Showing 30001 words to 33000 words out of 159134 words
Chapter 11 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt
mata duk abinda ta kamata ai mata,
Ganin yana ƙoƙarin zama bakin gadon ne yasa yace"Malam tashi mu tafi zasu kulle ƙofa "
"Ka tafi kawai idan zazzabin ya sauka zan wuce"
"Ba dai ka mata abinda ya kamata ba?
" Sosai ma kuwa"
"To tashi mu tafi bana son cin musu" Ya fada yana ƙara gimtse fuska,dan ya fara lura da take_taken shi.
Ba dan yaso ba ya mike ya nufa kofa harda juyowa ya kara kallon ta,gaskiya wannan Ustazun ya kwabsa mashi,shi da yaso ya zauna yata kalle ta.
"Mu je ki kulle ƙofa" Ya fada yana yin gaba,
Da sauri Nafisa ta bishi ta kulle kofofin shiyan,
Cikin ikon Allah kafin wani lokaci zazzabin ya sauka,ta daina rawan sanyin,
Washegari da safe ta ji sauƙi tunda har ta ita tashi tayi sallah,sannan taje ta gaida Kaka wacce ba karamin jin daɗin ganin ta tayi ba,sannan ta koma daki ta kwanta,
Kamar yanda suka saba daukar karatu a shiyan kaka dun safiya yauma haka ne,sai dai Yaya Nurudeen ya riga kowa shigowa,shida bai cika zuwa ba,
Sai kalle_kalke yake ta ina zai hango ta,ganin sun fara karatu ne yasa ya mike ya doshi dakin Nafisa,
Ji yayi muryar Kaka ya dakatar dashi"ina zaka"
Shafa kai ta fara ya nuna mata dakin Nafisa "zan dubo mai jiki ne"
"Dawo ka zauna dan yanzun ta bar nan,jikin da sauƙi dan har tayi sallah ta kuma zo ta gaida ni,sannan bana son na ƙara ganin irin haka"
Ya gane me take nufi wato bata son ya kara cewa zai shiga dakin.
Ba dan yaso ba ta dawo ya zauna,can kuma ta tashi ya fita,dan ya lura kaka ba raga mashi za tayi ba,har balle ta gano ƙudirin shi akan yarinyar.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*21*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Misalin karfe takwas da rabi na safe ta tashi tayi wanka da ruwan ɗumi,sosai ta ji daɗin jikin ta,Nafisa ce ta je shiyan Ammi ta karbo mata kayanta,riga da zani ne na Atamfa wanda rigar ya saukar mata har guiwa sai zani,
Kasancewar ranar sati ne babu aiki kowa na gida,shi yasa duk ranar ashiyan Kaka suke karin safe,sannan suke cin abinci dare,
Shi yasa ma yau duk suka hadu Ana cin abincin safe,
Hauwa'u ce ta shigo da sallama,gaisawa suka yi har da Kaka,
"Ga wuri ki zauna,Nafisa kawo mata abin kari"
Zama tayi tana murmushi domin ba karamin burge ta suka yiba,"kaka na koshi,na gode,"
"Nafisa kira mata Habiba"
Da to ta amsa tana mikewa,
Jimawa kaɗan sai gasu sun fito tare,tana biye da ita a baya,
Duk da kayan jikinta sun mata yawa zani kuma leɓe daya yafi daya tsayi,ga kuma ɗan kwalin da yafashi kawai tayi akai bata Daura ba,amma ta fito shar da ita,fuskarta ya ƙara haske,yayi fayau da shi,
Nuna mata kusa da ita tayi"zauna a nan "zama tayi tana gaida su,
Wasu sun amsa wasu basu amsa ba,
Tambayar ta matar da ta ji an kira da Hauwa tayi" Kin yi karin safe"
Jinjina mata kai tayi"eh"
Kaka ce tace"Zainab jeki shiyan Ammi ki anso ledan magunguna "
"To kaka"ta faɗa tana fita,
" Wai nikam ina Surajo yake ne ko yau ba zai karya ba ne?
"Na dai ga kofarshi a kulle" Cewar Salman.
