Showing 18001 words to 21000 words out of 129098 words
Chapter 7 - AMNA DA SAFNA Book Complete Hausa Novels by Aisha G Umar.docx
burin ɗan garuwa yayi, irin ƙaton wayar nan mai bottle, ya miƙa mata, da sauri ta amsa tana tambayar sa wani suna yasa?" Dialing tayi bayan sanar da ita sunan da yayi saving numbern da shi, a kira na Uku ne ya ɗauka yana faɗin, "sorry I'm meeting now".
ganin cewa bai ma san numbern da aka kira sa da shi ba, yasa Safna cewa "Dady it's me Safna Ammu na ce ba lafiya Dady dan Allah ka taimake ni" ta ƙarashe faɗin tare da fitar da hawaye a idon ta, cikin tashin hankali yace "what happen with her?" Babu ɓata lokaci ta sanar dashi, "ok I'm coming right now".
Kashe wayar tayi da tinanin, da ma ta san indai Dady yaji to zai yi gaggawan zuwa, miƙa masa wayar tayi haɗi da yi masa godiya "Safna kan ki na zubar da jini sosai" kan ya ƙara yunƙurin wata maganar tace, "zanje in wanke yanzu" ta faɗi tana sharar ƙolla, ita fa da so samu ne, in mutum zaiyi mata magana yayi mata kalma ɗaya ko biyu ya wadatar.
Zuwa ɗaki tayi ta shiga toilet ta wanke jinin da ke zuba, ta ɗaura ƙyalle à wurin, bata tsaya canza kaya ba, ta nufi inda Ammu take "Hasbunallahu wa ni'imal wa kiil" ta faɗi lokacin da zafin jikin Ammu ya ratsa hannun ta bayan ta ɗaura à kan ta.
Saurin tashi tayi ta ɗibo ruwa a kwano ta ɗauko ya di mai laushi ta fara tsomawa tana matsewa sai ta ɗora kan Ammu tana mammatsa mata, da addu'an Allah yasa dabarar yayi kafin zuwan Dady.
Ta ɗau 30 minute ba ta tsaya ba, amma zafin jikin ya ragu, sai à lokacin Dady ya zo cikin manyar kaya, irin na hamshaƙan masu kuɗi, ɗaukar Ammu sukayi zuwa Hospital, Safna ma akayi mata bandejin goshin ta, Dady ya tambaye ta me yasame ta haka, sai ta bashi amsa da bugewa tayi, dan sanar da shi gaskiyar babu abinda zai amfane ta da shi.
Doctor ne yake sanar musu da, "ba wani babban abu bane yasa ta kasancewa a yadda take yanzu face rashin motsa jiki sosai da ba'a sa ta, kuma ya kamata a rinƙa kula da ita wurin fitar da ita waje ta rinƙa shan iska, saboda kasancewar ta kullum à ɗaki guri ɗaya zai kawowa da jinin ta rashin jin daɗi gurin kewayawa a jikin ta, kuma hakan zai haifar mata da wani abun daban, ku sai mata keken guragu zai tai maka muku wurin tura ta ba tare da ta sha wuya ba" Bayan sun gama jin abun da likita yace Dady yayi masa godiya, da kuma sanar da shi za'a kiyaye.
Bayan fitowar su suka nufi ɗakin da Ammu take, "shirya ta mu koma Gida Safna" Cewar Dady, to ta amsa masa dashi sannan tace "thank you so much Dady" "No my daughter akan me zaki yimin godiya? dama kula da ku a wuya na yake, so don't thank me" ƙasa kawai tayi da kan ta, da roƙon Allah ya bata abun da zata sa kawa Dady da shi, saboda shine mai kula da matsalar su à ko da yaushe.
AMNA.
Koda isan su gida Ummee suka shiga tashin hankali dan ganin Raunuka a jikin Ɗan su, duk da anyi masa tritment, tambaya suka shiga yi musu, sai dai har yanzu Amna batayi magana ba, sai ma wucewa ɗaki da tayi.
