakalli d'akincan yakan tuno Mani da rayuwar da tayi aciki, haka shima Nuraddeen mijin nata, aduk sanda naganesa gabana na tsananta fad'uwa sai inji kamar zan ganesu ne atare, wannan yasa nafara tunanin yin nisa da garinnan da duk wani abu da zai nadinga tunowa da b'atan nata, daga baya kuma nayi tunanin cewa to idan da mutuwane tayi shima zan kasa rayuwane a inda muka rayu da ita?, Sai kawai naji na gamsar da kaina nahaqura kawai naci gaba da rayuwata anan, Amma yanzu wannan yanayin da nake jina aciki suna kamanceceniya da wanda kika bayyana mani kinaji, don haka idan kin amince yau d'innan zamuyi nesa da garinnan, wataqil hakan zai rage mana damuwa da rad'ad'in da mukeji aranmu, qilama yasama mana farincikin da bama tsammanin samu anan gaba."
"Na amince da hakan malan, Amma ina zamu tafi?."
"Wannan kuma ALLAH shikad'ai yasani kuma duk inda ya zab'a mana daidai ne agaremu."
Nan suka shiga tattaunawa tare da shawarwari akan tafiyar tasu, sun amince kuma sunyarda da shawarar da junansu suka yanke don haka suka tashi suka shiga kakkamta duk wasu abubuwan da suke buqata da bazaya gagaresu d'auka ba, wanda mafi yawanci suturar jikinsu ce sai 'yan kud'ad'ensu da sukayi ajiya da wud'anda suka samu na jinya da sauran abubuwansu masu muhimmanci, koda qarfe hud'u tayi nadare sun shirya tsaf, ana kiran sallar farko na asuba suka silale suka bar garin bayan baba ya ajiye wata takarda adaidai bakin qofar gidan idan anshigo daga ciki..
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[8/17, 10:19] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
_Barakallahu lakum😍 naga comment d'inku kala kala akan tafiyar iyayen Rashida, Wanda mafiya yawancinku basu so hakan ba kuma beyi masu dad'i ba, Karku manta sau da yawa ALLAH kan tsarowa bawa wata qaddara arayuwarsa yayin gujewa wata qaddarar tasa. inbaku manta ba iyayen Rashida mutanen qauyene basuda zurfin tunani da hankaltar cewa zamansu agarin shine daidai domin akowane lokaci 'yarsu zata iya dawowa idan tana raye kuma sune nafarko da zata fara nema, damuwarsu d'aya shine, fita daga cikin halin quncin rashinta da suka shiga da kuma yanayin ciwon da suka fito daya kusa kaisu ga rasa rayukansu, A tsoron kada su sake fad'awa cikin qaddarar shiga wani quncin da zai jawo masu ciwon da yafi wancan yasa suka koma fad'awa cikin qaddarar rashin had'uwa da 'yar tasu, to haka abun yake ko a zahirance acikin yanayin rayuwarmu ta yau da kullum, alokacin da muke qoqarin gujewa wata qaddarar tamu to muna sake fuskantar wata qaddarace ta daban da ALLAH yarubuto muna acikin littafinmu, tabbatuwar wannan qaddarar akanmu shike tilastamu da aiwatar da abunda zai zamo silar wanzuwarta, idan mun duba, ko a musulunce ALLAH ya halastawa bawa idan yana cikin tsananin kunci da takurar rayuwa da yayi hijira daga garin da yake zuwa wani garin saboda yasamu sauqi matuqar ba annoba bace, don haka kuyi haquri👏 idan da rai da rabo Rashida zata sake had'uwa da iyayenta, abunda kawai banida tabbaci akai shine, a Ina?, Yaushe ne?, Awane lokaci kuma awane waje?,😍 Domin samun amsar sai kun jure bibiyarmu acikin wannan littafin, SANNU SANNU dai Bata hana zuwa....😍 Luv you guys fillah_💞
Page___50💎
Cikin sa'a sukayi nasarar ficewa daga anguwar ba tare da kowa ya gansu ba, daga su sai jikukunansu guda biyu na kaya da kuma 'yar jikka ta ratayawa irin ta maza dake sagale a kafad'ar baba suka nufi tasha, sunjima zaune abakin wani shago kafin baba yatashi yaje ya d'ibi ruwa a randar dake ajiye bakin qofar masallacin dake cikin tashar yayi arwala, Saida ya d'ibi wasu a buta yaje ya kaiwa umma itama tayi arwalar had'e da ciro sallayar da sukazo da ita cikin kayansu ta shimfid'a sannan yabar wajen da sauri jin antayar da sallar yana fad'in,
"Kibi jam'i maman Rashida Ina fitowa zamu shiga motar duk da muka samu tagama lodi."