Zainab ce ta shigo da leda a hannun ta mika ma Hauwa'u,
Amsa tayi ta ciro magunguna ta shiga nuna mata yanda zata sha,
Allura ta ciro ta shiga haɗawa,"zamu shiga daki sai na maki Allura zuwa yamma kuma zan dawo sai na maki daya"
Numfashi ta sauke sannan ta mike tsaye,kallon kofar fita falon tayi,"ina so in je in gaida Ammi,bari in na dawo sai ki yi min"ta faɗa tana nuna ƙofa,
"Da dai kin tsaya sai na maki dan sauri nake zani wurin aiki"
Tana kokarin yin magana ne kaka tace"ku shiga daki na sai ku yi "
"To Kaka" Cewar Hauwa'u tana mikewa,
Ba dan ta so ba tabi bayan ta,
Mintina biyu tsakani,sai jin tashin ihu suke,sai kuma gashi ta fito da mugun gudu ɗan kwali a hanu tayi waje,yanda kasan wacce kura ya biyo,
Duk da kallo suka bita,
Kafin Hauwa'u ta fito ɗakin riƙe da Allura a hannu,tana kiran sunan ta,
Kaka ce ta dakatar da ita daga ƙoƙarin binta da take "lafiya?me ya faru?
Tsayawa tayi tana dafe ƙwanƙwaso" Wallahi nima ban sani ba kaka,amma ina ga duk yanda akayi tsoron Allura take yi"
Yamutse fuska Aunty Maijiddarh tayi"sai dai in iskanci amma me abin tsoro ga Allura"
"Wallahi kuwa,ke dai bari kin San idan mutum ya samu wuri babu tsiyan da ba zai shuka ba" Cewar Khadija,
Ibrahim ne yace"na ga dai Uwar faɗin ma haka take "
Kaka ce ta dakar dasu"bana son rashin girmama abinci,wannan ba ɗabi'a mai kyau bane kana cin abinci kana surutu,
Sallamar shi da suka ji ne ya jawo hankalin su,
Niman kusa da kaka yayi ya zauna,
Da sauri Aunty Maijiddarh ta taso tazo tana kokarin zuba mai kunun kyada dake cikin fulas,da hannu ya mata alama akan ta dakata,
Jiki a sanyaye ta tashi ta koma wurin zaman ta,
Gaida shi Hauwa'u tayi ya amsa,a takaice,
"Zainab maza ku tashi ku kira min Habiba ta bar yarinya tana zaman jiranta"
Turo baki tayi"kaka to ai ita ba ƙaramar yarinya ba ce,kawai ita Hauwa'u ta yi wucewar ta jiki magayi,idan ta ji jiki da kanta zata nime a mat...
Haɗa ido da suka yi dashi ne yasa ta kasa karasa maganar daje bakinta,cikin sauri ta tashi ta fita,
Da kanshi ya zuba kunun a kofi har sai da ya kusa kammalawa sannan suka shigo wai basu ganta ba bata shiyan Ammi,
Dan haka kaka tace Hauwa'u ta wuce Nurudeen zai karasa mata Alluran,wanda hakan ba karamin daɗi ya mashi ba.
Sallamah ta masu ta wuce,
Yana kammalawa tashi yayi ya fita kaka ce ta dakatar dashi"ina zaka kuma baka ci kosai ba"
"Sauri nake saboda yau zamu tafi wa'azi Nijar"
"Yanzun zaku tafi?
" Sai zuwa anjima amma yanzun akwai in da zanje ne"
"To Allah ya tsare hanya ya dawo da kai lafiya,"
Da Amin ya amsa,sannan ya wuce.
Har ya saka katin kofa sai yaji kamar yana jin motsin mutum,
Dan haka juyawa yayi,sai dai bai ga kowa ba,hango gefen zani yayi,
Dan haka a hankali ya taka ya isa in da take zaune a ta lungun dakin su,ta makale ta haɗa kai da guiwa,
"What are you doing here?
Baki ta buɗe tana ƙoƙarin saka ihu,domin ba karamin tsoro taji ba,
Ihun ya makale ne sanda taga wanda ke tsaye a gabanta,
Dafe kirji tayi tana sauke numfashi,
Cikin jin haushi ta turo baki" Shi ne zaka ba mutum tsoro"
Jin kamar takun tafiya ne yasa ta juya baya,Salman ne ke ƙoƙarin bude nashi kofar,
Kokarin yin magana yake yi,yaji an riƙe mai ƙafa gam,
Juyo da kallon shi kanta yayi,ta tsugunna yanda kasan me niman gafara,gashi ta wani marairaice fuska yanda kasan kyanwa,sai wani rau_rau da ido take yi,"dan Allah karka faɗi in da nake"
Jan kafar shi yayi"me yasa?
