Showing 99001 words to 102000 words out of 260204 words
Chapter 34 - Sannu Sannu Complete Hausa Novel By Billy S Fari.txt
yana fitowa ana fara kiraye kirayen sallar magrib yace.
"Nuraddeen mutashi muyi harma, kaji ankira sallah."
Miqewa Nuraddeen yayi ya zubowa baffa ruwa abuta shima ya zubama kansa sukayi arwala sannan suka nufi masallaci,
Bayan sun dawo ne suka tarar da baffa Usman bakin qofar gida riqe da ledar kwanonin abincin data zama dole kullum sai yasa ankawo masu daga gidansa ko kuma yazo da kansa yakawo masu, da sauri Nuraddeen yaqarasa wajensa had'e da gaishesa sannan yakarb'i abincin yayi cikin gida, fuskar baffa sake taqaraso wajensa shima yamiqa masa hannu suka gaisa yana fad'in, "agaida malan usmanu baban Nuraddeen sannu da zuwa kazo adaidai don yanzu nake tunanin inkiraka awaya."
"To gani nazo, ALLAH yasa kan wasu nerorine zaka bani in take." yafad'a cike da raha,sun jima suna zolayar junansu abun gwanin sha'awa kafin su qarasa shiga cikin gidan, inda suka hango tabarmar da Nuraddeen ya shimfid'a masu suka nufa suka zauna tare da aza wata sabuwar fira wacce mafi yawancinta duk akan maganar tafiyar Nuraddeen ce, a nan baffa ke sanar dashi maganar kud'in da yazo dasu d'azu wud'anda ya saida dabbobinsa, sosai baffa Usman ya nuna masa rashin jin dad'in hakan da yayi tare da sheda masa cewa akwai wasu shima ahannunsa da yake da niyar bashi yaqara amma saidai basuda yawa dubu talatin ne.
Nan dai sukaci gaba da firarsu har kusan qarfe goma da rabi sannan baffa Usman yawuce,
Bayan wucewarsa ne Nuraddeen yakawo masa abinci yaci shima suka d'an ta'ba fira sannan suka bid'in inda zasu aza awazzansu, a lokacinne baffa ya d'oko wayarsa da niyar sanya masu karatun baqara don haka yakeyi har safe saboda ta d'ebe masu kewa, sai gashi yaga kusan 5missed call kuma duka na inspector najida ne, har ya danna lambar zai kirata sai kuma yayi saurin katsewa saboda agogon wayar daya nuna masa kusan qarfe 11:45 na dare, don haka bazai yuyu yakirata awannan lokacin ba duk da dai yaso yaji dalilin kiran nasa da tayi don yasan akwai wani abu mai muhimmanci da aka samu wanda shine yahaifar da kiran data yimasa, fasa kiran nata yayi har zuwa gobe da safe idan ALLAH yakai mana rai.
_Kuyi haquri dis days sai ahankali abubuwa sunyi yawa kawai Ina squatting ne nad'an yimaku typing._
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*ππ
[8/17, 10:19] Billy S Fari: πΆββοΈπΆπ»ββοΈ *SANNU SANNU*πΆπ»ββοΈπΆββοΈ
π _Bata hana zuwa..._π
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARIπ*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*π
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*π
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*π
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*β€οΈ
Page___47π
Saida ya miqa jaririn wajen Fatima ita kuma takaima Rashida shi sannan yakoma ya d'auki malamin ya maidashi gida, abakin qofar gidansa ya tsaya cikin mota bayan ya ajiyesa yana jiran yakawo masa magungunan da za'afara yiwa Nuraddeen amfani dasu, ba'afi mintuna biyar ba yafito riqe da wata leda 'yar madaidaiciya, bud'e motar yayi had'e da zaunawa a mazauninsa daya tashi yana kallon gefen driver inda dr. nura yake zaune yafara yimasa bayani,
"Dr. Ga wannan ruwan, ma'u kalne, za'a dinga zubasu kullum cikin ruwan wankansa marfi d'aya aduk lokacin da za'ayi masa wanka, sai wannan shi kuma garin hulbane, za'a d'ebi kamar qaramin cokali d'aya sai asaka marfi uku na wud'an can ruwan ma'u kal d'in akwab'asu waje d'aya sai ashafe masa jikinsa dashi kafin ayi masa wankan har na tsawon mintuna bakwai zuwa takwas lokacin maganin yabushe sai a mummurje masa shi sannan ayi masa wankan." ya qare fad'a yana nunama Dr. nura wata gora aciki dake cikin ledar tare da wani qullin garin hulba d'aure ga leda baqa, wasu qananan kwalabe guda biyu ya sake nuna masa had'e da cewa.
