Showing 207001 words to 210000 words out of 260204 words
Chapter 70 - Sannu Sannu Complete Hausa Novel By Billy S Fari.txt
kuma wlh kika sake kika bud'e baki akan wata maganar da ta shafemu saina tsine maki, jeki ni bazan iya zamaba don ALLAH baiyini da matacciyar zuciyar da zan zauna sai wani yabani ba."
"Assha innarmu, ai inaga duk tafiyar d'aya ce, dama dama wannan shida ba roqa zakije kiyiba, taimaka makine za'ayi acikin gidanki a matsayinki na uwa kuma matar d'an uwansu wanda sune dolenmu."
"Dallah tafi can, nadai fad'a maki ni kinga tafiyata."
Ta ficewarta tanata maseefa da ita, har takusa fita tadawo tanufi d'akin da baffa Ali ke jinya, tana kaiwa bakin qofar kafin ta d'aga labule yajefo wata gora dake gefensa tabugeta ga qwabri yana fad'in.
"Wane d'ebabben albarkane abakin qofar d'akinnan, tsinannin yara, d'iyan abun kware!, Magulmata da basuyi gadan mutunci ga iyayensu ba, wanene anan?"
Muryar Inna ruqayya yajiyo tana fad'in.
"Kai ka kai ka kai!, Ali yau maseefar taka akaina zaka saukar da ita?, Ni kake jifa da gora salon nima ka kaini kabaro gaba d'ayanmu mukoma zaune ana nunamu, to wlh kaga inda nayi nafasa shigowa, wannan muguwar gora dad'a so kakeyi ka karya mun qafa da ita, to nafasa shigowar sai anjima idan na dawo."
"Haba ruqayya, are bansan ke bace, nazata shashashun yarannanne masu kaida komowa da d'an kai suna regena, Yi haquri kiwhigo mana muyi magana."
"ALLAH da sai in tafiyata abuna, wannan ai mugunta ne" tafad'a tare da d'aga labulen ta tura kanta aciki, ai kafin ta ida shiga tayi saurin dawowa baya sanadiyar wani irin wari daya bugi hancinta tana fad'in.
"Nashiga uku ni ruqayyatu, Ali mezanji haka! Kardai kace bayan gidane kayi azaune yake wannan d'oyi haka!,"
"Haba kekuwa! ya za'ayi nayi bayan gida bayan Ina iya motsawa da kaina, ga yaronnan Yusuf kinsan bazai barni cikin qazanta ba."
"To nikam narantse maka da ALLAH bazan iya minti d'aya a d'akinnan ba saboda warin da yakeyi, yanzu ma ALLAH yagani ka cuceni da kasa nashigo ciki bayan kasan akwai irin wannanazababben wari aciki, wai! To nidai zani wajej bid'o maka abunda kaci tunda yanzu ba kada mamora, kakoma mani cima kwance."
"Ikon ALLAH, yanzu da bakinki kike fad'ar haka bayan kinsan irin wahalar da nakeyi daku lokacin da ina lafiya?"
"Yo yanzu kuma aimuke wahala dakai tunda bakada lafiya, ka jika da wani zance, Ina ai gaskiya nafad'a ba qarya ba zaka wani yab'omun gori, yanzu shekararka nawa ahaka zaune? Ai inaga ko ban biyaka ba duka nakusa biyanka wahalar da kayi damu, kajimun zancen banza da wofi, nikam tin wuri wlh ka sawwaqemun indai qafarnan takace ke wari don bazan iya cigaba da rayuwa dakai ba."
Tana gama fad'ar haka tabar wajen batare da tsaya sauraren abunda zai cewa ba duk da tana jiyo sautin kiran sunanta da yakeyi amma ta tafiyarta.
Haka rayuwa taci gaba da gudana tsakaninsu, muneera dai su baffa sun hanata zuwa bara don da sukaga ma tana nema ta tilasta mata baffa Usman yasa takwashe kayanta takoma gidan baffa inda baba nusaiba, kuma tana samun kulawa daidai gwargwado don har makarantarsu nusaiba ta islamiya da daddare take binta, kuma ba laifi tana fahimta, duk da tagirmema baba nusaiba tana bata girmanta daidai gwargwado a matsayinta na matar wan mahaifinta kuma itama tana jin dad'in zama da ita sosai, gaba d'aya muneera ta canza daga muneerar shekarun baya da batasan ciwon kanta ba izuwa kamilar muneera data san ciwon kanta yanzu, duk wani taimakon aikin gida takan riqawa baba nusaiba batare da tajira ance tayiba kuma tana kula da qannenta su Rashida cikin so da qaunar juna.