A hasale cikin ɗagun murya Ummee ta fara magana, "har yaushe zaki bar abubuwan nan da ki ke yi Amna? Tun da ki kayi shiru nasan bai wuci ke kika haddasawa Mubarak wannan raunin da yake jikin sa ba, ke wace irin Mutum ce wai, baki da aiki sai neman rigima?" Rintse idanun ta tayi yayin da taji magan-ganun Ummee a gare ta.
"a ah Ummee ba yadda ki ke...." katse sa Ummee tayi "rufamin baki dama duk san da zata kwaso rigima ai a bayan ta kake, kai ga ka mai 'yar-uwa" "Biba kada kice haka saboda baki san dalilin da yasa faruwar hakan ba, domin nasan Amna baza tayi abu ba tare da dalili ba" Cewar Mamma dake zaune gefe tana ƙara kallon Mubarak cikin tausayawa.
Ummee ce ta ƙara cewa, "haba Mamma dubi abin da ta jawa Ɗan-uwan ta, ita kam koda yaushe bata san haƙuri ba ne, ita kinga jikin ta da ko ƙorzane ne? Duk abun da ake faɗawa Amna a kan haƙuri ba ta ɗaukar sa, sai kace ita tafi kowa zafin zuciya" Ta ƙarashe maganar cike da masifa.
"Mubarak meya faru a makarantar?" Mamma ta tambaye sa, sanar da ita komai yayi, babu ƙari ba ragi, sallallami suka hauyi cikin tashin Hankali, "yanzu abun da ya faru kenan, Lahaula wa la ƙuwwata illa billah, Amna wani irin abu ki kayi haka? ba ku zuwa ku sanarwa da mahukuntan makarantar su ɗau mataki da kansu?" Cewar Mamma cikin tashin hankali da tinanin a binda zai biyo baya.
Ummee kam kasa magana ma tayi saboda tsaban tashin hankali, sai da ta sauke babban ajiyar zuciya sannan ta fara kiran Amna, fitowa tayi har lokacin bata cire kayan ta ba, kuma fiskar ta ko alamar fara'a babu, sai lokacin suka ga jinin da ke kayan ta, "wannan kenan duk jinin mutanen ne, na shiga Uku Amna zaki kashe ni da raina, wannan wani irin masifa ne? Yanzu waya san abun da zai faru, bayan abinda kika jawo mana"
Sai lokacin ta buɗe baki tace "Ummee ku duba raunukan da suka yi masa fa" ta faɗi tana nuna inda yake, kan ta ƙasa "munji sun yi masa rauni, to kuma babu wata hanya da za kiyi sai na ramawa?" Cewar Ummee, Mamma ma tace, "Amna nakan goyi bayan ki a ko da yaushe, duk da abin da yaran sukayi ba daidai bane, amma hanyar da ki ka bi bai dace ba, yanzu Allah kaɗai yasan abun da zai faru gaba, dan nasan iyayen su baza su bar maganar ba".
Miƙewa kawai Amna tayi ta wuce dan yin wanka tayi Sallah, bin ta da kallo su kayi Mamma tace, "babu ruwan ta fa" "ai kin san ta Mamma duk abinnan da tayi ganin dai-dai take masa" faɗin Ummee tana girgiza kai cike da takai ci, shima Mubarak miƙewa yayi da ƙyar, "sannu Mubaraka bari in tafasa ruwa in mammatse maka jiki, baka zauna haka ba", Mamma ta faɗi hakan tare da miƙewa.
DARE.
Su Ummee sun kasa sanar da Baba abun da ya faru, dan ko yanzu daya kira su hira kawai sukayi, ba tare da kawo maganar ba.
BABA.
Bayan ya gama magana da iyalan sa, ya ijje waya kenan kiran Zilla ya shigo wayar sa, dagawa yayi da mamaki, "ka yi mamaki ne? To ba abun mamaki bane beautiful, kawai naji ina son jin muryar ka ne, na ƙosa gobe yayi in haɗu da kai, saboda ina da abubuwa masu ban sha'awa da zan ba ka, amma kamar wani lokaci zamu haɗu?" Ta faɗa masa yana ɗaukar wayar.
