Showing 18001 words to 21000 words out of 159134 words

Chapter 7 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt

27 Sep 2025

9724



Buɗe first aid box,da Nafisa ta kawo yayi yana ciro wani kwalin cream wanda naga an rubuta Ketoconazole a jikin shi,buɗewa yayi ya ciro sannan ya ɗauki cotton Bud's guda daya ya tatsa Cream din a jiki sannan ya shiga shafamata a hankali yana kallon yanda take dan matse ido,
Koda ya kammala shafamata cream ɗin bai sake mata hannu ba,sai kallon hannu yake domin ba karamin jan hankalin yake ba.

Sai sannu kaka ke mata,
Haɗa ido suka yi dashi dake zaune ya wani hakimce yana shan abu a kofi,
Harara ta zuba mai,tana ɗauke kai,domin ba karamin haushe ya bata ba,ko sannu bai ce mata ba,
Ganin abunda ta mai me yasa ya kauda kai yana jinjina rashin kunyar ta,

Dariya Ibrahim yayi yana ajiye wayar hannun shi"ƴan mata ya kike hararar mana Young Ustadz"domin ya ga abinda ta yi,"Kaka ina kika samo yarinya mai kyau haka?

"Tubarkarla,mai taimakama Ammi ce,dazu ta zo,gashi Sorajo na ƙoƙarin kona yar mutane"

Jin yanda yake shafamata tafin hannu ne yasa ta zare hannun ta a cikin nashi tana kallon shi,
Murmushi ya sakar mata,
Ibrahim ne ya katse su"ni dai tamin Kaka,me sunan ta"

Ɓata fuska tayi"ni fa bana son shashanci,"

Mikewa yayi tsaye "Tsohuwa sai da safe"

"Ba zaka ce mata sannu ba,bancin ka kona ta da ruwan zafi"

Bai bata amsa ba yasa kai ya fita,

Cikin jin haushi tace "ku tashi ku tafi na sallame ku"

Mikewa suka yi suma cewa "tunda laifin wani ya shafe mu sai da safe"

Sakawa tayi Nafisa ta rakata har shiyan su sannan ta dawo,dan ita a nan shiyan kaka take kwana,

Washe gari da Asuba,tana barci taji wayarta na ƙara kamar zai fasa mata kunne,
Tsaki taja tana jawo wayar tare kashewa,
Ƙara kira aka yi,wanda sau uku tana kashewa,amma sai ƙara kira ake yi,
Ana huɗun ne dai ta ɗauka cikin jin haushin damunta da ake yi tace"pls abar ni in yi barci "

Daga ɗayan bangaren taji ance"tashi zaki yi ki fara gyaran falo ki daura abin kari "

Cire wayar tayi daga kunnen ta tana duba ko ƙarfe nawa ne "ƙarfe biyar dai dai yanzun"

Cikin tsananin gajiyawa da maganar tace"A'i ba zan iya ba barci nake ji"

"Dole zaki tashi domin haka aka tsara maki,dole sai kin shiga jikin mutanen gidan kafin ki samu ki cika aikin ki,dan haka tashi ki fara gyaran gida"

Ranar haka tayi kyaran falon har kicin tana hawaye,domin Allah ya gani ita wannan aikin azabtar da ita ake,sai da ta kammala har karin safe kafin ƙarfe bakwai,
Zuwa lokacin ji take kamar zata faɗi tsabar gajiya da ciyo da jikinta ke yi,
Ruwan Tea kawai ta iya sha sannan ta fito harabar gidan,
Kalle_kalle tayi,sai dai ba kowa a tsakar gidan,dan haka zagayawa tayi ta baya in da sai gashi tana hangar ɓangaren samarin gidan,
Karema tsarin jeren ɗakunan wurin kallo tayi,kafin naga ta nime wani dan dutse nisa kaɗan da wurin ta zauna,
Hannu naga tasa kasan hijabinta sai gashi ta ciro karan sigari ɗaya tare da abin kunnawa,
Tunda ta saka abiki ta fara zuka har wani lunshe ido take tana jin wani natsuwa na sauko mata,haba ta yaya za'ayi ace wani tabar shaye-shaye,ai gara kawai a cillata rijiya,

Jin kamar karan tafiya ne yasa ta dago kai a firgice ta na kallo wurin,
Sai dai cikin rashin sa'a idanun su ya faɗa cikin na juna,wanda ba ƙaramin firgita tayi ba.......

🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*14*

*Na mai da Littafina mai suna a sama na kuɗi,tare da JAURO,idan kina son daya 300,dari uku,guda biyu kuma da Yar Tsanar Zinari tare da Jauro,dari biyar 500,ko wani daya dari uku*
*Hauwa Umar,Zenith Bank, 2284905309*
*ko katin waya na MTN,tare da turo shedar biya ta 08141644865*


Cikin sauri ta maida hannun ta baya tana fuskewa,tare da ɗauke idanunta cikin sana,

Shima ɗauke idon shi yayi a kanta yana turo kofar daya buɗe ya shege tare da maidawa ya rufe,
Banɗaki ya shiga yayi wanka,sannan ya canja kaya zuwa riga da wando na ratsattsen shadda fari kar,sai ɗaukar ido yake,
Yana gama shiri ya fito daga bangaren su,ya nufe shiyan Ammi,
Koda yayi sallamah babu kowa a falon dan haka samun wuri yayi ya zauna yana daddanna waya,daga dukkan alamu abu mai muhimmanci yake yi,

Sam bata lura da mutum dake zaune a falon ba,da fari dogun tsaki ta fara ja tana rike Kwankwason ta,"waiyo Allah baya na,Allah ya tsina ma VIP,gara aikin komai da wannan"ta faɗa tana komawa kicin,

Jin tsinuwar da aka yi yasa ya dago kai dan ganin wacce tayi wannan lafazin a cikin gidan su,domin yasan tsunuwa ba ɗabi'ar su bace,sai dai ko da ya dago bai ga kowa ba,tsirama hanyar kicin din ido yayi na ɗan lokaci kafin yaci gaba da abinda yake yi,
Ammi ce ta fito falon domin ta san cewa da safen ne zai wuce dan zai gudanar da wa'azi a Jos,
Tunda ta hango shi zaune ta saki murmushi,wato dai ba zai shigo dakin ta ba,domin haka ɗabi'ar shi take,baya taɓa shiga dakin ta da sassafe haka,

Jin takun takalmin ta ne yasa ya ajiye wayar hannun shi yana mikewa,karasawa yayi inda take ya riko hannun ta yana sumbata,"Good Morning Ammi"

Shafa kanshi tayi"Morning Sweet heart,Allah ya Albarkaci rayuwar ka"

"Amin Sweet Ammi"riƙo mata hannu yayi suka zauna kan kushin,

Ɗan ɗaga murya kaɗan tayi ta na kiran sunan " Biba,Biba"

Da sauri ta fito kicin tana goge hannu tare da amsawa ta karaso in da suke tana amsawa,cikin girmamawa ta tsugunna "Mam gani"

"Ɗan Allah ki kawo ma yaro na kofin shayi, amma karki sa madara da Sugar,sannan kar kisa tafasasshen ruwa,ki yi amfani da wanda ya ɗan fara hucewa amma ba sosai ba"

"Yes Mam" Ta faɗa tana satar kallon shi,
Da sauri ta dukar da kai tana mikewa,a zuciyar ta tana raya,na shiga uku,ba dai wannan bane yaron matar nan oh young ustaz kenan,hakan na nufin akanshi da baban shi zata yi aiki, ya Allah gashi ta gwabsa tun a matakin farko,me yasa da ya zuba mata ruwan zafi bata haƙura ba,Allah ma yasa dazu bai ga tana shan sigari ba,kai data shiga uku in dai wannan aikin ya lalace a wurin Vip.