Hakan yasa su baffa sukayi tunanin samamata mijin aure duk da kuwa shekarunta sunja sosai, inda akwai wani abokin baffa Usman dake gadi acan cikin birnin kano agidan wani alhaji, amma d'an asalin nan qauyensu ne yanada mata biyu da yara goma sha hud'u donnhar ya aurar da wasu ya tab'a ganin muneera tun lokacin da dad'ewa yayiwa baffa Usman maganar yana so yabashi aurenta, Amma saboda matsalar iyayenta da rawar kanta alokacin baffa Usman yabashi haquri saboda kada su samu matsala a abokan takarsu ta sanadiyar aurenta, don haka sai ya iskesa ya sake tuntub'arsa akan maganar idan har yanzu yanada ra'ayinta kuma cikin iyawar ALLAH yanuna masa shi bai damu da tsufanta ba har yanzu yana sonta indai za'a aura masa ita, nan take su baffa sukace suma sun amince yaje yaganta suyi magana, yana zuwa kuwa muneera ta amince masa ba b'ata lokaci don dama abunda ta dad'e tana jirane ALLAH bai kawo mata ba sai yanzu, iya darasin duniya dai izuwa yanzu ta d'aukesa don haka babu abunda take buqata yanzu inba samun abokin zaman da zata ida sauran rayuwarta da shiba.
Duk da yanayin da baffa Ali yake ciki hakan bai hanasu bashi haqqinsa ba na zamansa mahaifi agareta duk da kuwa babu abunda zai iya attakawa alokacin saboda yanzu ciwon qafar har yakai yafara shafuwar lafiyan jikinsa, ya rame sosai tamkar ba shiba, babu yanda ya iya illa yabi abinda sunka zomasa dashi don ko yace yaqi amincewa tofa bayada qarfin da zai iya dakatar dasu, Inna ruqayya kuwa tayi maseefa tayi jidalinta har tagaji lokacin da zancen yazo mata wanda zuba idon da baffa Ali yayi ya matuqar tab'a mata zuciya har ta d'auki fushi dashi tadena kulasa dama can Kuma ba wata kulawar take basa ba tunda tafahimci halin da yake ciki, acewarta bazata iya zaman shaqar wannan warin qafar tasa da yake fama da ita ba.
Yusuf kuwa kullum cikin aikin gini da labaranci yake yana tara kud'ad'e don yasamu yakai mahaifinsa asibiti hakan yasa baya samu ya wuni gida sai da marece zuwa dare, baffa Ali yayita zaginsa yana fad'in wai shima gudunsa yakeyi shiyasa baya zama gida da rana, tsiga kuwa sai wacce yamanta, haka Yusuf zai zauna yayita kuka yana basa haquri amma tamkar yana sake turasa.
Bayan sati biyu aka tsaida zancen auren muneera tare dasu baffa da Yusuf da iyayen baba aminu mai gadi da sukazo nema masa auren nan da wata mai hita in ALLAH yakaimu, inda su baffa suka koma fad'i tashin kayan aurenta batare da sun jira komai daga kowa ba inba Yusuf da ako yaushe yake bibiyar yanda abun zai kasance ba matsayinsa na d'a babba daya rage masu abokin shawara agidan,
Tsananin tausayinsa da baffa keji yasa ya tambayesa in yana son 'yarsa muneera ya aura masa ita ko yasamu natsuwa akan yanayin da yake ciki, Yusuf na matuqar son Rashida amma daya tuna matsalar mahaifiyarsa da mahaifinsa sai ya nunawa baffa cewa bayada halin yin aure yanzu asali ma baida inda zai aje matar, baffa yayi murmushi had'e da cewa.
"Indai wannan itace matsalarka babu damuwa in Sha ALLAH, ALLAH bazai hana yanda za'ayi ba kashirya in Sha ALLAH zan aurama Rashida indai kana sonta, shekarunka naja yakamata ace kaima kamallaki iyalinka izuwa yanzu."