"Su kuma wud'annan man zaitun ne da kuma zaitu lawwiz (man tafarnuwa), za'a had'asu waje d'aya adinga d'iga kad'an a hannu ana yimasa man shafawa dashi bayan angama masa wankan sai kuma wannan, shi kuma garin habbatussauda ne, za'a dinga samun gawashi (garwashin wuta) idan angama shafa masa wud'an nan mayukkan dana gama yimaka bayani sai a turara masashi kafin asa masa sutura, sai wannan kwalbar ita kuma"
Wata doguwar kwalbace ya d'ago yana nuna masa sannan yaci gaba da cewa, "wannan zallar Zuma ce 'yar misra aciki don tafi kyau, garariya ce ita babu wani surki acikinta, adinga lasa masa ita tunda sassafe kafin yasha nono, sannan ana bashi ita akai akai ko yaushe, hakama idan zasu kwanta lokacin kwanciya ta tabbatar an lasa masa ita ko kad'ance yasha."
Wata baqar ledar ya sake ciro daban da wani ganye acikinta had'e da garin magani da kuma kwalbar man zaitu simsim (man rid'i) ya miqa masa.
Kariqe wannan daban mahaifiyarsa zata dinga amfani dashi, wannan ganyen na na'a na'a ne, zata tafasashi sai tasaka cokalin zuma d'aya acikin ruwansa kofi d'aya, tasa wannan man rid'in shi kuma marfi d'aya tajuya sosai tasha da d'an zafinsa, wannan garin maganin shima zata dinga d'ibarsa tana turare jikinta dashi, in sha ALLAH sukad'ai zasuci gaba da karya duk wani mugun sihiri ko tsafi ko shafuwar aljanu ga duk wanda ya kiyaye amfani dasu, ta lizimci sauraren karatun alqur'ani kuma idan son samune a qauracewa duk wasu kalle kalle har zuwa lokacin da yaron zai samu lafiya, akula sosai, kada adinga barin yaron shi kad'ai domin hakan zai iya dawo mana da komai baya tahanyar sake qoqarin cutar dashi da zasu iya samun damar yi, balle yanzu da suke a fusace, kad'an suke jiran koda 'yar qaramar damace su sake samu don d'aukar fansar hanasu cimma burinsu da akayi, don haka akula sosai kada asake ayi wasa da hakan."
Malamin yaqarasa maganar yana miqawa Nuraddeen gaba d'aya ledar daya zo da ita, karb'ar ledar yayi sannan yamiqa masa hannu sukayi misabaha yana qara yimasa godiya sosai.
"Ba komai Dr. Ubangiji ALLAH dai yasa mudace, mutanene yanzu basuda d'igon tausayi da imani ko kad'an azuciyarsu inba guda guda ba, badon haka ba me wannan d'an qaramin halittar yayi daya isa ace ancutar dashi?"
"Abunda na dad'e kenan Ina mamaki malan, yanda na lura da irin wahalar da yaron ke matuqar sha bakad'an ya girgizani ba, mun kwashe kimanin watanni uku a asibiti ana abu guda amma babu wani sauyi da aka samu, wannan dalilinne yasa da yayata hajia maijidda tazo dubasa take bani shawarar mukoma gida dashi anemi maganukkan musulunci wataqil ALLAH zaisa a dace, dama kuma ni tuntuni na gama yanke wannan shawarar araina don haka kawai sai naji naqara samun qwarin guiwar yanke wannan hukuncin kuma alhamdulillah ga dukkan alama za'ayi nasara."
"Dama haka abun yake, wani lokacin maganin cuta na tare damu ko ince akusa damu amma saboda yanda muka bawa asibitocinnan muhimmanci fiye da komai saimu barsu muje can muyita shan wahala, muyita kashe kud'ad'enmu a banza bayan ALLAH ya halasta mana neman kowane irin magani aduk inda yake matuqar babu shirka aciki ba wai muce ala dole saina asibiti ba."
"Tabbas hakane malan, ubangiji ALLAH yasa mudace."
"Amin ya ALLAH"
"Malan nawane kud'in maganin?"
"Dubu talatin ne gaba d'aya amma idan wannan yaqare za'a dawo a karb'i wani, sau uku za'a karb'a hacikin wata uku shikenan angama.
Ciro kud'in yayi yamiqa masa tare da sake yin godiya sannan malan yafita shi kuma yaja mator yabar wajen,
Kamar yanda malamin yayi masa bayani haka yayiwa Rashida da Fatima bayani, sannan yaroqesu da su kula sosai kada suyi wasa da maganin nasa, maido kallonsa ga Rashida yayi yace.