"Bana son Allura"
"Bout you are so big to say that"
Shagwabe fuska tayi"ni dai dan Allah karka faɗa ma kowa"
Jinjina kai yayi,ya juya ya wuce abin shi,
Mintuna kaɗan sai ga Ibrahim da Aunty maijiddarh,sai Bilki,
Kawai sai ganin mutane tayi tsaye a kanta,
Ihu ta kurma yanda kasan wacce za'a yanka ta mike tana ƙoƙarin gudu,
Da sauri Aunty maijiddarh ta rukota,
Hmmm ranar sunga hauka domin kuwa da kyar suka kai ta shiyan kaka da kuka da ihu,duk yanda aka so ayi Allurar dole hakura aka yi aka kyale ta,dan har da cizon Nurudeen tayi a hannu,gabaɗaya ta hargitsa gida,dole aka kyale ta,
Wurin shan magani ba tada matsala domin ko banza ta ci kwaya balle kuma wannan,
Bayan sati ɗaya,
Sai da taji sauki sosai sannan ta koma shiyan Ammi,bayan kaka ta kira matan gidan tai masu kyakkyawar kashedi akan bata yarda ko da wasa a ƙara cin zarafin wani ɗan aiki a gidan ba,idan kuma aka kuma yi mutun zan haɗu da ita,
Wannan dalilin ne yasa ta dan samu sauƙi,dan bata shiga shiyan kowa sai na kaka,
Sai dai idan ta haɗu dasu a hanya,
Tsakanin ta da yaran gidan kuwa ko kallon banza,dan sai dai su zage ta amma bata gaida su,tunda ba girman ta suka yi ba,har gara Aunty maijiddarh,tunda taga wani lokaci tana da kirki,
Zaman gidan gabaɗaya ya isheta domin ko wanda zata yi aiki domin shi bata ganin shi tun wannan ranar daya faɗa ma su Nurudeen in da take,dan ta tabbatar da shi ya faɗa masu.
Ganin ƙafar Ammi da sauƙi ne yasa taimata karya akan zata ganin Mahaifiyar ta wai jikin nata ya tashi,
Cikin tausayawa ta amince mata sannan ta haɗa mata tsaraba sosai,har da kaka,
Ranar da zata tafi ne ta fito wanka kenan sai gashi taga shigowar kira a wayar ta,duk da babu suna kuma yawancin lokuta da numbobi mabanbanta yake kira amma ta fahimce me kira,
Dan haka ɗauka tayi,
Abu na farko da yace shine"me yasa zaki tafi?
Shiru tayi tana mamakin ta yaya akayi yasan zata tafi bayan ko A'i bata san da maganar tafiyar ta ba,
"Ina buƙatar hutu" Ta bashi amsa.
"Ba dai akan dan abun da ya faru ba?
" Me kake nufi?
"Nasan komai,na kuma san kin warke,abu ɗaya kawai zai sa na bari ki tafi hutu saboda nasan baya ƙasa,ya tafi Sudan yin wani aiki tare da mahaifinsa,karshen watan nan zasu dawo,ina nufin nan da sati uku,kina da damar da zaki iya hutawa na sati biyu,domin jinyar mahaifiyar taki,ki tabbatar ya dawo ya same ki,sannan a wannan lokacin idan baki yi saurin cika min aiki na ba kome ya biyo baya ki yi kuka da kanki "
Cikin tsananin mamaki tace"ar you threaten me?
Kai tsaye ya bata amsa da"Yes"
Bai jira tace komai ba ya kashe wayar.
