Showing 96001 words to 99000 words out of 159134 words

Chapter 33 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt

27 Sep 2025

9740

take so,mun tambaye ta ko dama kuna soyayya ne tace a'a ita bata taɓa faɗa maka ba,kuma tana can ta tayar da hankalin ta sai kuka take yi shi yasa muka ce bari mu zo mu same ka"

Kamar wasu marasa hankali haka yake kallon su,nuna kanshi yayi "ni Yusuf din tace tana so?

" Eh kai tace,dan ko mu munyi mamaki"

Girgiza kai yayi"gaskiya ni bana ra'ayin soyayya da mace bare kuma Ummu Salma,ba zai taɓa bari ba"

"Waye ba zai bari" Cewar Abdulrahman,

Kai tsaye ya basu amsa "Baban ku,ko ya sani ne? Ya mai da masu da tambayar,

" Bai sani ba,amma bana jin za'a samu matsala ta nashi bangaren "

Wani irin murmushi yayi wanda suka kasa gane kanshi da manufar shi "to ai anan babban matsalar take,domin ba zai taba yarda ba"

"To me yasa wai kuke ganin rashin yuwar haka,daga kai har Mama,yanzun kuma kai ka faɗi haka,ko dai akwai abunda bamu sani bane dangane da kai Yusuf?

" Abdulmajid kenan,babu wani bu,sai dai ko da ace ma su sun yarda ni ba zan yarda ba"

Wannan karon kalaman shi ya fara basu haushe "me a tattare da Salma da har zaka ce kai ba zaka yarda da Aurenta,na tabbatar idan kyau kake butaka to tana dashi,idan kuma kuɗi ne ko tarbiyya kaima kasan duk gidan su ka zo,ko me babban magana akan wannan lamarin"

"Babu wani babban lamari amma kasan shi aure abu ne na ra'ayi to ni kuma Allah bai Daura min wannan ra'ayi ba,kuyi haƙuri sannan ku ba ƙanwar ku haƙuri ta nime wani ta aura" Yana gama gadar haka ya tashi ya shige cikin gida ya bar su nan zaune a baranda,

Kallon juna suka yi suna jinjina wulakanci irin na Yusuf wanda basu taba tsammanin haka daga gareshi ba,sun dauka zai amshesu da hannu biyu sannan yayi farin ciki akan lamarin ya nuna jin daɗin shi,sai gashi ya nuna masu saɓanin haka,

"Tashi mu tafi"
Mikewa yayi suka fito sannan suka samu abin hawa ya maida su har ƙofar gida,

Suna shiga shiyan su zama suka yi a nan falo saman kushin in da Abdulmalik ke zaman jiran su,
Yana jin shigowar su ya tare su"Kun same shi? Ya kuke yi dashi? Dama soyayya suke yi ko?

Dafa kafadarshi Abdulmajid yayi"duk yanda kake tunanin abun ba haka yake ba"

Zaro ido waje yayi"kamar ya?

"Zauna kaji"
Nan suka shiga ba shi lamarin duk yanda suka yi da Yusuf din har wutowar su,"yanzun ban san yanda zamu yi da Salma ba,kasan ita matum ce mai tsayawa akan magana daya har balle a kan abinda take so,yanzun duk wani shawara da zamu bata ba ɗauka zatayi ba,"

"To me zai hana mu same Baba da maganar" In ji Abdulrahman.

"A'a yayi sauri Gara dai mu fara dai-dai ta kansu tsakanin shi da ita sannan mu shawo kan Mama tukun na kafin Baba"

"Hakan yayi, yanzun mu je mu kwanta kun ga har ƙarfe goma tayi gobe ma san abun yi"
Da wannan shawarar suka tsayar in da kowa ya shige ɗakin shi ya kwanta kowa zuciyar shi cike da nimar mafiya ma kanwar su.

