Showing 126001 words to 129000 words out of 260204 words
Chapter 43 - Sannu Sannu Complete Hausa Novel By Billy S Fari.txt
kuwa harda qaramin yaro (yusuf) dake fuskantar damuwa da kuma barazana ta dalilin hakan._
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*ππ
[11/14, 22:52] Billy S Fari: πΆββοΈπΆπ»ββοΈ *SANNU SANNU*πΆπ»ββοΈπΆββοΈ
π _Bata hana zuwa..._π
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARIπ*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*π
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*π
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*π
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*β€οΈ
Page___58π
Shiru Yaya Maryam tayi na tsawon daqiqu uku kafin tace.
"Hakan shine daidai, dama abunda nayita qoqarin lurar dakai kenan ka kasa ganewa, to amma batun cewa za'a mayar masu da yaro don yanke duk wata alaqa dake tsakaninmu kabarta don ni gaba d'aya bana buqatar jinmu yakoma zama atare dasu tunda basa da zuciyar imani."
Sun jima suna tattaunawa kafin yabar gidan har lokacin yanajin d'aci akan maganganun da baffa Ali yafad'a masa.
β’β’β’ β’β’β’ β’β’β’
Baffa nagama waya da malan balarabe yakalli d'an uwan nasa ya sakar masa murmushi cikin qarfin hali sannan ya juyar da kansa gefe, yana maimaita innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun aransa.
Dafa kafad'arsa baffa Usman yayi had'e da cewa.
"Meke faruwa ne Yaya?"
"Abunda Nuraddeen yayi gudun faruwarsa." Yabashi amsa had'e da juyowa suna fuskantar juna.
"Kayi haquri Yaya, dama dole hakan zata faru, mu auna kanmu a matsayinsu mugani, don haka dole zamu lallab'asu har su fahimcemu, ayanayin yanda damuwowi sukayi masu yawa kamarmu, abune mai wahala su iya riqe fushinsu alokacin da sukaji labarin tafiyarsa musamman idan sun jine daga bakin daya kasa yimasu kyakkyawan bayanin da zayasa sufahimta, shi kuwa rashin bayani acikin kowane al'amari shike haifar da husuma da kuma aikin dana sani, don haka dole muyi haquri har zuwa lokacin da zasu fahimcemu."
"Shikenan Usman, amma duk da haka mufara jaraba zuwa wajensa idan mun sauka."
Awa hud'u ta d'aukesu kafin su isa kano, ana ajiyesu tasha suka sake shiga motar da zata kaisu qauyen na yarimawa, cikin qananan daqiqu suka isa sukaci sa'a kuwa yana zaune bakin gida yana arwala suka yimasa sallama, bai amsa ba har saida ya gama arwalarsa ya d'aga kansa sama yayi addu'ar da akeyi bayan gama arwala sannan ya kallesu fuskarsa a sake ba yabo ba fallasa ya amsa masu salamar.
"A'a malan Idris, malan Usman sannunku da zuwa yanzu kuke tafe?." Yafad'a yana qoqarin ajiye butar da yayi arwala agefe, kallon baffa Usman baffa yayi kafin suji ya sake cewa.
"Kai Hassan kushiga ciki ku kawo ruwa a butoci magrib taqaraso ana batun tada sallah."
"Am sannunku da zuwa bari naqarasa masallaci kafin ku iso liman na batun tayarwa."
"To shikenan!"
Baffa yafad'a cike da mamaki a fuskarsa.
Basu sake Shan mamaki ba sai da suka fito sallah suka tarar da tabarma an shimfid'a a qofar gida da kwanonin abinci,
"A'a malan Usman ya akayi kukayi tsaitsaye? bisimillah kuzo kuzauna mana,
Gaggaisawa suka shigayi kafinsu baffa sufara qoqarin canza maganar izuwa asalin wacce takawosu, Amma ga mamakinsu sai sukaga kawai yajawo kwanoni abinci yana fad'in bisimillah malan idris muci abinci ko."