Ta gefen ido yake kallon ta tun lokacin da tsugunna a gaban Ammi har ta koma kicin,
"Ammi wace wannan? Ya tambaya yana cigaba da danna waya.

" Sabuwar mai taya ni aiki ce wacce kaka ta dauko "

"Ammi bana son ta,ki sallame ta,zan sa asamar maki wata mai hankali"

Kallon mamaki take mai,domin tunda take dashi wannan ne karo na farko data taba jin yayi magana akan al'amarin daya shafi cikin gida,dan haka ƙara maida hankalin ta tayi kanshi,tare da amsar wayar dake hannun shi wanda yake daddannawa ta ajiye gefe "yaro na,faɗa min,shin akwai wani abin ne,ko ta maka wani laifi nr?
Ɗan murmushi ya sakar mata ganin lokaci ɗaya tana ƙoƙarin shiga damuwa" Ammi na,ki kwantar da hankalin ki,babu komai,kuma bata min komai ba,kawai dai bata min bane Ammi,ban yarda da yarinyar ba,kamar akwai abinda take ɓoyewa "

Ajiyar zuciya sauke"batai maka ba,kuma kana zarginta "

Jinjina kai yayi.

"A ganin dana ma yarinyar ban fahinci wani abu tattare da yarinyar ba na damuwa ba,tana da kokarin aiki daidai gwargwado,na yaba da tsaftarta da kuma girkin ta,sai dai ban san Me ka hango ba a tattare da ita wanda yasa harka fara zargin ta,wanda ni ban hango ba,abin mamaki ban taba jin kace wani bai maka ba sai yau,ban sani ba ko zargin da kake mata ne yasa kace bata maka ba,amma dai na san kasan cewa babu kyau kace halittar Allah bai maka ba,kuma insha Allah dana kara samun sauki da yardar Allah zan sallame ta,tunda kaka ce ta kawo ta,dole nayi haƙuri da ita na dan wani lokaci,kuma ni ma zan saka ido a kanta "

"Insha Allah zan kiyaye Ammi," Kafin ya kara magana sai gata ta fito hannun ta riƙe da ƙaramin Tea plate mai dauke da ƙaramin kofin shayi,
Ajiye mashi tayi a gaban,ba tare data dago ba ta mike zata wuce,
Ji tayi ya ce ma mamatshi "ki yi hankali da ita,sannan ki fara kasa ido a kanta,da zaran kinga abinda baki yarda dashi ba dangane da ita ko da kaɗan ne,ki sallame ta,karki damu da kaka ta kawota,ni zanji da komai"

Iya nan wakai taji ta karasa shiga kicin,

Jingina tayi da kofar kicin ɗin,wato dai daga dukkan alamu da ita yake yi,zargin ta yake yi,kuma ya sanar da mamarshi,Allah yasa bai sanar da ita batun shan tabar ta ba,dole ta fara takatsantsan ta samu ta karasa wannan aikin,
Komawa tayi ta bakin ƙofar fitowa ta labe da kyau ta yanda zata iya jin me suke faɗi,

"Idan ka tafi yaushe zaka dawo"

"Nan da kwana uku insha Allah,domin a local government uku zanyi wa'azi a garin"

"Pls Suraj ka dunga saka kayan sanyi,domin kasan yanzun lokacin sanyi ne kuma Jos a kwai sanyi sosai,ka dunga shan ruwan zafi akai_akai,kar ka bari mura ya kamaka kasan yanda yake maka"

"Insha Allah Ammi"

Ɗan marairaice fuska tayi"gashi Abbu ku bai dawo ba,kai kuma zaka tafi ka barmu ni da kanwar ka,gabaɗaya in baku gidan baya daɗi,pls karka je ka daɗe "

Ɗan dariya yayi"karki damu Ammi,Abbu ma zuwa jibi insha Allah zai dawi,so karki damu,"