"Maman baby aduk lokacin da zakiyi wani abun kitabbata kin kawosa wajen fatima, kada ki kuskura kibarshi shikad'ai kinji ko?."
"In Sha ALLAH."
Tafad'a had'e da sa kuka tana mai yimasu godiya bisa kulawa da taimakon da sukeyi mata, aranta tana mai tabbatar da cewa sunyi mata halaccin da har tamutu bazata tab'a mantawa dasu ba kuma bazata iya biyansu abunda suka yimata ba
β’β’β’ β’β’β’ β’β’β’
Baba da umma kuwa duka sun samu sauqi sosai don babu inda baba baya zuwa saidai har yau hannunsa da qafarsa basu koma daidai yanda suke ba, babu wani cowo dake damunsu yanzu inba rad'ad'in rashin 'yarsu da kuma tunaninta ba, daidai da sekon d'aya basu tab'a mantawa da itaba ko cire tunaninta aran suba, yanda baba yasamu lafiya sosai yasa yau da likitoci sukazo round aka basu sallama, baba balarabe na kasuwa umma takirasa ta sanar dashi, ba'afi mintuna goma ba sai gashi yazo da mota cike da farinciki suka kwashi kayansu tare da yima sauran majinyatan dake tare dasu sallama suna masuyi masu addu'ar ALLAH yabasu lafiya suma sannan suka wuce zuwa gida.
Suna barin assibitin motarsu baffa na tsayawa, nan wani dake jinyar d'ansa shima ya sanar dasu cewa d'azu aka basu sallama basu dad'e da barin asibitin ba, godiya yayimasa sannan ya juya yakoma cikin motar drivern ya tayar suka nufi yarimawa, adaidai bakin qofar gidan suka tsaya baffa yakira baba balarabe ya sanar dashi sunanan qofar gida sunzo duba baba shida iyalansu, cike da farinciki yabasu izini shigowa, da kansa yaje yatarbosu dag qofar gida had'e da yimasu iso zuwa ciki, hannu biyu suka tarbesu tamkar babu abunda yatab'a faruwa, inda nan take malan balarabe ya aika aka siyo masu ruwa masu sanyi kowa yasha sannan aka shiga gaggaisawa tare da yimasu umma yajiki, Inna Bilkisu kuwa yanda kikasan itace Yaya hawwa haka kurum taji tsananin kunyarsu bazata bari ta iya had'a idanuwa dasu ba sai wani sissinne kai takeyi, bayan an gama gaggaisawa ta soma jajanta masu akan abunda yafaru had'e da basu haquri, dukkaninsu babu wanda yace uffan inba aunty marwiyya da tun d'azu malan balarabe yakirata yasanar da ita batun sallamar, itace tafara zuwa ta gyaggyara masu gidan kafin su iso, suna isowa suka taddata har tagama tagyara ko Ina, cikin nuna yarda da qaddara tare da barwa ALLAH komai tace, "Babu komai Bilkisu, bawa ai baya tab'a kaucewa qaddararsa, munyi Imani da ALLAH ya qaddarowa Rashida haka kuma munasa ran tunda bawani yayi mata ba ko yaushene ALLAH zai bayyana mana ita."
Tana rufe baki sukaji muneera dake can gefe riqe da ledar pure water tana tsutsa tace,
"Kai ka kai, Wlh ALLAH kidena yiwa ALLAH qazafi, baruwansa acikin b'atan aunty Rashida, duk inna hawwa ce da innarmu da kuma baffana, su sukayi mata wannan abun tab'ata, Nima anso asakani aciki waccan inpeston (inspector) da suka kamamu aka kulle suka wankeni dama ni ban aikata komai ba sune sukayi, ya nura ne nake so kuma wlh ALLAH yanzu ma nadena sonsa, babu ruwana dashi ko ya nura?"
Tafad'a hannunta acikin kai tana susa tana kallon Nuraddeen da gaba d'aya kunya tagama rufeshi awajen ya sadda kanshi qasa, bashi kad'ai ba hatta su baffa Usman da sauran mutanen da sukazo tare sinne kai sukayi cike da wata irin matsananciyar jin kunya, da qarfi aunty marwiyya tajuyo tana kallon Nuraddeen ranta a b'ace tace.
"Dama Nuraddeen mahaifiyarka itace silar b'atar 'yar 'yaruwata?. Tirqashi billahil azhim rai baifi rai ba, dama nadad'e Ina zargin ko dasa hannunta aciki saboda yanda tanuna mana tsantsar tsanar da takeyi mata lokacin da muka kaita, naso tun alokacin na taka mata burki amma Yaya maryam tahanani saboda darajarka da mutuncin bayin ALLAH dake tare daku, to wlh bazata yuyu ba shari'a da ita sai tafiddo mana da yarinyarmu tun daganan ko har qarshen rayuwarmu, danqari maqari daga had'a sinnar ma aiki sai salwantar da rayuwar yarinyatabiyo baya.."