"Da ma wai haka take da surutu ne ko me? Danni banga jan ajin n'a ta ba" Cewar Baba a zuciya, sannan ya amsa mata da, "kamar da yammaci" "kashsh gaskiya banji daɗi ba, yammaci yayi nisa, amma ba komai sai lokacin i love you beautiful" kashe wayar yayi ba tare da ƙarasa jin abunda take faɗa ba, wani takaici ya rufe sa, dan shi ƙyamar ta ma yake, "Allah ka bani sa'a akan wannan aikin da na ɗauko" kawai ya faɗi a fili.
WASHE GARI, ASABAR RANAR HUTU.
SAFNA.
Duk da abin da ya faru jiya bai sa ta hutawa ba, sanin cewa yau ranar Aikin ta ne, cike da juriya ta fara aikin har ta gama, ɗauko keken da Dady ya kawo wa Ammu tayi ta ɗora ta a kai, dan fitar da ita tsakar gida dan shan iska.
Tasa Ammu à gaba tayi tana kallon ta, bayan ta fito da ita waje, ta zauna akan kujera ita ma, "sannu Ammu, na san dai yanzu kin ɗan ji sauki ko?" Lumshe ido Ammu tayi sannan ta buɗe alamar eh taji sauki, "yauwa Ammu na haka nake so, insha Allahu nan bada daɗewa ba, zaki samu lafiya daga dukkanin Matsalar ki".
murmushi Ammu tayi mata dayin mata alama da "Allah yasa hakan, nima abinda na keso kenan" ta ɗago hannun ta da ƙyar alamar "matso kusa dani" murmushi ita ma Safna tayi, ta sauka kan kujerar da take, ta tsugunna haɗi da ɗaura kan ta a saman ƙafafuwan Ammu, tana mai jin farin ciki a ranta, rabon da Ammu ta fito ko ƙofar ɗaki ta manta bere waje.
#To fah, shin iyayen su Jalo zasu bar maganar kuwa?.
Ya Baba zaiyi idan yaji abunda autar sa tayi? Zai goyi bayan ta ko kuwa?.
Baba zai ci nasara ko daiii?. Nifa har na fara tinanin wani abu😁
Fitar da Ammu waje shan iska zai ɗore kuwa?.
______________________________________________________________________________________________
Part 2️⃣1️⃣▶️2️⃣2️⃣
Shafa kan ta Ammu take yi a hankali, yayin da zuciyar ta ke tinanin wani abu daban, katse mata tinani Safna tayi sanadiyyar ɗagowa da kan ta da tayi, tana faɗin, "Ammu na ina zuwa kinji, ba daɗewa zan yi ba" da ido lawai Ammu ta bita.
Ba ta ɗau lokaci ba ta dawo da ƙaton paranti à hannun ta, ɗauke da kula da kuma plate mai zurfi da cokali a ciki, ijje sa tayi haɗi da buɗe kulan, ashe ferfesun hanta ne a ciki yaji romo sai tashin daddaɗan ƙamshi yake wayyooo😋.
Diba tayi tasa a mazubin sannan ta rufe, ta mayar gefe, zama mai kyau tayi a inda ta zauna ɗazu tana facing ɗin Ammu, "musamman dan ke nayi wannan ferfesun Ammu nasan zaki so shi sosai, yana ɗaya daga cikin abincin da Doctor ya umurta da ki dinga ci" murmushin jin daɗi Ammu tayi da yadda 'yar ta ke kulawa da ita yadda ya kamata, da itane kawai take iya magana mai tsawo.
ɗibawa tayi à spoon ta fara ba ta tana ci, sosai ya yiwa Ammu daɗi, Safna kuwa tana ba Ummee tana yi mata hira.
Fitowa daga falon yayi yana waya, sai dai ganin su da yayi yasa shi tsayawa yana kallon su, musamman Safna da take bawa Ammu abinci tana ta bata labari, sakin baki yayi yana kallon yadda take magana tana ta murmushi wani gurin kam har dariya take, "Ashe dama tana magana haka? har dariya take yi" ya faɗi a zuciyar sa.