Murmushi ta sake tana ɗan daka tsalle kaɗan tare da dunƙule hannun ta"Yes "tafiya zai yi zuwa Jos kuma har na tsayin kwana uku gashi mai gidan ma baya nan," Waiyo daɗi, this is the right time da zan gama wannan aikin na bar wannan gidan kafin su dawo"
Cikin jin daɗi ta koma kicin dan karasa kife kayan data gama wanke wa,idonta ne ya sauko a kan inuwar mutum,
Ɗan tsayawa tayi jim,tana kallon inuwar,a hankali ta ƙarasa ta jikin windon tana jan labulen windon baya tare da lekawa,tabbas mutum ne ke a lebe a jikin windon,sai dai duk yanda taso ta iya hango wani abu dangane da wanda ke wurin bata iya ganin komai ba,
Komawa tayi ta tsaya tana nazari,kenan hakan na nufin labe ake masu,kenan dai ace ba ita kaɗai bace keda buri a akan wannan aikin,

Da sauri ta zagaya ta ƙofar kicin din ta fita,sai dai cikin rashin sa'a tana isa sai dai hangar bayan na miji tayi,to waye wannan kuma,lallai akwai matsala dole tayi sauri tayi komai kar ya zamana abin harin su ɗaya,
Koda ta koma ta samu harya fita,ita kuma Mam ta koma ɗakin ta,
Yanzun ta wata hanya zata bi ta samu ta fara shiga dakin Abbu kafin dakin wannan ɗan rainin hankalin,
Dole tana buƙatar sanin komai daga nan zuwa gobe,domin iya lokacin da take dashi kenan,gashi daga dukkan alamu wannan matar bamai bari a shigar mata daki miji bane koda ta hanyar shara.
Komawa tayi ta zube kan gado tana runtse ido akan dole sai ƙwaƙwalwarta ta fara aiki,

Yana fita daga falon bayan sun yi sallamah da Ammi,wurin parking ya nufa inda yana isa aka buɗe mai kofar mota ya shiga sannan aka maida aka kulle,
A hankali motar ya fara tafiya dan barin harabar gidan,
Jinginar da kanshi yayi a jikin set yana lumshe ido na wani lokaci,
Motar na gama barin gidan direbobi suka hau kan hanya da kyau,
Gani na yi ya saki wani lallausar murmushi na gefen baki,wanda ba karamin kyau yayi ba,duk da bansan na Menene ba,

Amma a zuciyar shi kuwa rayawa yake lallai wannan karon daga dukkan alamu tarkon shi zaiyi babban kamu,wanda yana ganin ta hanyar wannan Beran ne zai kai ga Asalin abin Farautar shi,
Gabaɗaya shiyansu Abbu zagaye yake da Camera ta ko ina har izuwa shiyansu na samar,wanda babu wanda ya san dasu face shi,
Wannan karon ya shirya wasan da gaske,

Sai dai kuma wannan halitta kallon ta kawai yake,amma tun ganin farko daya mata ya riga ya shaida ita waye,
Ya san yana da mantuwa akan abinda ya san baida amfani,idan kuma lokacin amfanin shi yazo yana tunashi,haka ƙwaƙwalwar shi take,dan haka tsaf ya sheda ta,wato dashi zata yi wasa ko,lailai bata san waye shi ba,amma a hankali zai fahimtar da ita ta yanda da ƙafar ta zata bar gidan,
Wani murmushin ya kuma saki yana buɗe idon shi,tare da fara ma Annabi kirari a zuciyar shi.