"Dakata marwiyya! Daga jin yarinya tafad'i magana saiki hau akai kifara wud'annan maganganu marasa dad'in ji, don ALLAH kiyi shiru mubi komai ahankali." Baba balarabe yafad'a yana mai kokonto akan maganganun, d'ago kai baffa yayi cikin karyewar murya yace.
"A'a Balarabe, kabarta tafad'i duk abunda ke cikin ranta hakan zaisa tasamu sassucin da mu muka kasa samu alokacin da muka gano gaskiyar wannan al-amarin, kudena kokwanto akan maganganun da waccan yarinyar tafad'a domin duka gaskiyane, nakasa sanin wane mataki zan d'auka a lokacin da abun yafaru shiyasa nayanke shawarar sanarda hukuma domin suyi bincike akan wud'anda nake zargi, wato matata mahifiyar Nuraddeen sai qanena Aliyu da kuma matarsa wato mahaifiyar waccan yarinyar, duk tsawon wud'annan watanni da aka d'auka sunacan kulle a hannun hukuma ana bincike wanda jiya bincikensu ya tabbatar masu da cewa akwai sa hannun iyalina aciki tare da wani boka da suka had'a kai akayi mata asiri, wanda hakanne yayi silar barinta gida, wannan shine gaskiyar abunda yafaru." Yaqare maganar yana goge hawayen dake zubar masa cike dajin d'acin abun aransa.
Cike da mamaki da al-ajabi su baba ke sauraren maganganun dake fitowa daga bakin baffa har zuwa yanzu daya dasa aya, cikin kuka umma tajingina kanta ajikin bangon d'akin tana fad'in.
_"Hazbunallahu wani'imal wakeel, qadarallahu wama sha'a fa'ala,"_
Baba kuwa wata irin ajiyar zuciya ya sauke had'e da cewa.
"Ba'a sauya tsarin duk wata qaddara da ALLAH yarubutowa bawansa, don haka malan Idris Ina roqonka da kaje kajanye wannan qarar daka kai ta iyalinka da d'an uwanka, yanzu muyi haquri tunda mai faruwa tariga da tafaru bazamu iya canxa komai ba saboda abun da duk akace ya had'a da sammu ko asiri to saidai ayi haquri abisa da addu'a domin itace makarinsa, indai ta b'angarenane malan Idris nayafe masu, _wa'ufawwidu amri ilallah_ inasa tsammanin ko yaushene ubangiji zai sake had'amu da 'yarmu kafin rai yayi halinsa, kaima Nuraddeen kayi haquri, nasan kaima kanada damuwar da dole ta d'ara tamu ko suzo d'ai, amma haqurin da addu'ar su zakayi kaima saboda sune kawai maganin wannan al'amarin." gaba d'aya kasa cewa komai baffa yayi, baisan wane irin karamcine baba take son kashesa dashi ba bayan halaccin daya yimasa na bashi 'yarsa, miqewa yayi yabi hanyar fita har yana harhad'a hanya Wanda da kad'an yafad'i saboda wani irin jiri daya d'ibesa, da sauri Nuraddeen yaje yakamasa, shi kuma baffa Usman tsayawa yayi yana taba su baba haquri tare da tabbatar masu da cewa yanzu haka yau hukuma zataje kaima bokan samame aka mosa kuma da yardar ALLAH za'aganeta.
"Hmmmm!" Kawai aunty marwiyya tafad'a tana jijjiga qafa tana hurar hanta alamun da sake d'innan, russunar da kai baffa Usman yayi agabanta yana kallonta yace, "ayi haquri, tabbas ba dad'i kuma ba'a kyauta maku ba, Amma insha ALLAH za'a bimata haqqinta yanda yakamata."
"A'a Usman Wai banace abar zancen ba, kuje asake bayin ALLAHn nan don giraman ALLAH." Baba yafad'a yana maitabbatar masa da abun har cikin zuciyarsa.