Washegari ta riga kowa fitowa wanda ita kanta Mama sai da tayi mamakin fitowar ta,domin ba ta zata ba,
Cikin sakin fuska ta gaida Mama,wacce ta kasa yin shiru "what the occasion"

Dan dariya tayi kaɗan "babu komai Mama,kawai dai ina cikin farin ciki ne"

A tunanin ta ko ta hakura da maganar su na jiya ne dan haka tace"ai gara da kika cire shi a ranki domin hakan zai fi maki"

Girgiza kai tayi"A'a ban cire shi a rai na ba,kawai dai sun min Alkawarin taimaka min ne"

"Su yannin naki? Ta tambaya cikin mamaki,

" Umm "ta fada tana haɗa shayi,

Bata ce mata komai ba har sai da ta tabbatar ta karasa shan shayin ta sannan ta kalle ta" Bana son ki saka yakinin ki da yawa a kansu,domin haka zai iya cutar dake,abu na biyu ko da ni na amince ki sani mahaifinki ba zai taɓa yarda ba ballantana ni ma kuma ba zan taba yarda ba"

Ji tayi nan take duk wani kwarin gwiwa data tashi dashi Mama ta sare shi"me yasa baki son Yusuf,me yayi maki da kika tane shi har haka Mama
Yusuf fa is a normal gay,yana aiki a kamfanin Baba,ana biyan shi Albashi wanda na tabbatar da zai iya riƙe mu,to Mama me kuma ake buƙata,na tabbatar da idan da Ace tun farko bai da tarbiyya Baba ba zai taɓa yarda ya shigo dashi cikin gidan nan ba,ke ma kin sani"

Kallon ta kawai take yi tana kuma jinjina irin fahimtar ta da kuma yarda da tayi da mahaifinta,tabbas data san shi waye da bata faɗi haka ba,dan haka ba tare data bata amsa ba ta mike ta shige daki abunta,

Da kallo ta bita cikin mamakin abunda tayi,ta dauko magana sannan bata karasa ba ta wuce,
Dan haka tashi tayi ta bita daki,in da ta same ta tsaye da waya a hannu daga dukkan alamu kira take kokarin yi,

Kallon ta tayi"lafiya?

"Mama baki ce komai ba?

Zama tayi bakin gado" Me kuma kike son na faɗa maki Salma wanda zaki fahimce ni?

"Kin ce kar na ji kunya a duk lokacin da nake da wani buƙata ko niman taimako na zo na same ki a matsayin ki na mahaifiyata zaki taya ni samun mafita,amma sai gashi a karon farko kina kokarin jefa rayuwa ta cikin hatsari ta hanyar hana ni aure"

Dafe goshinta tayi ta dan murza tana busar da iska cikin tsanin damuwa da lokaci guda ya baiyana a fuskarta "ina maki gudun aikata wani babban kuskure wanda zai ta bibiyar rayuwar ki na tsayin har a bada Salma! Ina maki gudun tafka babban kuskure irin wanda na aikata a baya!ina maki gudun rayuwa mara tabbas,kokonta da bullewa Salma! Bawai ban fahimci halin da Kike ciki bane,kawai dai ina tsoron halin da zaki shiga ne,domin duk irin nunin da zan maki,ba zaki taba fahimtar komai ba domin idanun ki a rufe suke wanda ni kaina bana fatan abunda zai buɗe maki su har abada balle ki fuskanci abunda ke gaban ki,sai dai ki sani auren wannan yaron da zaki dauko ma kanki tamkar mutum ne ya faɗa rami sannan yaci gaba da haka ramin wai a kokarin shi na fitowa har wata rana wannan ramin yayi zurfin da zai fado ya danne shi,
Ni idan da ace wani kika kawo ba shi ba wallahi zan yi farin ciki dashi na kuma taya ki karbar shi,amma Yusuf har abada ba zan taba karɓar shiba,domin kokin aure shi ba zaki taba samun abunda kike nima ba"
Kama hannun ta tayi duka biyu ta haɗa wuri ɗaya"ɗan Allah ki fahimce ni Salma,ki canja wani zaɓin zan taimaka maki kin ji?