Shiru Yusuf yayi yana jinjina halayyar baffa wacce ahalin yanzu tayi qaramci, a koda yaushe yana qoqarin rama cuta da alkhairi kamar yanda annabi keyi, bayan duk cutawar da iyayensa suka yimasa amma gashi zai d'auki 'yarsa yabashi wannan wace irin kyakkyawar zuciya yake da ita da batada riqo balle qoqarin rama cuta da cutar da aka yimata, kuka yafashe dashi tare da zayyane masa gaskiyar dalilinsa naqin auren baffa yace bakomai, in Sha ALLAH baya hango komai sai alkhairi acikinsa don haka ya kwantar da hankalinsa, baffa Usman kuwa kafe kai yayi akan bai yarda ba Kuma bai amince da had'inba saboda Inna ruqayya, yasan Yusuf baida wata matsala don kusan halayyarsa irin ta ya nura ce Amma abun dubawa shine halin da zasu jefa yarinyar aciki, Kar azo a maimaita abunda yafaru ashekarun baya ga yarinyar mutane abubuwa duk sukabi suka lalace, Inna Bilkisu ce tayita lurar dashi har ya amince amma yace ba yanzuba kamar yanda baffa ke buqata sai idan takammala karatunta na sakandiri, yanzu tana aji hud'u don se daga baya baffa yayi tunanin sasu makarantar saboda yanda bokon gaba d'aya yafice masa arai, badon baffa yaso hakan ba ya yarda tunda har ya samu ya amince.
Bayan wata d'aya su baffa aka fara shore shiren auren muneera don dama a satin farko na sabon wata yakama, duk abunda yakamata uba yayiwa 'yarsa sunyiwa muneera Kama daga kan kayan d'aki har zuwa na aikin gida da sauransu, muneera kam tayi kuka ba iyaka da nadamar biyewa iyayenta da tayi tun tana cikin qurciyarta ta kasa riqe 'yan uwan mahaifinta da kyau si gashi yanzu sunyi mata gatar da bazata tab'a mantawa ba, baba nusaiba da Inna Bilkisu ma sun tsaya mata sosai wajen gyara kanta duk da tana nocewa, Amma suka nuna mata aishi aure ba ruwansa da tsufan mace matuqar tanada rai da lafiya dole tagyara kanta don samun natsuwar mijinta, Inna ruqayya kuwa ko ajikinta don har ranar da aka d'aura auren muneera Saida ta tashi fita baran Saida Yusuf yayi da gaske sannan tahaqura shima Saida yabata dubu uku tukuna, gaba d'aya haukan tsufa yaqara tarar mata akai da rashin arziqi takoma wata birkitacciyar tsohuwa sai dai ace ALLAH yakyauta.
Alhamdulillah anyi auren muneera lafiya an watse lafiya batare da wata hayaniya ba ko tashin hankali, acan cikin kano inda baba aminu ke gadi cikin wata anguwa ya kama mata hayar d'aki d'aya a wani gidan haya mai d'akuna barjik aka kaita har zuwa lokacin da zai kammala mata nata d'akin acan bebeji inda matansa suke..
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*ππ
[11/14, 22:52] Billy S Fari: πΆββοΈπΆπ»ββοΈ *SANNU SANNU*πΆπ»ββοΈπΆββοΈ
π _Bata hana zuwa..._π
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARIπ*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*π
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*π
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*π
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*β€οΈ
Page___93π
Cike da mamaki muneera tabi mahaifiyar tata da kallo tana fad'in, "innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun, Inna wai kece?"
"Eh nice nan! lafiya kike rafkamun uban salati haka sai kace wacce ta canza maki?, waima bari na tambayeki, dana ganki anan ke kad'ai ina shi mijin naki da tunda yazo sau d'aya gaishemu shima d'in da daddare har yanzu bai sake komawa ba saboda mugun hali don kar yace mana ungo."
Kallon kallo suka shigayi shi da ita kafin tace.
"Maigida innace fa!"
Da sauri ya duqa qasa yana gaida Inna ruqayya data saki baki tana kallonsa kafin tace.
"Yanzu muneera wai wannan shine mijin naki?"
"Eh Inna." Muneera data rasa yanda zatayi da ita tafad'a tana kallonsa, jitayi mahaifiyar tata nafad'in.
"Tirqashi! Kaico muneera, kice baki rabu da wahala ba, tsiyace ta taradda tsiya don wannan tsohon dagani babu tsiyar da yake tsinana maki, ana mutum haka hannuwa duk aqwaq qwange ba ko wannan ungo ta alkhairi! tun d'azu nake miqa masa hannu kusan mintuna biyar amma bawan ALLAH nan yayi biris dani ya d'auke mani kai don d'ibar albarka, Ina in bazai bani ba sai yafad'amun intafi abina sai yabarni tsaye ina miqo hannu, kaganka wallahi da gani bakada kir.." Bata qarasa ba muneera tayi saurin cewa.
"Haba inna meye haka kuma!, Ai baisan ke bace kuma baya canji Shiyasa bai baki ba."