Kallon wayar dake hannun ta tayi,sabar bacin rai ne yasa ta buga wayar da ƙasa,me yake nufi,threatening ɗin ta yake saboda wani banzan aiki da bata masan amfanin me takardun zasu mai ba,sannan kuma duk halin da take ciki a gidan ya sani,to kodai ba ita kaɗai ɓace take mai aiki,
Tsaya ma tukun,ta ji yace ya tafi aiki Sudan tare da Mahaifinsa,bayan kuma ta san Abbu na gida,to wani mahaifi,Something is not right some were,tunda take aiki tare da VIP bata taba ganin yayi serious about wani abu ba kamar wannan aikin,
Komawa tayi ta zauna saman gado,ta shiga duniyar nazari,na farko shi dai ba Aljani bane,dole mutum ne,to waye shi,bata taɓa ganin shi ba,amma shi yasan komai game da ita,ta yaya,
Dafe kanta tayi,tana buƙatar sanin abubuwa masu yawa,amma kuma ta yaya zata yi hakan,
Ajiyan zuciya ta sauke tana jin kanta na daurewa,dan haka tashi tayi ta saka kaya sannan ta dauki Sim card ta jefa a jakka,
Ko da ta bar gidan ba wai ta tsaya a nan Kano bane,ko kuma tayi Abuja,kawai Jirgin Legos ta shiga dan gara taje can ta huta,in da anan suka hadu da Ummita.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*22*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Kwanan ta biyu a Legos ranar sun dawo daga cin abinci tana zaune tana danne danne a Laptop sai saki take yi,mikewa zauna tayi ta dafe kanta,kallon Ummita tayi dake zaune tana kallo a TV sai faman dariya take yi,
Kiran sunan ta yi"Ummita"
Amsawa tayi ba tare data juyo ba,
Cikin jin haushi ta wurga mata filo,"dan Allah malama ki juyo "
Juyowa tayi tana bata rai ta katse mata kallo"gani"
Kyara zama tayi"ni kan baki ganin kamar akwai abinda bai tafiya dai-dai?
"A ina kenan?
"Wannan aikin da nake yi"
"Me kike nufi,kinsan wannan karon ba abinda na sani"
A jiyar zuciya ta sauke"da fari aiki akan Young Ustaz da Baban shi,sai kuma na fahimta mijin Goggon shi ya ɓace ba'asan in da yake ba,"
"Eh to ɓacewa yayi,is a normal thing"
Girgiza kai tayi"is not normal,Nafisa tace min Shamsuddeen ba yaron Ammi ba ne mahaifiyar sa sun rabu da Abbu,to shi kuma Ustazu fa?
"Yaron Ammi ne da Abbu mana"
"Kai ina da wata a kasa,ki duba fa ki ga,karshen magana na da VIP cewa yayi Ustaz ya tafi wani aiki da Baban shi a Sudan,kuma a lokacin Abbu yana gida"
"Oh Biba ni dai ban fahimci abun da ke kika fahimta ba,ni dai a gani na da ki bata lokacin ki wurin wannan bincike ba gara ki samar ma kanki mafitar da zai kai ga waɗannan takardun kawai,ayi a wuce wurin"
Dan shiru tayi,kafin tace "tabbas a kwai wani abu a kasa,yauwa kin ga matso ki gani" Ta faɗa tana nuna mata fuskar Laptop ɗinta,"kin ga anan sunan mahaifin sa Abu Sufyan,shi kuma yana amfani da Suraj Abdul Basir,waye Abdul Basir? Me yasa yake amfani da wannan sunan a maimakon Abu Sufyan?
"Ni dai Biba ki yi a hankali domin na lura wannan aikin ba kamar irin wanda muka saba yi bane"
Komawa tayi ta kwanta"in Allah ya yarda idan na koma da zaran ya dawo zan kammala komai na dawo,kin san wani abu kuwa"ta faɗa tana kunna Sigari,
"A'a sai kin faɗa?
" Da na kammala wannan aikin London zamu koma da zama,gaba ɗaya Nigeria ya ishe ni"
Ihu ta saka cikin tsananin jin daɗi ta taso ta rungume ta suna dariya,
"Shi yasa nake ji dake Aunty Biba,gashi Alhaji Mansur sai damuna da kira yake akan yaushe zaki dawo,"
"Kyale dan wahala,ni yanzun bata nasu nake yi ba,so nake kawai naga na kammala wannan aikin in huta"
"Ai kuwa sai dai ki yi hakuri dan wallahi na riga na tura masa Address din mu,idan baki ganshi yau ba kya ganshi gobe"
Haka dai suka cigaba hiransu,
Zamanta a Legos ba karamin daɗi ya mata ba,dan har bata son ta tuna cewa zata koma wannan gidan aikin.
Ranar da zata koma aiki har da Kukan zuci sai da tayi,dan ta san zata koma aikin shara kenan da wanke-wanke,.
