Showing 135001 words to 138000 words out of 260204 words

Chapter 46 - Sannu Sannu Complete Hausa Novel By Billy S Fari.txt

taya wannan yaron ya zamo jinin alhaji bayan jikinta da kamanninsa nafad'a mata akwai alaqa mai qarfi tsakaninsa da ita, wannan shine tmbayar da tashiga yiwa kanta tanaci gaba da kuka.

Acan waje kuwa kud'd'i Dr yaba baba yace yaje yakai umma asibiti adubata saboda bai kamata ta zauna da zazzab'in ba tunda ba'asan meke damunta ba.

Godiya yayi masa sosai sannan yakoma cikin d'akin ya d'auko little daya isko lafe ajikinta yana kallo yanda take kuka.

Bayan Dr nura yawuce ya taimaka mata tashirya yana yimata fad'an tacire damuwa aranta kar azo ace itace keneman yimata barazana a lafiyar jiki sannan suka wuce asibitin.

Basubar gidan ba sai bayan isha'i ammie tarakkosu har part d'in hajia nafeesa don su gaisheda dady tunda a part d'inta yake.

Dr nura yafara shiga kafin su ammie da Fatima su shigo suma yana zaune shida hajia nafeesa da yaranta suna kallon wa'azin shaikh Ahmad tijjani Yusuf a tashar Sunnah tv, dama matuqar yana part d'inta to tashar ake kalla gaba d'aya saboda tarbiyar yaransa, idan kuwa baya part d'in basuda aiki sai kallon tashoshin waqe waqe da cartoon,

Sallama d'auke abakunansu suka shiga aka amsa masu.

Yaranta ko gaisuwa Babu suka mimmiqe zasu shiga d'akunansu dady ya katsa masu tsawa.

"You stupid, bakuga mutane bane zaku shige baku gaishesu ba? Maza kudawo kugaisheshu." Yafad'a ransa a b'ace, kumbure fuska hajia nafeesa tashigayi tana binsu da harara har yaran suka duqa suka gaishesu suka tafi,

Ita dai ammie naganin haka tagaida dady tare da d'aga wayarta da ake kira tafita don bazata juri walaqanci ba ko kad'an,

Gaisheta dr. dasu Fatima sukayi ta amsa ciki ciki tana wani hurar hanta, Dr ya d'auke kansa daga kallon da yake yimata zuwa ga mahaifinsa yace.

"Am dama dady Rashida ce tazo gaisheku, kullum tana son tazo ALLAH bai yarda ba sai yau."

"Af ikon ALLAH, maman little Nuraddeen kuke kiransa ko wa?"

"Eh baffa."

"ALLAH sarki, sannu kinji Rashida, ayita addu'a ana jurewa kowace irin jarabawa in sha ALLAH komi zai zama tarihi."

"Hajia nafeesa kinga maman wannan yaron da kike tambaya kwanaki kina ganin Dr nashigowa tare dashi."

"Au sannunki, ai nazata wlh agidan reno suka d'aukosa har ina cewa ALLAH dai yasa ba shege bane."

Da sauri Dr suka d'ago kai su duka suna kallonta kafin dady ya girgiza kai cike da takaici yace.

"Nafeesa kenan, to bahaka bane, da uwarsa..." Kafin yaqarasa yaji tace

"Ai to baza'a gane hakan ba tunda ba'asan kowaye uban sa ba, Ina tsintar uwarsa akayi ko?."

Bata qarasa ba ya katsa mata tsawa had'e da cewa ta tashi tabashi waje.

Bayan tatafi dady yayita ba Rashida haquri kamar zaiyi kuka ita kuma tanuna ko ajikinta tunda tasan yanada ubansa, kawai dai dole zataji ba dad'ine ko kad'an, Fatima kuwa harda hawaye tana ganin da ace tana haihuwa baza'a tab'a jifarsu da zuwa gidan reno d'auko d'a, juyowa yayi gareta yaci gaba da cewa. "Fatima kada kibari kalaman auntynku suyi tasiri azuciyarki, ALLAH shi yake badawa bai manta daku ba in sha ALLAH jikina nafad'amun rabonku na kusa kusa domin akoda yaushe bamu cire qauna ga rahamar ALLAH ba, don haka kuyi haquri, kuyi haquri kunji ko?"