Ana gama sallar addu'a kad'ai yayi yafito da sauri da sauri tare da tallabar jikukunan nasu dake gabanta yana fad'in. "Hanzarta maman Rashida naji motoci sun fara tashi."
Tofi tayi acikin hannayenta dake sama bayan tagama yimasu addu'ar ALLAH yazab'a masu wajen zuwa mafi alkhairi arayuwarsu had'e da shafawa sannan tamiqe tanad'e sallayar tabi bayansa, suna isa motar Niger na d'agawa wacce ita yaso su samu don d'azu yana arwala yaji drivern motar nafad'in passinger biyu ya rage masa tacika, sai gashi kafin ya d'oko kayan nasu su iso wajen har ansamu ciko, shiru yayi had'e da ajiye jikkunan yana kallon umma da sai yanzu ta ida qarasowa wajen,
"Ai har motar tacika, kingata can yanzu tawuce" yafad'a cike da damuwa don baya son abunda zaizo ya dakatar dasu daga tafiyar wanda hakanne yasa ma ya kasa sanar da d'an uwan nasa.
Murmushi tayi tare da cewa, "ka kwantar da hankalinka, inda tanufa qilan zuwanmu can d'in ba alkhairi bane."
"Hakane kuma."
Yabata amsa tare da nufar rumfunan da motocin kowace jaha ke tsayawa lodi, duk motar daya duba bai wuce yaga mutum biyu ko ukku aciki har yawuce kusan motocin jahar, gombe, sokoto, katsina, adamawa da kuma bauchi babu inda yaga mota takusa cika balle tashi, har yajuya zai bar wajen yaji ana fad'in.
"Borno mutum uku, mutum uku borno."
Da sauri ya juyo yanufi inda motar had'e da cewa driver borno zaije.
"To kashiga, saura mutum biyu." Karan motar yafad'a yana sake d'aga murya yana fad'in "mutum biyu borno."
A sauri baba yasake matsawa kusa dashi yace "ai mu biyune nida matata."
Yana rufe baki saiga cikon mutum d'aya an samu, da d'an gudu gudunsa yaje yakira umma tare da d'oko masu jiku_ kunansu, miqa hannu umma tayi takarb'i d'ayar ganin sunyi masa yawa saboda yanayin yanda yake tafiya tunda ba lafiya yacika ba yayi saurin wucewa yana fad'in. "A'a kedai d'aga qafarki muje."
Suna zuwa akasa kayansu bayan mota suka shiga drivern ya tayar da motar suka bar tasha, suna hawa titi had'e da kama hanyar tafiya baba yarufe idanuwansa had'e da sakin wata irin ajiyar zuciya, kallonsa umma tayi itama tana ajiyar zuciyar tare da aza kanta saman kafad'arsa tana karanto addu'ar tafiya yayinda mutum ya hau abun hawa, wacce tafito daga bakin mafificin halitta kuma ya tabbatar mana da cewa duk wanda yayita alokacin daya hau abun hawansa zaiyi wata tafiya to ALLAH zaikaresa da ga sharrin duk wani abunqi dake cikin tafiyar da sharrin qarfe ko kuma had'ari, zai sanya tarin alkhairai masu d'imbin yawa acikin tafiyar tasa da yardar ALLAH.
_"ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBARU subhanallazi sahhara lana haza wama kunna lahu muqrinin, wa inna illa rabbina lamunqalibuun, allahummah Inna nas'aluka fi safrina hazal birri wattaqwa, waminal amali ma tarda, allahummah hawwan ala safarana haza wad'wi Anna bu'udahu, allahummah antasswahibu fis safri, walkhalifatu fil ahli, allahummah inni a uzu bika min wa'thaa'issafri, wa kaabatil manzwari, wasuu'il munqalabi fil mali wal ahli."_
Domin samun fassarar wannan addu'ar zaku iya duba littafin hisnil muslim, addu'a ta tis'in da shida (96) don nemawa kai kariyar ALLAH daga sharrace sharracen miyagun mutanen dake kan hanya da kuma munanan had'urran da sukayi yawa alokutan tafiye tafiyenmu,
Tana addu'ar hawaye nazubo mata a fuska, hannu baba yasa yagoge mata had'e da cewa.