"Yazeed kana jina kuwa?, Yazeed" daga can ɓangaren ake cewa jin yayi shiru, "Aliyu zan kira ka" kawai ya furta tare da sauke wayar a kunnen sa, ci gaba da kallon ta yayi, ya fara takawa a hankali kamar wanda ake kira, har ya isa kusa dasu idon sa na kanta, yana jin yadda muryar ta ke ratsa kunnuwan sa.
Tana gama bata, ta ijje kwanon gefe, Ammu kuwa sai murmushi take yi, ganin yadda Mahaifiyar ta ke murmushi, yasa ta cikin farin cikin da ta daɗe bata tsinci kan ta ciki ba, ɗauke da murmushi a fiskar ta tace, "kin ji daɗin labarin da na baki Ammu?" Tayi mata tambayar kamar tana jiran Ammu ta bata amsa, "eh yayi daɗi sosai" taji maganar sa gefen su, ba tare da ko jin motsin zuwan sa ba.
Da sauri ta juya duk da tasan muryar waye amma tayi mamakin furucin na sa, fiskar sa ta gani da murmushi abin da itama za tace bata taɓa ganin hakan daga fiskar sa ba, sai dai ɗaure fiskar da yake yi a duk sanda suka haɗu.
Ganin kallon mamakin da take masa yasa shi fahimtar ya saki layi fa, ɗauke idon sa daga kan ta yayi ya fiske, ya taho gurin Ammu ya durƙusa haɗi da dafa Keken yana cewa, "Aunty Maryam kina lafiya? Na daɗe ban gan ki ba" amsa masa Ammu tayi ta ido, wanda ba fahimtar hakan zaiyi ba, ɗauke ido Safna tayi daga kansa saboda takaicin maganar ta sa, ta ɗauki parantin dan kaiwa kitchen.
Shi kuwa Yazeed juyawa yayi ya bita da kallo, "kada fa ta raina ni dan ta ga na kalle ta?" Ya tambayi kan sa, sai kuma ya miƙe ya koma inda Safna ta tashi ya zauna, yana ƙure Ammu da ido, yana tuna lokacin da take da lafiya, tana da kirki sosai, shima yafi zama a wurin ta wancan lokacin.
"Aunty Maryam kin tuna lokacin da ki ka mana wani irin abunci, mema sunan shi?" Ya faɗi yana tuna sunan abincin, "yauwa Dambu" ya faɗi yana murmushi, yana ci gaba da cewa, "kin iya abinci sosai, haryanzu ban taɓa cin abinci mai daɗin na ki ba, ina fatan ki samu lafiya wata rana ki dafa mana abinci fiye da na da" kulle ido Ammu tayi da a lama itama ta tina wani abun.
Buɗe ido tayi tare da ɗago hannun ta a hankali ta ɗora kan fiskar sa, tana mai sanya masa albarka a zuciyar ta, ranar Asabar da lahadi ne kawai baya zuwa gaishe ta, amma duk ranar da Safna take zuwa makaranta sai ya shigo ya gaishe ta, indai har Safna tana nan kam baya zuwa, tana jin daɗin zuwan da yake yi gaishe ta.
Tsayawa tayi tana kallon su, da mamakin Tsayawar sa har yanzu a wurin Ammu, sannan ga Ammu ta ɗaura masa hannu a fiska, me hakan yake nufi? dan ita ta ma ji tsoro dan ta ɗauka faɗa zai yi saboda fitar da Ammu da tayi, amma sai taga saɓanin haka.
Bata ƙarasa wurin ba sai da taga barin sa wurin sannan, "Ammu lafiyan yaya Yazeed kuwa?" Ta faɗi tana zama a kujerar, sai dai murmushi kawai Ammu tayi mata ba tare da bata amsa ba.
AMNA.