K'wafa Dr yayi tare da miqewa yafita ransa ab'ace, dama shiyasa tun farko baya shiga sha'aninta ko kad'an saboda gujewa irin wud'annan matsalolin, dama albarkacin mahaifinsa takeci amma daga yau tagama.

Sallamar Fatima yayi yarage daga shi sai ita da kuma little sannan yakira hajia nafeesar tafito daga d'aki, nuna mata kujera yayi ta zauna tana wani shashshan magani yace.

"Nafeesa kinsan ALLAH."

"Eh" ta amsa masa ciki ciki.

"Wlh idan baki ba yarinyar nan haquri ba bisa abunda kika jefeta dashi narantse da ALLAH abakin aurenki kenan!" Da sauri Rashida tad'ago kai had'e da cewa.

"A'a dady wlh babu komai nahaqura, ni batama yimun laifi ba idan ma tayi naya..."

Bata qarasa ba sanadiyar juyowar da yayi fuskarsa a d'aure ya d'aga mata hannu da sauri tayi gum takama bakinta.

"Zaki iya zab'an duk abunda yayi maki arai, amma hukuncin da nayanke yana nan babu ja da baya,"

Har zai miqewa yafita yaji muryar hajia nafeesa tace.

"Kiyi haquri." Ciki ciki tana Mai jin wata iriyar tsanar Rashida da d'anta aranta.

"Jeki Rashida, ALLAH yayi maki albarka." Yafad'a tare da ciro kud'i da batasan ko nawa bane yamiqawa little a hannu.

Bayan tafita yakalli hajia nafeesa yace. "Kiguji duniya nafeesa da qyalqyalin dake cikinta, wannan rayuwar da kika d'auka bamai b'ullewa dake zuwa ga kyakkyawan qarshe bace shiyasa nake qoqarin aduk lokacin da kika tozarta wani agabana innuna maki kuskurenki saboda ko meye yazo maki da sauqi."

"Amma alhaji.."

"Rufemun baki." Yakatsa mata tsawa had'e da ficewarsa.

Lokacin da Rashida kuwa tafito ta samesu tsaitsaye ammie nabasu haquri akan abunda yafaru don taji komai da kunnenta, haquri tasake ba Rashida sannan tace.

"Son yakamata suje sugano umma kafin suwuce."

"No... ammie tun d'azu suka wuce asibiti ita da baba saidai idan munqara dawowa."

"Ok son kuyi haquri don ALLAH kasaki fuskarnan taka, bana son inganeku cikin damuwa kinji ko 'yatah kuyi haquri." Murmushi sukayi kusan atare sannan sukayi mata sallama zukatan kowanensu ba dad'i kafin su shiga mota subar gidan, motarsu nafitowa daga cikin gate napep d'insu baba nawutowa sun dawo daga asibitin, kusan saida sukayi clashing da juna sannan napep d'in ta ajiyesu sukuma suka wuce.

πŸ€ͺ *Target bend*πŸƒπŸ»β€β™€οΈ




*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*πŸ‘πŸ˜­
[11/14, 22:52] Billy S Fari: πŸšΆβ€β™€οΈπŸšΆπŸ»β€β™‚οΈ *SANNU SANNU*πŸšΆπŸ»β€β™‚οΈπŸšΆβ€β™€οΈ
πŸ’Ž _Bata hana zuwa..._πŸ’Ž


_WRITTING BY:_ *BILLY S FARIπŸ’Ž*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*πŸ’‹

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*πŸ’ž

*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*πŸ’–

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❀️

Page___63πŸ’Ž

Tunda suka hau titi babu wanda yacewa wani uffan har suka isa gida, kowanensu ya lula duniyar tunani akan yanda rayuwa zataci gaba da tafiya dasu bisa linzamin qaddarar da suke akai, musamman Dr nura da yake ganin gaba d'aya cinmutuncin da matar mahaifinsa tayi akansa yaqare, don haka akwai buqatar ya d'auki matakin yiwa abun tufqa tunkafin yayi tsayi.