Babu yanda suka iya saboda yanada matuqar muhimmanci agaresu da bazasu iya yimasa musu ba, wanke hannayen su sukayi sukasa suka fara cin abincin tare har suka qare,
Bayan sun kammala, baffa yace.
"Don ALLAH malan balarabe kayi haquri ka sauremu, nasan an aikata maku ba daidai ba, amma kuskurene da babu wanda ya isa ya kauce masa, tabbas Nuraddeen yabar qasarnan saidai bada son ransa ba, nine natirsashi ganin yana shirin ruguza rayuwarsa, kuma dama ce wacce yasamu tun kafin wud'annan matsalolin su faru, ganin ba lallai bane ya sake samun wannan damar ba kuma ga yanayin da yake ciki yasa daya tirje akan babu inda zaije saboda yana tsammanin dawowar matarsa garesa wanda abune gaibi akan dawowarta yasa natilasta masa zuwa koya fita daga cikin halin damuwar da yake ciki."
"Hmmm malan Idris kenan!, Ai bance kunyi wani laifi ko kuskure ba, meye laifinku don kunyi qoqarin inganta rayuwar d'anku?, Meye laifinku don kunyi abunda zai sakaku cikin farinciki?, Ba kuda wani laifi don haka kumanta da komai, fatana d'aya muma ALLAH yabamu ikon d'aukar darasin da kuka koyamana muma mu inganta rayuwar 'ya'yanmu kamar yanda kukayi koma fiye da hakan.?"
Duk iya qoqarin da sukayi wajen ganin sun lurar dashi ya fahimci gaskiya hakan ya cutara daga qarshema cewa yayi.
"Don ALLAH da girmansa malan usman mubar wannan magana kada tajawo rugujewar sauran mutuncin dake tsakaninmu, d'anku dai ALLAH yabashi ilimi mai albarka mukuma ALLAH yatsare mana 'yarmu aduk inda take yabata juriyar shanye duk wani abu da zai nemi duqufar mata da farinciki."
"Amin" suka amsa masa dashi bayan sun sake bashi haquri sannan suka wuce zukatansu a dagule.
Bayan suntafi yakira Yaya Maryam lokacin tana zaune itada Rashida tana bawa little da sai qara wayau yakeyi nono,
"Na'am balarabe ya akayi? Duk lafiya dai kuke ko?"
"Lafiya klw Yaya, dama iyayen yaronnan mijin Rashida ne sukazo bada haquri...."
"Kaga rufemun babinsu bana son ji, ai Ina mumuka haifi aburmu kuma muka bashi aurenta ko! don haka yanzu mun raba, ko suna so ko basa so yazama dole yabawa Rashida takardar ta, bazata koma gidansa ba ko mutuwa zaiyi, shashancin baza da wofi." Yaya Maryam ta katsesa tana masifa,
Wata irin zabura Rashida tayi had'e da miqewa tsaye da kad'an little yafad'i, Yaya Maryam tayi saurin riqosa had'e da kashe wayar tana binta da wani mugun kallo mai cike da tarin tambayoyi, hankalinta atashe takalleta tana fad'in
"Mekike fad'a haka gwaggo!," da yake da haka suke kiran sunanta sannan taci gaba da cewa.
"Wai wa ake zancen zai sakeni?, Duk fa iya adadin kwanakinnan dana d'auka zuciyata cike take da mararinsa, idanuwa da kunnuwana cike suke da son ganinsa da kuma jinsa, kawai nayi shirune saboda kada kuga rashin kunyata tayi yawa amma Ina son na had'u da mijina, shine kuma kuke cewa sai ya sakeni?, Meye laifinsa?, Wne zunubin ya aikata da za'ayi yunqurin rabashi da ni?"
"Ungo nan marar kunyar yarinya." Yaya Maryam tafad'a had'e dayi mata daqquwa tanaci gaba da cewa.