"Kinsan inda muka nufa yanzu?"
Girgiza masa kai kawai ta iyayi tana mai tunanin yanda duniya tajuye masu daga farinciki Mai yawa na bayan shekaru zuwa baqincikin da basusan iya adadin lokacin da zasu d'auka dashi kafin yabarsu,
"Jahar borno muka nufa kuma Alhamdulillah akwai wani babban mutum dana sani acan abokin alhajin da nake saro takalma a shagonsane ana cemasa alhaji shu'aibu maiglass, muna yawan had'uwa dashi idan yaje wajensa ni kuma naje kaimasa kud'insa in amso takalmi, yanda alhajin kejin dad'in mu'amalar kasuwanci dani yasa wata rana ya had'ani dashi muka gaisa har yake fad'amun ai aminin sane yana zowa daga borno me shima yayi sayayar kayan glass nayin qofofin zamani, to tun daga lokacin duk yazo in muka had'u sai yayi mani alkhairi don babban mutumne sosai, kinga idan munje sai munemi gidansa kafin musamu inda zamu zauna.
"Shikenan duk da dai mutum bashida tabbas amma tunda ba muda wata mafitar ALLAH yasa hakan shiyafi zama alkhairi kuma yakaimu lafiya."
"Amin, ki kwantar da hankalinki in Sha ALLAH babu wata matsala."
"ALLAH yasa." Tafad'a tana share qwalla a idanuwanta.
••• ••• •••
Baffa Ali kam yayi sanyi sosai akan abunda yafaru, yayi dana sani mai yawa akan biyewa harkar mata da yayi wacce ta jefasa cikin halin qaqa nikayi, yayi nadamar shiga al'amurran Yaya hawwa Amma duk da haka yana jin tsanar baffa mai tsanani azuciyarsa bisa abunda yasa akayi masa shida iyalinsa a matsayinsa na d'an uwansa, hakan yasa tunda suka dawo yafita harkar kowa yana rayuwarsa shi kad'ai, baruwansa da kafatanin mutanen gidan acewarsa suma munafukaine tunda aka kasa samun wanda zaiyi belinsa acikinsu, had'uwa dubu kuwa idan zasuyi da baffa bazai d'aga Kai ya kallesa ba balle yasa ran zai gaishesa, dama dama baffa Usman yakan d'an saki jiki dashi sugaisa yawuce shima d'in ba sosai ba, Kuma hakan ko kad'an bai dami baffa ba saima addu'ar neman shiriya daga ALLAH.
Muneera kuwa tuni ta manta da babin ya nura rayuwarta takeyi kamar ba itace muneerar dake faman kukan son ya nura dare da rana ba, Amma tasha alwashin bazata tab'a sure ba inba saurayin birni d'an kwalisa ba irin ya nura, shiyasa takeci gaba da yiwa maqwabcinsu da yace yana sonta walaqanci kuma Inna ruqayya tagoyi bayan haka, saidai duk da haka yanzu basuda bakin fitowa tsakar gida suyi tijara kamar yanda suka saba gudun kada a mayar masu da jawabin abunda baffa yasa akayi masu wanda ita kanta tana kallon baffa amatsayin azzalumi wanda yaci amanar d'an uwansa, dama mai hali baya fasa halinsa.
••• ••• •••
Dr. Nura kuwa tunda safe yaso yin tafiyarsa zuwa kano amma yanda yaga Fatima takwana da tana fama da ciwon kai wanda dama lokaci zuwa lokaci yana taso mata yasa yafasa tafiyar, gashi sai kiransa akeyi wajen aikinsa akan wani emergency daya taso na gaggawa, Babu yanda batayi dashi ba akan yatafi kodon issue d'in Rashida amma ya kafe akan matuqar ba sauqi yaga ta samu ba babu inda zaije, hakan yasa tayi qarfin halin tashi taje tayo wanka tare da kiran mai aikinsu tace takawo mata abinci taci, bayan taci ya d'ebo mata magani tasha, a maimakon takoma ta kwanta sai tawuce part d'inta, zaune ta isko Rashida a palour rungume da little Nuraddeen tagama dama mashi madarar (NAN) da ake had'a masa da ita zata bashi.
"ALLAH sarki aunty yanzu nake cewa idan nagama bawa yaronki madara zanje naduboki da jiki, injin da sauqi ko?" Rashida tafad'a tana qoqarin d'aurama little Nuraddeen dake qoqarin kamo fidan