Gaba d'aya sai sukajidaren ranar yazo masu abai baice, hatta 'yar firar da suka sabayi a kowane dare kasawa sukayi kowane ya shige part d'insa ya kwanta, haka ma da safe kusan yanda suka kwana haka kowane yatashi fuskarsa babu wata walwala har suka zauna wajen karyawa ba wanda yace wani abu bayan gaisuwa, miqewa Rashida tayi bayan tagama nata Karin zata wuce d'akinta taji muryar Dr yace.

"Koma kizauna maman boy ina son zamuyi magana dake."

Bamusu takoma ta zauna yayi gyaran murya had'e da cewa.

"Ina mai baki haquri bisa abunda yafaru jiya, da nasan hakan zata kasance wallahi da ban d'aukeki nakaiki gidan muba, gashi hakan da nayi na neman sauya walwala da kuma farincikin gidannan gaba d'aya, naroqeki kimanta da abunda yafaru domin haka zaisa rayuwarki taci gaba da inganta kamar yanda tafaro, tabbas Bata kyauta ba data cutar dake ta hanyar munanan kalamanta batare da tasan koke waye ba! kuma ko kad'an batayi maki adalci ba a matsayinta na uwa da tasan irin zafin da akej idan aka aibatawa mutum d'a, Amma duk da haka Ina nema mata afuwa a matsayinta na matar mahaifina, ina tabbatar maki da hakan bazata sake faruwa ba in sha ALLAH kinji."

"Uncle kenan! bazance banji komai araina ba akan abunda yafaru jiya kasancewar yazamo silar jefaku cikin halin da tunda nake zaune daku ban tab'a ganinku acikin koda makamancinsa ba, ba ina damuwa bane akan abunda tayi mani ba, kawai damuwata tabayyana ne adalilin yanayin da nake kallon fuskokinku aciki, kalamanta abune da babu tushe, asali ko kuma inganci aciki da har zan damar da kaina. amma shi b'acin ranku da kuma damuwarku tamkar wutace dake cin zuciyata idan Ina ganinku acikinsa wanda natabbata bazata dena ciba har sai lokacin da naga farinciki yabayyana fuskokinku, kuyi haquri domin nima nazamo sila wajen sa ajefeku da kalaman da suka cutar da zukatanku."

Kallon Fatima Dr yayi had'e da cewa.

"Kijifa abunda take fad'a!, taya za'ayi tazamo silar cutuwar zukatanmu bayan laifin ita akayiwa."

"Hakan nafaruwa kuwa Dr, musamman ga zukatan da basu fiye son kansu ba kuma suke kallon damuwar wasu amatsayin tasu, don haka damu da ita mu manta da komai mu fuskanci gabanmmu."

"Shikenan ALLAH yaqarawa zukatanmu haquri kuma yabasu girman d'auke duk wata jarabawa da kuma gwagwarmayar rayuwa."

"Amin ya rabbi."

Suka fad'a tare suna murmushi, nan suka dasa rankon sabuwar firar da basuyi ba jiya,

Bayan wata uku little yaqara wayau Rashida ta yanke shawarar yayesa saboda ganin irin girma daya taso masa kuma babu abunda bai iya ciba. Ana saura sati d'aya tayayeshi suna zaune ita da fatima tace.

"Aunty nifa wani sati cire yaronki zanyi amama, ALLAH nagaji da tsutsannan da yakeyimun."

"Kai maman boy, shekararsa d'aya da wata d'aya fa kenan?"

"ALLAH nagaji aunty zalina yakeci sai yayita cizona da haqoransa masu kaifin tsiya sai kace reza." dariya Fatima tayi had'e da cewa.

"Aikuwa baki isa ba, sai yayi 2years tukuna, haquri kawai zakiyi kema wayasan yanda ummanmu tayi fama dake."