A hankali ta zame hannun ta a cikin nata"Mama ki yi hakuri duk yanda naso na natsu na fahimce ki na kasa,domin har yanzun baki ba ni wani kwakkwaran hujja ba da zai hana ni son shi,dan haka ki yi hakuri har yanzun ina kan baka na Yusuf shine zaɓi na"tana gama fadar haka ta tashi ta bar mata ɗakin "

Da kallo ta bita,sai dai wannan karon zuciyar ta cike yake da rauni ganin irin kuskuren da yarta ke kokarin tafkawa a rayuwar ta,sai dai ko zasu kai ruwa rana ne ba zata taɓa bari hakan ya faru ba....
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*59*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*


Ganin lokacin tashin Baba yayi ne yasa suka shiga dakin shi da sallamah,
Cikin farin cikin ganin yaran nashi ya amsa yana sakar masu murmushi,zama suka yi kan kushin "Baba muna da magana"

Ajiye Turaren da yake fesawa yayi ya dawo ya zauna a daya daga cikin kujerun da suke zagaye a dakin, yana fuskantar su,ganin yanda suka ba maganar da zasu faɗa Muhimmanci suka natsu,
Yasa yace"Ina jin ku"

Ajiyar zuciyar Abdulmajid ya sauke kafin ya fara magana "Baba Salma ta faɗa maka ra'ayin ta game da tafiya makaranta?

" A'a,wani abun tace maku ne?

"Ta samu Mama jiya da maganar cewa ita bata son tafiya karatu London ba tare da Aure ba,ina nufin wai aure take so"

Dan shiru yayi na dan wani lokaci alamun nazari kafin ya ce"tunda har ta zaɓi haka to ba matsala ba ne,da ace taje tana aikata wani abu bayan idon mu gara da ta faɗa kun ga sai ai mata abun da take so,in yaso sai su tafi tare da mijin ta,ko ba haka ba?

Kallon juna suke yi suna sakin murmushin nasara domin basu ɗauka lamarin na wurin Baba zai zo masu da sauƙi ba,"haka ne Baba"

"To dama tana da wanda take so ne,ko kuma ta tsayar?

" Eh tana dashi Baba,sai dai kuma data fadama Mama sai cewa tayi sai dai bayan ranta dan bata isa ta aure shi ba,"

"Wannan ai maganar banza ne,bayan yarinya na son shi kuma har ta faɗa,so take ta saka ta a wani hali ko kuma so take na mata auren dole,karku damu zan fahimtar da ita amma kan aure sai an yi tunda suna son juna,tukunna ma waye yaron,waye mahaifin shi?

" Baba ai ka riga ka san shi,Yusuf ne me zuwa nan gidan "

Dan jim yayi kafin kuma kamar wanda aka tsikara tace"ba dai Yusuf ba?

"Shi Baba"

Nan take wani irin zufa mai matukar sanyi ya shiga fito mai daga jiki ta ko'ina,hankalin shi ya tashi yayin da yaji wani abu ya tsaya mai a rai"ba dai Yusuf ba,dama amanata zai ci yana soyayya da ƴar tawa bayan duk abinda nake ma shi bai ishe shi ba"

Kallon tsoro da mamaki suke mai,sai suke ganin kamar ba shi ba,yanzun fa ya amince amma kuma yake yi kamar bai gane me suke nufi ba,

"Baba dama soyayyar bari daya ne"

"Kamar ya?

" Shi baya son ta ita ce ke son shi,dama so muke ka faɗa ma iyayen shi ko zasu shawo kan shi "

Wani irin ajiyar zuciya mai matukar ƙarfi ya sauke wanda yasa sai da suka kara shan jinin jikinsu da wannan lamarin,gashi har share zufa yake yi yayin da idanun shi suka yi ja "to tunda baya son ta ai ba dole bane,ba sai ta nime wani ba,ni ban damu ba ko ma waye ta kawo zan aura mata amma banda Yusuf"

"Baba amma fa yanzun ka nuna amincewar ka me ya faru,shin me yasa baku son ta auri Yusuf,ko dai akwai wani abu dangane dashi ne wanda ya kamata mu sani,?