"Ke wane zunubin kika aikata da uwarsa ta rabaki dashi, kin ganemun shashashar yarinya da batasan ciwon kanta ba, to bari infad'a maki wlh munfiso kimutu atare damu muyi maki sallah murufeki da mumaidaki gidansa uwarsa ta sake halakar mana dake, don haka tunwuri kiciresa aranki matuqar kina son muzauna lafiya dake kinji nafad'a maki."
"Haba gwaggo! Haba gwaggo wannan wani irin tsattsauran hukuncine zakuyi mana, inada yaqini akan tunda wannan jarabawa tasameni shima t yake cikin irin tashi jarabawar, don ALLAH kada kura bamu kodon yaronnan." Taqarasa maganar tana kallon little dake hannun ita Yaya Maryam d'in had'e da fashewa da kuka, har ga ALLAH Yaya Maryam taji tausayinta, Amma Babu yanda ta iya, wannan ita kad'aice hanyar da zasubi su kub'utar da 'yarsu daga sharrin uwar mijinta, wacce itama tanacan cikin mummunan yanayin da basuda labari akai, cikin dakewa da qarfin hali tace.
"Rashida kawai kuhaqura da juna, yaro kuma Allah shizai rayashi ko bakwa tare don haka kibi umurninmu kizauna lafiya."
Wani kukan ta sake fashewa dashi had'e da durqushewa qasa tana fad'in.
"Innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun, astagfirullah ALLAH natuba kayafemun laifukana, ya ALLAH ka sauqaqamun wud'annan jarabawowin rayuwa kada sufi qarfin zuciyata susa na sab'a maka," kallon yya matram data kauda kai tana goge 'yan guntayen hawayen da suka zubo mata tayi.
"Gwaggo baifa sakeni ba, taya zaku rabamu?, Karku manta dani harshi zamu iya sake ahiga wani hali idan kuka yimana haka, kunada iko akaina ammashi sam bai kamata kununa iko akansa tahanyar tirsasashi ya sakeni ba."
"Kedai zaki shiga wani halin keda kike ganin bamu isa mutirsasaki akan abunda muke ganin shine alkahiri arayuwarki ba, amma bandashi tunda har ya iya mance awane irin hali zaki shigaba keda abunda ke cikinki ba ya tsallake qasarnan ya tafiyarsa duk da yasan abunda yafaru dake Amma saboda ya gyara rayuwarsa kuma ya farantawa iyayensa yatafi yabarki acan duniyar da bai masan inda kike ba don ya inganta gobensa, ba kekad'ai da ba kyanan ba hatta mu iyayenki da yasan muna nan ya wofantar damu ta hanyar tafiyarsa batare da saninmu ba, wannan shi kike tunanin har zai shiga wani hali idan aka rabaku.? Tir da wannan banzan tunani irin naki" tana gama fad'ar haka tafice d'auke da little da yayi bacci a hannunta
Tunda tafara magana Rashida ta dasqare a inda take tsaye, shin Anya maganganun da gwaggon tata ke fad'a gaskiya ne ko a'a?, Ko kwanto tashigayi akan cewa habibyn nata zai iya tafiya acikin yanayin da ake na b'atanta kuwa?, Inaaa hakan bazai yuyu ba , tabama kanta amsa had'e da miqewa tana goge hawayenta, dole yau sai tahad'u da mijinta koda hakan na nufin za'a rabata da lumfashinta ne, dole ta qaryata d'ayar zuciyarta dake neman gasgata kalaman da gwaggo tafad'a mata.
'Dakin da anan ne aka bata tashiga ta d'auko mayafinta da sauri tanufi qofar fita gidan, kota halin qaqa yau tanada buqatar zuwa ta had'u da masoyinta kuma mijinta, sand'a tafarayi gudun kada taganta ta hanata zuwa har ta isa bakin qofar gidan
Tana fitowa taci karo da Fatima aqofar gida ita da Dr ya kawota.
Cikin farinciki Fatima tarungumeta tana fad'in "'yar halak ina zakije ne ko kema kinyi kewar tamune kamar yanda mukayi?"
Ganin yanda idanuwanta sukayi jajir saboda kukan da tayi yasa Fatima cewa.