"ALLAH sarki umma, ai da zaku had'u kika tambayeta Allah zata fad'a maki bata wani sha wahalar renona ba saboda da kanta take fad'a cewa ni 'yar baiwa ce."

"ALLAH!?" Fatima tafad'a tana dariya hadde da zaro idanu, gwaggo mai aiki dake goye dashi tana mopping tace.

"Gaskiya hajia ta yaye yaron nan tunda ya iya cin komai, tubarkallah qato dashi gayanan yana neman karyamun baya,"

"Laaa...gwaggo har dake?, Zo kawomun yarona indai goyone daga yau yadena son naki."

Qarar wayar rashidane data jiyo rurinta ad'aki ya katse firar tayi saurin miqewa don ta d'auko gwaggo tace

"A'a Bari nad'auko maki, Amma cin hancin yaye d'an hajia ne zan baki."

"Aikuwa angama gwaggo." Rashida tafad'a tana dariya

"Ai sai kuyi bari abbansa yadawo zan fad'a masa ai."

koda gwaggo takawo mata wayar har tayi missed call, murmushi tayai ganin lambar Yaya Maryam da kullum saita kira idan bataji takirata ba taji ya lafiyarau take ita da litte, saurin kiranta tayi don kada tasake kiranta bugu d'aya ta d'aga.

"Rashida ya kike? kuna lafiya."

"Lafiya klwa gwaggo ya wajensu baba balarabe?"

"Kowa lafiya Rashida, Ina maigida."

"Gashinan ya hayewa gwaggo mai aiki baya, dama yanzu nake zancen zan yayesa da aunty saboda mugun tsotsans."

"Kul! Karki fara, kibari koda wata biyar ne nan gaba yad'an qara qwari kinji nafad'a maki ko?" 'bata fuska tyi kamar zatayi kuka had'e da cewa.

"Kai gwaggo kinga yanda yazama wani tulele dashi, ALLAH bazan iya da tsutsar saba."

"Cit d'inki, kenan ummanki sau uku tana zancen yayeki amma saboda qulafucin nono saita fasa har saida kika shekara biyu cif sannan ta yayeki, shima d'in haka kika dingayi kamar zaki mutu duk kikabi kika tada mana da hankali."

"Nid'in gwaggo!?" Tafad'a tana kallon fatima dake jin duk abunda Yaya Maryam kefad'a tana gumtse dariyar dake neman kucce mata.

"Ked'in fa, some some nawa kikayi?, Banda ALLAH yayi zakinfita ai da yanzu saidai labarinki, don haka kibari sai nan da wata hud'u idan ALLAH yasa munada rai."

"Shikenan gwaggo, ya labarinsu ummana?"

"Kiyi haquri Rashida har yanzu bawani labari akansu, amma munanan muna addu'a ALLAH ya karkato hankalinsu sudawo gida."

Wata gauruwar ajiyar zuciya tayi kafin suyi sallama tana dubon inda Fatima ke zaune, kashe mata ido d'aya tayi had'e da d'aga mata gira tana dariya tace.

"To 'yar baiwa ya akeyine?."

"Ummaaa!.." tafad'a cikin sigar damuwa.

"ALLAH sarki, ummanmu gaskiya baqaramin so da tausayinki take ba, amma ke shine kike so kicuci yaronmu, to ALLAH yakama ki duk naji abunda Yaya Maryam tafad'a, ashe haddasu some some akayi akan nono, oh ni Fatima! gaskiya umma taga jalala." taqare maganar had'e da tintsirewa da dariya tana tafa hannuwa, tayi hakanne saboda tadaqile tasirin damuwar dake shirin ziyartar Rashida akan zancen rashin dawowar iyayen nata da suka gama da Yaya Maryam.

Binta da kallo Rashida tayi tana murmushi, a zuciyarta tana mai addu'a, Allah ya dawwamar da irin wannan farinciki da Fatima ke ciki atattare da ita nahar abada.