Sallama suka fara ji ana ƙwalawa a ƙofar Gida tare da Ƙonƙosa wa, daga jin sallamar kasan ba lafiya ba, "waye yake mana irin wannan sallamar ko ƙaƙƙautawa babu haka?" Cewar Mamma da ta fito daga ɗaki, daidai fitowar Ummee ita ma daga ɗaki, a tsorace Ummee tace "Mamma jiya kwana nayi ina tinanin abun da Amna suka yi jiya, anya ba Folisawa bane kuwa?".
Zaro ido Mamma tayi a tsorace ita ma tace "zai iya yuwwa, amma dai yanzu muje muga su waye" "Mamma wai maganar me kuke yi ne?" Cewar Amna da ta tashi daga barci jin maganar da suke, hararar ta Ummee tayi tace "Tun da kin tashi sai kije kiga su waye ai" bata yi magana ba ta ɗau ƙaramin mayafi ta yafa ta nufi gate.
Tana buɗewa taga mutane, malaman makarantar su maza biyu da mata biyu, sai wasu da bata san su ba, maza uku mata biyu sai kuma police biyu maza, ƙure ta da ido su kayi ganin me kama da Baturiya ta fito, wannan kam ai bama kama ba Baturiyar ce.
Su kansu Malaman na su basu gane ta ba, saboda kasancewar ta mai hazaƙa da kuma rigima da wanda ya taɓo ta yasa kowani Malami ya san ta, amma rashin ganin ta da glass yasa su rashin gane ta.
Risina wa kaɗan tayi alamar girmamawa ganin Malaman ta tana gaishe su, amsawa su kayi police Kofur Habu yace, "Baturiya nan ne gidan su Amna Hussaini Baba da kuma Mubarak Hussaini Baba?" Cike da mamaki take kallon su, kamar bata san meya faru jiya ba, tace "eh nanne" "ok yi mana sallama da Baban ku" faɗin ɗayan police ɗin Kofur Ali, cike da mamakin hausar da tayi, "Baya...." "ya kika daɗe ne Amna daga ki duba suwaye?" Mamma ta katse ta da son faɗin baya nan.
Malamar su Amina tace, "wai dama Amna ce nan?" Ta faɗi cike da mamakin dama haka idon ta yake, wato shiya sa taji wasu ɗalibai na gulma jiya, sauran ma da mamaki suka bita, iyayen yaran sai magana a zuciyar su suke, wai wannan abar da ko jikin kirki babu, amma ita ce ta logwada musu 'ya'ya haka? kan tayi magana Mamma ta fito, zaro ido tayi tana sallallami, tace "Lafiya kuwa 'Ƴan-sanda abokan wasu?" Ta faɗi cikin rawar murya.
"Abokan kowa dai ko Kaka?" Cewar Kofur Ali, Mamma tace "ina Abokan wasu dai, ai in an ganku to da matsala" dariya kaɗan su kayi sannan su kace "Kaka zamu iya shiga daga ciki?" Jin maganar da sukayi yasa hankalin ta ɗan konciya kaɗan, domin inda da matsala suka zo sai dai ace a wuce station.
"Eh ah mezai hana? Bismillah" shiga sukayi dukkan su, after 5 minutes, Gaba ɗaya mutanen zaune suke kan shimfiɗar da Ummee tayi musu, gefe ma Ummee, Mamma, Mubarak da Amna ne, sai police ɗin da suke tsaye, gaishe da Mubarak da jiki sukayi, sannan suka tambayi Mahaifin su Amna? Mamma ta basu amsa, "Mahaifin su baya nan yayi tafiya".
Cikin Malaman na miji ne ya fara magana, "kamar yadda yaran ku suka sani mu Malaman su ne, mun zone sabida abin da ya faru jiya a School, ba a gaban mu ya faru ba, amma mun samu bayani daga sauran ɗaliban, wa'ennan su ne iyayen yaran" ya faɗi haɗi da nuna musu sauran mutanen.
Mahaifin Zanga ne yace, "Muna masu baku haƙuri akan abin da ya faru, tabbas yaran mu basu kyauta ba da suka tarunma yaro ɗaya sukai masa rauni" kallon-kallo Ummee da Mamma sukayi da mamakin jin maganar,