"Subhanallahi, maman boy meyake faruwa?" Hakan yasa Dr fitowa daga cikin motar yana kallonta had'e da qoqarin rufe marfin motar, qarasowa wajensu yayi kafin yace.
"Maman boy lafiya?" Yanda sukaga ta sake fashewa da wani kukan yasa Fatima riqo hannunta zata shiga cikin gidan da ita da sauri taja baya tare da tirjewa.
"Don ALLAH uncle ku kaini naga ya Nuraddeen, Ina son ganinsa Ina so nahad'u dashi Amma su baffa sunqi amincewa,"
"Kamar ya Rashida?" Dr.nura ya tambayeta cikin rashin sani.
"So sukeyi su raba aurena dashi uncle kuma Ina son mijina, bayada laifi, akan abunda yafaru amma gaba d'aya sun kasa fahimtar hakan! don ALLAH ko sau d'ayane kataimaka akaro nabiyu ka had'ani da mijina kamar yanda kahad'ani da iyayena."
Maganar takeyi tana kuka had'e da game hannayenta waje d'aya,
Alama yayiwa Fatima dasu shiga motar sannan yajuya shima yashiga had'e da tayarwa, hannunta Fatima tariqa tabud'e gambun bayan motar tasata ciki sannan tarufe itama tashiga yaja motar sukabar qofar gidan,
"Ina muka nufa?"
Ya tambayeta adaidai lokacin da suka fito qauyen.
"Bebeji." Tabashi amsa ataqaice tana goge hawayen da suka jiqa mata fuska sharkaf,
Tafiya mai d'an nisa sukayi kafin su iso gaba d'ayansu Babu wanda kecewa wani uffan, tuqi yakeyi da hannu d'aya, hannun d'aya kuma ya azoshi saman tagar qofar yariqe hab'arsa dashi ita kuma Fatima sai faman jujjuya kwalin wayar dake hannunta takeyi wacce dama itace dalilin zuwan nasu saboda kewarta da tayi mata yawa kullum cikin zancenta ita da little yasa Dr yasiyowa Rashida wayar don suriqa gaisawa sai gashi sun tarar da ita cikin wannan halin.
Bini bini take juyowa takalleta cike da tausayi kafin Dr yamiqo mata wayarsa.
"Kamomin Yaya maryam"
Scrolling contact d'insa ta farayi har takai ga lambar Yaya Maryam da yayi saving da Ya Maryam kano takirata.
Bugu d'aya ta d'aga muryarta a hargitse.
"Dr."
"Na'am, anwuni lafiya.?"
"Lafiya klw, yanzu nake zancen kiranka na nemi Rashida sama ko qasa narasa saboda nayi mata fad'a."
"Karki damu tana tare damu, dama shine kiran dana yimaki."
"Tirqashi Amma wannan yarinyar anyi shashasha, shine zata fita fisabillahi bazata fad'amun ba, gaba d'aya duk tabi ta tayarmun da hankali?."
"Kiyi haquri, Bata kyauta ba gaskiya amma yanzun nan zamu dawo tare in Sha ALLAH." Kasancewar akwai cikakkiyar yarda tsakaninsu yasa bata damu sosai ba duk da abun ya b'ata mata rai, asalima gaba d'aya ranta bai kawo mata cewa Rashida zatayi tunanin zuwa tahad'u da Nuraddeen ba balle har ta taka da kanta taje garin nasu,
Koda suka iso angama sallar isha'i suka samu gefen wani shago sukayi parking,
Fitowa tayi cikin motar suma suka biyo bayanta har suka iso inda za'a iya hango gidan,
"Inane gidan Rashida?"
"Wancanne uncle." Tafad'a tana nuna gidan da yatsa.
"To muje ko."
"A'a uncle bazan iya ba, kawai ni shi kad'ai nake son nahad'u dashi."
"Bari to naje nasa ayo mani sallama dashi.," Yafad'a tare da tunkarar gidan.