Kara share zufan daya karyo mashi yayi" Kawai dai ku bata shawara tabi shawarar mahaifiyarta,ku tashi ku tafi sannan bana son na kuma jin irin makamancin wannan maganar a gidan nan on dai akanta ne da Yusuf "

Cikin sanyi jiki da kokonton iyayen nasu suka fito daga dakin Baba yayin da suka samu Mama a falo zaune tana kallo a zahiri,amma idan ka fahimce ta da kyau ba kallon take yi ba kawai idanun ta ne a kan TV,
Duk zama suka yi kusa da ita,yayin da Abdulmalik ya dafa kafadarshi ta,"yin dogon nazari yana haifar da damuwa Mama"

Juyowa tayi tana ɗan lumshe ido"kanwar ku ke ƙoƙarin haifar ma da rayuwar mu da damuwa gaba ɗaya "

Matsowa Abdulrahman yayi cikin damuwa"Mama dan Allah ko dai akwai abunda kuke ɓoye ma na ne game da Yusuf ke da Baba banda baku son mu sani?

"Me ka gane Abdulrahman,shin wani abun ya faru ne?

" Mama munje mun samu Baba da maganar Yusuf da Salma,da fari ya yarda ya amince kafin sanin Yusuf take so,amma daga jin shine taje so,shima ya tashi hankalin shi ya nuna rashin yardar shi,Mama ko dai Yusuf yaron Baba ne bamu sani ba?

Kallon yaran nata take yi yanda duk suka tsira mata ido suna jiran karan bayani,
Girgiza kai tayi"Shi ba ɗan mahaifinku bane,domin mahaifinku ba shida wani ɗa a duniya,kuma na tabbatar da mata basu gaban shi,
Kawai dai akwai dalilin da yasa bamu amince da wannan auren ba,sannan ɗan Allah karku tambaye ni domin ba faɗa maku zan yi ba har abada kamar yanda shima mahaifin naku ba zai taɓa yarda ba har da shi kanshi Yusuf ɗin,domin shi yasan dalilin,
Abu na gaba shine kusan yanda zaku shawo kan kanwar ku ta bar wannan maganar ta canja wani"tashi tayi ta koma daki ta turo ƙofa,

Cakuɗe gashin kanshi Abdulmajid yayi"ohhhh,this doesn't make sense,kai na ya dau zafi,so nake na san wannan dalilin"

"Ni ma haka wallahi" Cewar Abdulmalik,

"Ku tashi mu je mu sami Yusuf tunda Mama tace ya sani sai mu rokeshi ta faɗa ma na"

Da haka suka bar gida,sai dai ko da suka je gidan su Maman shi ke shaida masu ya fita sai dai ba zai jima ba, dan haka suka zauna zaman jiran shi,
Ya ɗauki kusan awa daya kafin ya dawo,ko da ya gansu bai wani nuna zumudin zuwan nasu ba kamar sauran lokutan da suka saba zuwa har ya rasa ina zai ajiye su,

Jan kure yayi ya zauna yana miƙa masu hannu suka gaisa,"kun jima da zuwa ne?

"Eh amma ba sosai ba"

"Ai da kun kira ni"

"No ba damuwa tunda gashi ka dawo" Cewar Abdulrahman

"Da fatan kuna lafiya" Ya tambaye su, dan wannan karon dukansu su uku ne suka zo,

"Lafiya ƙalau,dama dai akan maganar jiya ne Yusuf,sai dai abin mamaki kamar yanda kace iyayen mu ba zasu yarda sai gashi hakan ne ya kasance dan har yanzun dukansu sun ƙi amincewa saboda wani dalili nasu wanda mu ba mu sani ba amma kuma kai kasani,shine muke rokon ka ko zaka iya faɗa mana ne yasa dukka suka ki amincewa da kai,menene dalili "

Ɗan dariya yayi wanda ya basu mamaki domin basu ga wani abun dariya ba acikin wannan maganar"shi Baban da Maman naku basu faɗa maku ba? Ya faɗa yana Daura kafa daya kan daya,

"Sun ƙi faɗa shi yasa muka zo ko zaka faɗa mana"

"Ai ba zasu iya faɗa maku ba,domin sirrin su ne"

"Dan Allah ka faɗa mana,menene wannan sirrin Yusuf" Cewar Abdulmajid cikin zakuwa,

Girgiza kai yayi"Umm umm,domin ƙwaƙwalwan ku da zuciyar ku ba za su iya ɗauka ba,May be ma zuciyar dayanka yana iya bugawa,dan haka"Let the sleeping dogs lie"(abar kaza cikin gashin ta)