Dr kuwa tunda yaji zancen Rashida na Shirin yayen little shima yafara shire shiren nema mata takardun shedar kammala primary, dama sun tab'a maganar karatun da ita tafad'a masa primary ne kawai tayi har take basu labarin yanda tahad'u da abban little a sanadiyar rashin son karatunta sunata dariya, bai wani sha wahalar samun takardun ba saboda yanda komai ya lalace zaka iya samunsu matuqar akwai kud'i atare dakai, kafin kace me har yagama had'a takardun da cike mata form d'in shiga makarantar gaba da primary na wannan shekarar tare da taimakon Fatima batare da sanin Rashidar ba, akoda yaushe Rashida cikin farinciki take natakusa yaye little Nuraddeen tahuta da tsutsa ita kuma Fatima nayimata dariyar maida ita makaranta da suke shirinyi bada saninta ba, wanda ALLAH kad'ai yasan yanda za'a kwashe matuqar har yanzu tana nan akan bakanta na rashin son karatu.

Satin yaye little nakamawa tahad'a gaba d'aya sauran kayansa dake hannunta takaiwa Fatima suna tayi mata dariya ita da Dr.

"Ikon ALLAH, maman boy wannan wace irin korace haka akeyiwa takwara, anharhad'o komai nasa sai kace zai bar gari"

"Uncle sunanta kora da hali, gaba d'aya nayi handing over dashi, gashi ga mamarsa kar akoma cewa ansanni, yabarni inhuta abuna ko d'akina kada yakoma leqawa har sai jinin jikina yadawo."

"E'em kedai! karfa ayi haka bayan kwana biyu kice kinyi missing d'insa."

"Cab! Uncle little d'in?, Ai yanda take addabar rayuwata da daddare babu wani missing d'insa da zanyi."

"Kika ce?"

Tayi dariya kawai had'e da juyawarta tabar falon fatima nafad'in.

"Muna nan dake zakizo ganinsa muma muyi maki handing over."

Randa akayi yayen little kuwa ba qaramar rigima suka shaba duk daya saba kwana wajensu amma sai kace wanda aka fad'awa yayesa za'ayi haka yadinga yimasu kuka cikin dare, sunyi lallashi har sungaji amma yaqiyin shiru, idan tayi tagaji taba Dr shima yayi nashi lallashin amma kamar ana sake sake turashi,

ALLAH sarki Rashida tun tana iya sauraren kukan har takasa tasa pillow ta dad'e kunnuwanta amma bata dena jiba, tashi tayi tayi zaune tsakiyar gadon tanajin kukan nasa har cikin ranta batasan lokacin da itama tafashe da kuka ba, batasan meyasa ba ko kad'an bata iya jurar kukansa gashi bazata tab'a iya fita da sunan taje taduba saba, d'aga hannuwanta tayi sama ahankali tafara yimasa addu'a.

"Ya ALLAH Kai kake karb'ar addu'ar mahaifiya ga d'anta, ALLAH kasa masa dangana, ya ALLAH kamar yanda yabar nono na ayau ALLAH karabashi da duk wani musibar rayuwa tun daga qanqantarsa har zuwa girmansa, ALLAH kasa yazamo mai juriya da haquri acikin rayuwarsa kuma ka albarkaceshi kasa amfani mai tarin yawa acikin wanda yasha na tsawon wannan lokacin."

Tana gamawa takoma takwanta tana cigaba da saurarar kukan nasa, ahankali tafara jin sautin kukan nasa na ragewa har tadena ji gaba d'aya, ajiyar zuciya tayi sannan tagyara kwanciyarta har bacci b'arawo yazo ya saceta.

Haka sukayi ta fama dashi har kwana biyu duk da qarfin hali kawai ne Fatima keyi itama kullum da zazzab'i take kwana, amma saboda shi take jurewa, arana ta uku ne safiya nawaye koda Dr nura yatashi yaganta a qudundune cikin bargo jikinta sai faman rawa yakeyi,

"Subhanallahi, Fatima bakida lafiya ne?" Yafad'a yana yaye bargon, yanda yagata ba qaramin tayar masa da hankali yayi ba da sauri ya Ida cire bargon yatada ita had'e da rungumota ajiki yana tattab'a wuyanta da goshinta,

"Fatima ko ciwon kanne?"