Tsaye kawai take duk qafafuwanta sunyi sanyi tanaji tamkar basu imata, kallon anguwar takeyi d'aya bayan d'aya,
Kafin tahango Yusuf tafe yanufo inda suke gefen wani tsoho dake saida kalanzir saman d'an teburinsa,
"Lado abani kalanzir na naira ashirin?"
"Ahhh... yusufa d'an gidan yayansa nura, Wai ina yashige ne kwana biyu nadena ganinsa.?"
"Laah...ashe lado bakasan yaje qasar waje ba?"
"Kai yusufa!, Kace wlh."
"Wlh lado da gaske nakeyi."
"Kai ALLAH ban yarda da kaiba, shi nuran d'an mahaukaciya ne da zaibar qasar nan bayan matarsa da tsohon ciki tab'ata, sai kace wanda bedamu da ita ba,"
"To ni kabani kalanzir d'ina kada innar mu tabugeni, ai sai katambyi mutane kaji, yanacan yaje k'aro karatunsa."
"Tirqashi! Amma gaskiya be kyauta ba."
Kukan da Rashida ke qoqarin dannewa ne yaci qarfinta had'e da kucce mata.
Da sauri Yusuf daya miqa hannu zai karb'i kalanzir d'in da lado kemiqo masa suka d'ago kai tare jin kukan da suka jiyo agefensu.
"Yaa rasulu manzon ALLAH, ke baiwar ALLAH lafiya.?"
Lado yafad'a had'e da sakin kalanzir d'in yana kallon Fatima da Rashida dake tsaye hasken k'wan shago na yadosu, da hannu Yusuf ya shiga nuna Rashida don fuskarta bazata tab'a b'oye masa ba aduk inda tashiga, kasa magana yayi sai faman ja da baya yana fad'in.
"Aun..aunt..auntyyy.."
Yaruga aguje yabar wajen had'e da nufar gida yana k'walawa su baffa....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*ππ
[11/14, 22:52] Billy S Fari: πΆββοΈπΆπ»ββοΈ *SANNU SANNU*πΆπ»ββοΈπΆββοΈ
π _Bata hana zuwa..._π
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARIπ*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*π
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*π
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*π
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*β€οΈ
Page___60π
Tunda Rashida ta tabbatar da cewa Nuraddeen yabar qasar taji gaba d'aya komai na duniya ya tsaya mata, Babu abunda ke mata dad'i haka kuma babu abunda ke burgeta arayuwar duniya, kallo d'aya zakayi mata kafahimci tsantsar damuwar da take ciki saboda yanda duk tabi ta susuce, batada wani aike sai kuka, na safe daban na rana daban hakama na dare daban, duk tabi tarame tayi baqi, rashin iyayenta namatuqar damunta musamman yanzu da take cikin wani hali marar misaltuwa duk da kuwa Yaya maryam da baffa sunyi qoqarin nuna mata sun sauko daga dokin naqin da suka hau saboda yanda sukaga tana nemanfita hayyacinta sai dai aransu ba haka bane.
Baffa Usman kuwa da baffa basu san abunda kefaruwa ba , gaba d'aya sun maida hankalinsu kocokom ga nemawa Yaya hawwa magani har zuwa lokacin da aka d'ibar masu nazuwa a d'auketa, ranar nayi misalin qarfe sha biyu na rana motar asibitin ta dira abakin qofar gidansu baffa, lokacin suna tsaitsaye da alamu dama suna jiran dakon isowarsune tun d'azu, wasu ma'aikatan lafiyane su biyar da kuma wani mutum yasha suit, da alama shine babbansu, Saida suka gaisa dasu sannan baffa Usman yayi masu jagora zuwa cikin gidan inda Yaya hawwa take ya bud'e masu d'akin,
Cikin qwarewar aikinsu suka shiga cikin d'akin yayainda Yaya hawwa tayi wani irin kukan kura tayo kansu.
Ba qaramar wahala suka shaba kafin su samu damar rirriqeta tana keta wani irin ihu daya karad'e ko ina tana fizge fizge, sai da sukayi da gaske sannan suka sakata cikin mota suma suka shiga.