Daidai lokacin Nuraddeen yadawo bayan yakai baba daketa aikin sharar kwallah cikin mota, guiwowinsa ya ajiye qasa agabansu had'e da bud'e baki zaiyi magana amma sai kuka yaci qarfinsa, kallo umma kad'ai da yayi yasa yaji duk guiwowinsa sun sare, qwarin guiwar daya zo da ita yarasa haka kalamn daya tanada don qara basu haquri da nuna masu irin halin da take ciki duk sun kuccema bakinsa, ganin haka yasa wud'anda sukazo tare suka tashi suka fara fita d'aya bayan d'aya suna goge k'walla, a yau sunyi dana sanin sanin Yaya hawwa bisa wannan ta'asa data aikata, yau sun tabbatar da hukuncin da baffa yayi mata ya cancanta da ita koma fiye da haka.
Ganin kukan nasa yai qarewa yasa baba balarabe yace "haba Nuraddeen, kayi haquri muyita addu'a, wannan kukan bayada amfani, kaduba kaga yanda kabi duk ka lalace, karame kayi baqi tamkar ba nuran da muka sani ba, shin idan kai kayi hakan, muda muka haifeta ya kakeso muyi?"
Cikin dasashshiyar murayarsa da bata fita sosai yana sheshshekar kuka yace, "umma, baba, don ALLAH kuyafemun bisa wannan sakaci da nayi, kuyi haquri kuyafemun." Sai alokacin umma tad'aga ta kallesa tace.
"Bakomai Nuraddeen, ba sakacinka ya janyo hakan ba, son zuciyar mahaifiyarka da babu yanda zakayi da ita, banga laifinka ba ko kad'an don duk wanda ya kalleka yasan kana cikin irin yanayin da muke ciki banbancin kawai cine namu ya bayyana afili, amma kai nuqurqusarka yakeyi acikin jiki, tabbas muna kewar rashin Rashida da alhinin inda qaddara takai mana ita, to yazamuyi? Zafa mu iya rasa rayuwarta gaba d'aya koda tana agabanmu ne, basai ta b'ata ba, don haka muyi haquri har zuwa lokacin da ALLAH zai bayyanata kaji ko?."
Kallonta kawai Nuraddeen keyi yana auna girman imaninta da kuma yaqininta ga ubangiji, sai yakeji inama ace tasa mahaifiyar haka take, nasihohi suka shiga yiwa junansu na muhimmancin yarda da qaddara da kuma haquri alokacin jarabawa, inda nan baba balarabe yajawo masu qissar annabi yusuf da mahaifinsa annabi yaqub har qarshe, gaba d'aya sunji sun samu natsuwa aransu amma tsakanin baba da Nuraddeen kowane da abunda yake qisawa aransa don mancewa da zancen b'atan Rashida agaresu abune da bazai tab'a yuyuwa ba.
β’β’β’ β’β’β’ β’β’β’
A 'bangaren boka kuwa tuni komai y tsaya masa saboda yanda al'amurransa suka hargitse kuma suka lalace masa, duk wani siddabaru da surqulle da yakeyi yanzu ko yayi basayi, gashi shed'anun aljanun da yake huld'a dasu gaba d'aya sun qone lokacin daya turasu wajen Rashida saboda qarfin addu'o'in data dingayi, kullum cikin tashin hankali yake da fuskantar fushin miyagun iyayen gidansa da suka b'atar dashi suka tab'ar dashi don ko yaushe cikin saukar qur'ani almajiran da baffa yasa suyi masa addu'a suke, shiyasa tun ba'aje ko inaba ALLAH yafara gwada masa ikonsa ta hanyar tarwatsa duk wani laqaninsa na tsafi da Kuma qarfinsa, hatta iri b'acewar da yakeyi ada wacce itake qara qayata masa bokancinsa yanzu ta gagaresa, fitama wahalar yimasa takeyi saboda tsoron abunda kan iyazuwa ya dawo, ga yunwar cikinsa ita kad'ai ta ishesa saboda duka aljannun sundena yimasa hidima, Yauma yana kwance duk ya qanjame ya qara naqashewa akan wacce yake da ita yaji wata irin gumza da qara na nufato 'yar bukkar da take ciki, arazane ya tashi zaune don ya tabbata wannan qarar ta mugun aljaninsa ne daya tura ya hallakar masa da Rashida, da sauri yafito yana waige waige kafin cikin wata irin wahalalliyar murya yaji mugun aljanin nafad'in
"Sunnqonaniiiii, sun halakaniiiii, sun naqasa mani rayuwaaa kuma dole zaann d'au fansaaaa, hnnnnnmmmmmmm" gumza yakeyi sosai irin wacce ke nuna tsantsar wahalar da yake cikinta. Cikin wani irin qamari yariqo boka bargaji da ahalin yanzu bayada qarfi ko ikon ganinsa ya dinga bugasa jikin itatuwa yana jefosa qasa, bai qyalesa ba saida yaga yasome sannan yayi wata irin muguwar qara yana girgiza,