"Ke rufamun baki, samna wannan ai qwanda kiyita baranki daki zauna dashi, mutum bazaice ungo ba ta alkhairi sai dai yayita karkace karkacen kai yana duqe duqen banza."
Ta qarasa maganar tana zura wuya tana kallonsa daga duqen da yake har ya gaji dajin maganganunta yamiqe yana mummurza hannayensa had'e da cewa.
"ALLAH yabaki haquri Inna."
"Innooo!, nace ba Inna ba innooo..don tsabar mugunta tsofai tsofai dakai ka kalleni kace mani Inna, haka aka Inna ba ungo ta alkhairi.."
Jin kalmar ungo da taketa maybe maitawa yasa mijin na muneer tura hannu a aljihu ya ciro naira d'ari biyar had'e da d'an rissinawa yamiqawa Inna ruqayya, tsabar sauri takarb'a har yakusowa tayi da hannunsa tana fad'in.
"Ikon ALLAH, to ko kaifa! da arziqinka kanemi maida kanka marowaci, to ALLAH qara bud'i kaji, agaisheka maza munneer kishiga ciki dashi kin barshi a tsaye don sakarci da rashin iya kula da miji, kushiga cika mana baffan naku nacan dad'a a guntule qafa abun gwanin tausayi."
Taqarasa maganar had'e da fashewa da kuka tasa mayafi tana sharar qwallan da suka zubo mata.
Muneera da tsabar baqin ciki da takaici sun rufe mata idanuwa tayi fuuu...tawuce abunta batare data qara bi takanta ba, bayanta mijin nata yabi yana kiran sunanta har ya cimmata ya tsaida ita, ganin da yayi idanuwanta sun cika tab da qwallah ya sashi cewa.
"Subhanallahi, muneera meye abun kuka!."
Cikin b'acin rai tabud'e baki zatayi magana yayi saurin dakatar da ita don yasan dole taji ba dad'i aranta, Amma ya zatayi? Mahaifiyar tace dole tayi haquri da ita, d'an murmushi yayi kafin yaci gaba da cewa.
"Baikamata ace kin nuna b'acin rankiba har kiyi fushi kitafiyarki kibarta awajen, ita uwa uwace baza'a tab'a canza taba komai lalacewarta, don haka kijeki idan kinada abun kyautata mata ki kyautata mata tare da magana mai dad'i cikin girmamawa, hakan zaisa nasamu natsuwar cewa koda nan gaba nayi tsufan da zan buqaci taimakonki to bazaki tab'a wofantar dani ba."
Dama damuwar muneera shine kar mijin nata yaji ba dad'i ko yayi qoqarin walakantata akan wannan abun da mahaifiyarta tayi, amma da taji yafad'i hakan sai tasamu wata irin natsuwa da sauri tabi bayan Inna ruqayya dake tafe can gefen titi tana faman qirga 'yan kud'ad'enta da bata gajiya da qirgarsu,
"Inna.." munnera tafad'a lokacin data cimmata tare da riqo hannunta suka koma cikin inuwar wata bishshiya.
"Lafiya muneera, ko saqo mijin naki ya sake turowa ki kawo mani?"
Murmushin da yafi kuka ciwo muneera tasaki had'e da cewa.
"Inna kenan!.." sannan tasa hannu cikin 'yar qaramar jikkarta ta hannu ta d'auko kud'ad'e aciki ta harhad'a, d'ari uku ne da saba'in aciki tamiqa mata had'e da cewa.
"Ga wannan Inna ni nabaki, kiyi haquri banida kud'i wannan ma sana'ar saida 'yan kayan yaji nakeyi d'an cinakin dana samune nahad'o da niyar inba baffanmu ko lemu asiya masa, Amma tunda kina so gashi saiki qara, in Sha ALLAH zan dinga kawo maki masu yawa idan ALLAH ya bud'a mani."
Rawa Inna ruqayya tafara kwasa awajen cike da farinciki kafin ta amshi kud'in tana fad'in.
"Kai a dai gaisheki muneera, ALLAH yayi maki albarka, haka nake son gani kullum don haka kiriqe mijinki hannu biyu yanda zaya yita baki kina bani kinji ko.?"
"To inna, Amma naroqeki don ALLAH kidena wannan baran bayada amfani ko kad'an, yanzu kinga abunda yafaru tsakaninki dashi ai baiyi dad'i ba badon ma yanada tunani ba sai hakan yasa wata rana ya koro makini, amma kiyi haquri Idan hakan dana fad'a ya b'ata maki rai." Taqarasa maganar tana hawaye tare da riqo hannunta.
Fisge hannunta tayi daga riqon da tayi mata had'e da d'aure fuska tace.