Wajen motar baffa yatako yana hango ta glass d'in motar yanda jami'an lafiya ke qoqarin yimata allurar da zatasa tayi bacci kafin su isa yasa hannu ya goge k'wallan da suka zubo masa a idanuwansa yana mai addu'ar Allah yabata lafiya, gaban motar ya koma saiti gefen driver inda babbansu yake ya saukar da glass d'in motar yamiqa masa hannu suka sake gaisawa yayi masu godiya sannan motarsu tabar wajen, ahankali dandazon mutanen da suka taru qofar gidan suka fara watsewa cike da tausayin halin da sukaga anfito da Yaya hawwa aciki saboda yanda tayi baqi da rama sosai fiye da tunani, inba wanda yasanta sosai ba bazaka tab'a ganinta kace itace ba.
Adai dai lokacin baffa Ali yadawo daga gona rataye da fartanyarsa a kafad'a yana rera 'yan waqoqinsa, yana hango su baffa Usman ya murtuqe fuska tunkafin ya iso har zai wuce abunsa sai kuma yadawo baya had'e da kallon gungun wasu yara dake tsaye abakin gidan.
"Kai me kukeyi anan naga kun had'e kanu kamar d'iyan awaki?"
"Wlh Yaya hawwa ce akafito da ita za'a kaita asibitin mahaukata abun gwanin tausayi."
Wani yarone daga cikinsu yafad'a hannunsa na tallab'e da kuncinsa.
Batare da baffa Ali yadamu da 'yan uwansa dake wajen ba yayi tsaki had'e da cewa.
"ALLAH yaraka taki gona, ai mun huta da gayyar tsiya kullum ana hanamu bacci ana tsorata iyalinmu da yaranmu,"
Juyowa baffa yayi ransa amatuqar b'ace yace.
"Karka damu Aliyu, SANNU SANNU ai bata hana zuwa...kamar dai yanda hawwa ke girbar abunda tayi haka kaima zaka girbi naka in alkhairi in kuma sharran."
Guntun tsaki yaja batare daya damu da abunda baffa yace masa ba yashige cikin gida yana cigaba da rera 'yan waqoqinsa...
β’β’β’ β’β’β’ β’β’β’
Kimanin satinsu Dr nura uku kenan da dawowa kano kawo Rashida, wanda sun jima hakanne sanadiyar Fatima data nace akan suyi zamansu sai qarshen wata saisu koma gaba d'aya tunda dama yakusa d'aukar hutu (annual leave), saidai hakan bazai yuyu ba saboda maganin little Nuraddeen da za'a karb'o masa gashi bayason idan yaje qarshen watan yasake dawowa har sai hutunsa yaqare,
Hakan yasa cikin satin da zasu koma kafin ranar tazo yayi sakko yaje borno ya karb'owa little maganinsa wanda idan yasha shine naqarshe,
Yana isa garin kai tsaye yawuce gidan iyayensa saboda akwai saqon da mahaifiyarsa tace yaje ya karb'owa Fatima na maganin da takesha,
Yana isa yatarar da mahaifinsa shima yadawo lokacin yana zaune kan dining table yana cin abinci, qarasawa yayi bakinsa d'auke da sallama yaje ya d'an russuna gabansa had'e da gaishesa.
Sake da fuska yamiqa masa hannu yana fad'in.
"A'a bokan turawa saukar yaushe?"
"Yanzunnan dady, mun sameku lafiya?"
"Lafiya klw dady, ya kasuwar."
"Kasuwa Alhamdulillah muna nan muna tattab'awa musanmman sabon shagon dana bud'e, abun Masha ALLAH gaskiya."
"ALLAH yaqaro bud'emai albarka, dady ammie fa?"
"Tana ciki, yanzu tabar nan inaga ankirata ne awaya."
Yana rufe baki tana fitowa, babbar mace ce mai cikar zati da kamala, farar mace ce sosai mai yawan fara'a da son mutane, kallo