Tana sauka a bakin Get din ta haɗu da A'i tsaye tana jiran ta,
Ganin tana ƙoƙarin shigewa ne yasa ta kira sunan ta,
Tsayawa tayi tana kallon ta,mika mata wani karamin waya tayi tare da karamin takarda,bata jira tace komai ba ta juya ta wuce,
Da kallo ta bita,kafin ita ma ta shige cikin gidan,
Sai da ta gaida Ammi wacce tuni ta ji sauƙi,sannan taje shiyan kaka ta gaida ita,sosai tayi farin cikin ganin ta,kafin ta koma shiyan su,
Fadawa tayi kan fado tana warware takardar da A'i ta bata,
"Karki zurfafa bincike,domin yana iya faɗawa kanki"
Ta maimaita maganar ya kai sau nawa,to me taje nufi da zai iya faɗawa kanta,
Nannaɗe takardar tayi ta saka cikin kayanta,
Amira ce ta zo ta faɗa mata cewar Ammi na kiran ta,
Fitowa tayi ta same ta zaune a falo,
Tsugunnawa tayi a gefe"Mam,gani"
"Alhamdulillah,dama so nake na sanar dake naji sauki,dama Kaka ta kawo kine domin ki taimaka min,kuma yanzun na warke,duk da ban jima dake ba amma naji daɗin aikin ki,Kaka tace na tambaye ki shin kina ganin zaki cigaba da zama damu anan ko zaki koma shiyan kaka?
"Zan zauna dake anan Mam," Domin ta san zama anan din ne zai fi bata damar sanin duk abinda take buƙata,
"Kin tabba ta?
" Eh Mam"
Murmushi tayi"shi kenan tashi ki tafi "
Godiya ta mata sannan ta koma daki.
Da yamma ne taje kaima Kaka Abinci ta ji suna magana Momy Saudat Mamar su Nurudeen,tana magana da Kaka cikin marairaicewa yayin da Aunty maijiddarh ke zaune tana sharan hawaye,
"Kaka nasan fa kinsan abun da ke wakana a tsakanin Suraj da Maijiddarh,gabaɗaya taki kula kowa,ta nace sai shi kaɗai take so,duba ki ga yanda duk tabi ta lalace,na rasa yanda zan yi,duk wani hanya da zata bi ta samu shiga a wurin shi ya to shi,ko kiran shi tayi a waya baya ɗagawa,taki cin abinci ba ta da aiki sai kuka"
"To ni yanzun Saude me kike son nayi mata?
" Kaka Suraj yana jin maganar ki,kome kija faɗa kai zai amince,ni wallahi tsoro ma nake kar yaje can wurin wa'azin shi wata ta samu nasaran aure shi,tunda matan ma yanzun da kansu suke kawo mashi tallan kansu"
"Kinsan dai shi ba yaro bane ballantana na takura akan sai yayi abinda nake so,ita maijiddarh ta hakura mana,ko ta samar ma kanta mafita amma ni dai kam ba zan iya mai magana ba"
Kuka ta fashe dashi tana rarrafawa gaban kaka"ni dai Kaka ki yi wani abu kai,ni ba zan iya auren kowa ba in ba Yaya Suraj ba,dan Allah ki taimake ni"
Shafa fuskarta tayi"ya isa haka,bari ya dawo za'a san abun yi"
Rungume kaka tayi babu kunya,tana mata godiya kafin su fito shiyan,
Da sauri ta labe ta ƙofar gidan dan ta cikin gida ba wurin da mutum zai labe,
Suna fitowa tsayawa suka yi a ƙofar gida,Momy Saudat ce tace"ya kama mu ƙara dagewa akan wannan lamarin,domin na lura da take_taken Goggon ku,so take ta saka Khadijah a wannan lamarin,dan haka wannan karon idan ya dawo ki yi duk yanda za ki yi alakar ku tafi na da ƙarfi,bana son ya tsubuce mana"
Tsaki taja"Momy kin san halin Yaya Suraj yanda kika san mai zuciyar dutse haka yake,duk yanda mace za tayi ba ya daga kai ya kalle ta,shi yasa wani lokaci take ban haushi "
"To ko zaki hakura?
Zaro ido tayi" Rufa min Asiri Momy,wane ni,ai ba irin