"To naji, maza kijeki yana jiranki."
"Kiyi haquri inna..."
"Nikam muneera yaushe kika lalace haka?, nace kijeki naji ba shikenan ba?."
Jiki a sanyaya muneera tabar wajen tanayi tana juyowa tana kallonta tana tafiya harta b'acema ganinta sannan ta ida shigewa ciki tana mai addu'ar ALLAH yaganar da mahaifiyar tata.
Bayan sati uku baffa Ali yaji sauqi sosai saboda yana samun kulawa wajen likitocin da kuma 'yan uwan nasa yanda ya kamata, babu wani rad'ad'i da yakeji kamar da sai abunda baka rasa ba, yanzu babbar damuwarsa d'aya shine yanda zai kalli 'yan uwansa inya tuna da walaqanci da kuma abubuwan daya tayi masu abaya amma duk basu dubi wannan ba sukayi tsaya wajen ganin yasamu lafiya, duk yatuna da wannan yana sashi dana sani da zubar da hawaye sosai, musamman idan yatuna yanda son zuciya da baqin hali yasashi biyewa matarsa ya raba yayan nasa da d'ansa na tsawon shekaru sai yaji gaba d'aya ya tsani kansa.
Yauma zaune suke duk su duka tare dasu baba balarabe sunzo dubasa da mijin Yaya Maryam anata fira ana dariya, shikam banda murmushi babu abunda yake iyayi don rad'ad'in cutar dasu da yayi dake zuciyarsa bazai bashi damar yin walwalar da zai iya dariya ba, wasu zafafan hawaye yaji sun zubo masa a fuska lokacin daya dubi yayan nasa yaga yanda tsufa ya dabai bayesa gaba d'aya don baida baqin gashi ko kad'an a jikinsa inba jefi-jefi gashin gaba d'aya yakoma furfura gwanin ban tausayi, kukane ya kufce masa ya shiga sheshsheka yana share majina, nan take gaba d'aya hankulansu suka dawo kansa, da sauri baffa Usman ya riqesa ganin yanda jikinsa ke rawa daga kan gadon yana qoqarin fad'owa saboda tsananin kukan dake nema yafi qarfinsa.
"Haba Ali!, shin har yanzu bazaka haqura kadena wannan kukan haka ba?, Duk fa mai rai dole ajarabcesa don agwada imaninsa, kai kamata ma yayi ka godewa ALLAH da yasa qafa d'aya aka cire maka, adaidai wannan lokacin akwai wanda gaband'aya dukkanin qafafuwan nasa yarasa, sai yace me?, Ana rayuwa haka ace Babu tawakkali?, Fad'amun naji shin wannan kukan naka zai iya dawo maka da qafarka ne da bazaka haqura kafawwalawa ALLAH ba domin shi kad'ai yasan dalilin dayasa hakan faruwa, kuma duk yanda ALLAH yayiwa bawa to yatabbata hakan shine mafi qololuwar alkhairi agaresa."
Baffane kefad'ar haka tare da riqo hannun baffa Ali cikin sigar lallashi, dik wanda ke wajen ya matuqar tausaya masa saboda baqaramin tashin hankali bane rasa wani sashe daga cikin sassan jikin mutum, su a tsammaninsu adalilin haka yake kuka, gaba d'aya suka taru suna bashi baki da ban magana akan ya yarda da qaddarowar da ALLAH yayi akansa, Saida yayi kukansa mai isarsa sannan yayi shiru cikin jin nauyi ya d'ago kai yana kallon baba balarabe yace.
"Malan balarabe kayafeni bisa maganganun dana fad'a maka cewa, yayana da d'an uwana Usman sun zauna acikin gari suna zaginku akan cewa sunyi nadamar had'a zuria'a daku saboda sanadiyar auren 'yarku yarusa mana farincikin gida da kuma ahali, ba gaskiya nafad'a ba da nace maka sunce Nuraddeen ya tafiyarsa wajen karatunsa batare daya sanar daku ba saboda zaku iya sa akamashi arufe da sunan shiya halakar maku da 'ya, ba gaskiya nafad'a maka ba da nace maka yayana yace bada son ransa ya bari 'yarku ta auri d'ansa ba don dama bai yarda da tarbiyarta ba don ance ita dakanta ke bud'e baki tana iqirarin cewa aure take so kuma qiyi mata wai lallai sai tayi karatu, shine data fara bin maza kuka rufesu da d'ansu yace yana sonta kuka aura mashi ita, shine data gano cikin dake jikinta ba nasa bane tagudu tabar gari, gashi yanzu tasaka shi cikin