"A'a Gara dai a fige ta"

"Kun ga ni iyaye na ada talawaka ne,saboda iyayen ku ne muka samu rufin Asiri har muka samu muhalli na kuma samu abun yi,ƙila shi yasa suke ganin rashin dacewar na aure ƴar su,ni ma kuma bai dace na aure ƴar mai gida na ba,kun ga gara dai da kasance ayi Cut your coat according to your clothes(dai_dai ruwa dai_dai tsaki) ku samar mata wani kawai "

"Wannan ba hujja bace Yusuf,kuma baka faɗa mana har yanzun ainahin dalilin ba"cewar Abdulmalik,

Ajiyar zuciyar ya sauke,yana mikewa tsaye" Kun ga ku tashi"

Duk kallon shi suke yi cikin rashin fahimta,

"Ku tashi mana"

Mikewa tsaye suka yi suna jira su ji me zai ce,

"Wannan ya zamo karo na karshe da zaku ƙara takowa gidan mu da sunan yi min maganar wata mace,bana ra'ayin ta,bana ra'ayin ƙanwar ku,bana sonta a takaice,ina fatan kun fahimta,dan haka ku zo ku fita" Ya fada yana nu a masu hanya,

Cikin tsananin jin zafin wulaƙancin da ya masu Abdulmajid ya shako wuyan rigar shi "kai har kayi kyau da arzikin da zaka ce baka son kanwar mu,in banda rigima da rashin sanin ciyon kai irin na Salma me zata yi da jaki mara hankali wanda bai san abun arziki ba irin ka,ko an faɗa maka muma muna son ka ne,ko kuma muna son ƙanwar mu ta aure mutum irin ka,daga yau idan ka ƙara ganin mu a ƙofar gidan ku duk abinda kaka dama ka mana,Stupid"ya faɗa yana ture shi gefe,
Bayan Abdulrahman ya samu nasaran cire hannun shi a wuyan Yusuf din wanda yake ta faman shafa makoshi da tari dan ba karamin shaka yayi mai ba,dama ya sani ko lokacin da yake zuwa gidan su duk cikin su babu wanda ya kai Abdulmajid zuciya,

Ko kallon su bai yi ba ya juya fuuu ya fita a gidan,dama wannan karon da mota suka zo dan haka buɗe gidan baya yayi ya shiga ya zauna yana hadiyar zuciya,dan babu abinda yafi bashi haushi irin yanda ya fito a gaban fuskar su yace baya son Salma,wannan abun ya ƙona mashi rai,
Ko suka iso suka shiga mota ba wanda yace ma ɗan uwan shi komai har suka isa gida,
Ya rigasu sauka a motar dan haka gani suka yi kai tsaye ya shige cikin gida,
Da sauri,suma bin shi suka yi,sai dai kafin su isa garya shige dakin Salma ya turo ƙofa,
Dole sai komawa falo suka yi suka zauna suna zaman jiran fitowar shi,

A zaune ya same ta tana danne_danne a waya,
Tsayawa yayi a kanta yana huci,
Dago kai tayi tana kallon shi,sai dai bata ce mashi komai ba,

"We need to talk"

"What happen"

"Ba zaki aure wannan yaron ba"

"Wa kenan?

" Wanda kike so"

Yusuf "

"Koma waye ba zaki aure shi ba,yanzun kam ina bayan su da Baba"

"Yaya" Ta kira sunan shi tana mamakin me ya faru daya hassalashi haka,

"Ido na fa ya kalla yace min baya son kanwata,wani irin cin fuska ne yafi haka,idan har kina ganin girman mu da darajan mu a matsayin mu na yannin ki yi ki fitar harkar yaron nan,in aure kike so akwai mazajen da suka fi shi komai wallahi zamu tsaya miki har sai kin aure shi,na maki aikawari"

Kallon shi take ido cikin ido"me zai hana kamin wannan alƙawarin wurin ganin na aure wanda nake so?Yaya ba wai ina son Yusuf bane dan in canja ra'ayi a kanshi a ko wani lokaci,A'a kawai ina son shi ne domin na aure shi,kayi haƙuri kome

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login