Yafad'a arud'e da sauri ta d'aga masa kai had'e da cewa.

"Inajin sanyi sosai."

Yatabbatar da haka don gaba d'aya jikinta yayi zafi sai rawar sanyi takeyi,

First-aid d'insa yatashi ya d'auko yaciro maganinta na ciwon kai da take yawanyi ya b'alla mata yabata tasha ya had'a mata dana maleria sannan ya maida ita ta kwanta ya lullub'a mata bargo yana yimata addu'a.
_As'alallahul azhim, rabbil arshil azhim, anyashfiki, laa ba'asa d'ahurun in sha ALLAH_

Ya tofa mata had'e dayi mata sannu sannan yayi kissing d'inta a goshi yabar d'akin, bayan mintuna biyu yadawo ya d'auki little dake sharkar baccinsa hankali kwance dama haka yakeyi, ya hanasu bacci da daddare da safe kuma yayita sharkar abunsa har rana, yanufi wajen Rashida dashi yace tagyarashi zai kaishi wajen ammie Fatima batada lafiya, nan take Rashida taji ba dad'i aranta sai take ganin kamar rigimarshi ta haifarwa da Fatima rashin lafiya.

"Uncle baka ganin zai dami ammie sosai tunda baya bacci da daddare."

"Nooo..Bakomai ki gyarashi, ai taso akaimata shi tun farko mu mukaqi ganin zaifi sauqi tunda yafi sabawa damu, amma yanzu tunda ga dalili sai akaimata shi, koba komai zata sama mashi maganin da ake ba yara na yaye tunda mu bamuyi dubarar haka ba?"

"Shikenan uncle." tafad'a tare da karb'arshi agurguje tashiga shiryashi, koda yadawo d'auke da akwatinsa har tagama shiryashi yakarb'esa sannan yanufi wajen ammie dashi.

Satinshi biyu a hannun ammie kuma yana samun kulawa sosai wajenta da kuma umma da kusanma yayen awajenta yake, don matuqar dady na part d'in ammie to awajenta yake kwana, little kam har zazzab'i yayi shima kusan sau biyu amma Rashida bata tab'a zuwa dubosa ba saidai Fatima da Dr suje duk da har yanzu itama tana fama da zazzab'in, babu yanda fatima batayi da Rashida ba akan taje taduboshi don har saida aka kwantar dashi asibiti na kwana d'aya amma taqi zuwa.

Baba balarabe kuwa da aka sanar dashi safiya nawayewa yaje ya sanar da Yaya Maryam suka yanke shawarar zasuje ganinsa idan ALLAH yakai ranmu gobe,.....





*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*πŸ‘πŸ˜­
[11/14, 22:52] Billy S Fari: πŸšΆβ€β™€οΈπŸšΆπŸ»β€β™‚οΈ *SANNU SANNU*πŸšΆπŸ»β€β™‚οΈπŸšΆβ€β™€οΈ
πŸ’Ž _Bata hana zuwa..._πŸ’Ž


_WRITTING BY:_ *BILLY S FARIπŸ’Ž*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*πŸ’‹

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*πŸ’ž

*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*πŸ’–

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❀️

Page___65πŸ’Ž

Nanfa dady yayi gyaran murya had'e da cewa.

"Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah, inaga yakamata ace kowa yanemi waje ya zauna hakanan tunda ubangiji ya nuna ikonsa yanda yake so, alokacin da yake so kuma adaidai inda yake so, duk da dai azahirance wannan abun daya faru abun mamakine da kuma ban al-ajabi agaremu saidai bazai kuma hanamu fahimtar ko meye ke wakana awannan wajeba duba da kuma la'akarin yanda alokaci d'aya ALLAH ya dunqule ahalin da muke tunani biyu ne atare damu yakoma ahali d'aya, wannan abun farincikine da kuma murna agaremu, don haka ina mai neman alfarmar kowa yanemi waje yazauna ko don baqinmu da suka shawo hanya na tsawon awanni akwai buqatar ace sunci, sun


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login