*this is just the beginning*

*Yanzun Aka Fara*
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*15*

*Na mai da Littafina mai suna a sama na kuɗi,tare da JAURO,idan kina son daya 300,dari uku,guda biyu kuma da Yar Tsanar Zinari tare da Jauro,dari biyar 500,ko wani daya dari uku*
*Hauwa Umar,Zenith Bank, 2284905309*
*ko katin waya na MTN,tare da turo shedar biya ta 08141644865*

*Not edit*

Jin an dafata tare da girgiza ta yasa ta dago kai a ɗan razane,

"Lafiya Biba tun dazun Ina ta magana amma kinyi zirfi cikin tunani,meke faruwa ne"

Ajiyar zuciya ta sauke me ƙarfi tana dafe kirjin ta,"Hmm,babu komai Nafisa,wai ina imagine ne a kan faruwar wani lamari mai tsayi,kin san kuwa a kan waye"

Girgiza kai tayi"A'a "

"A kan Young Ustaz"

Ɗan zaro ido tayi"Young Ustaz kuma?

"Eh,wai ina imagine ne yace ma Mam baya so na,bai yarda da ni ba,kinsan wani abin mamaki"

Nan ma girgiza kai tayi domin da tafara kulle mata kai,

"Wai har ina dab da barin wannan gidan bayan na kammala aikina,amma sai gashi kin tasheni daga mafarki na,naso ace naga yanda abin zai kasance," Kallon ta tayi"me yasa kika min magana?

"Ohh yi hakuri,dama nazo wucewa ne na hange ki anan,shi yasa na zo"

Matsawa tayi "zauna anan"

Zama tayi kusa da ita"na gode "

Jin an kara buɗe ƙofa an fito ne yasa ta kalle wurin,
Mutumin dazu ne dai ya kuma fitowa ya tafi,
"Waye wannan"

Kallon wanda ta nuna mata tayi"Yaya Shamsuddeen kenan"
"Amma ba'a giddan yake ba ko"
"A gidan yake,baƙi taɓa ganin shi a shiyar ku ba?
" A'a "
"To ai shima yaron Abbu ne,sai dai shi Mamar shi da ban ne,"
Cikin mamaki take jinjina kai,domin a list ɗin da aka bata babu sunan shi a ciki"to shi ina Mamar shi"
"Gaskiya ban sani ba amma dai a yanda naji sun rabu da Abbu"
"Me ya raba su?
Kallon mamaki take mata" Ya za'ayi in sani"
"Oh haka ne,never mind me,amma suna kama sosai da Ustazu,dan dazu ma na ɗauka shi ne,har na tafi mafarkin zaune"

Dariya tayi"mafarkin zaune ba,to bani labari akan mafarkin ki,"

Ita ma dariya tayi"kinsan wani lokaci mutum na zaune haka kurin zai kama imagining wasu abubuwa na faruwa,faɗa min halin Ustazu da yayanshi "

Wannan karon ma sai da tayi dariya"ɗan Allah Biba,karki ɓata ma young Ustaz din mu suna,wai ustazu"

Tabe baki tayi ba tare da tace komai ba,
Mai do fuskarta tayi ta kalle ta"ya cika girman kai,sai ya dinga kallon mutane kasa_kasa"

"La aikuwa Yaya Suraj bai da matsala,kawai dai kin mai rashin fahimta ne,kuma kinsan wani lokaci idan ba wai ka zauna da mutum bane baka sanin halin shi,daga shi har Yaya Shamsuddeen wallahi ba su da matsala,ɗan garama yaya Suraj wani lokaci zai dan maka magana,amma shi kuwa Yaya Shamsuddeen da wuya ki ganshi cikin gida,"

"Waɗancan ɗakunan kuma nasu waye"

Nuna mata take da hannu "kinga a gefen na yaya Suraj na Nuriddeen ne,sai na Ibrahim da Salman"

"Gidan akwai mutane har haka ne,su kuma ya'yan mutum ɗaya ne su?

" A'a,kawai dai bari na miki ƙwari_ƙwari,a yanda dai na sani,ita Kaka da kike gani Mijinta babban malami ne,a hanyar shi na zuwa wa'azi Sudan suka yi hatsarin jirgi ya rasa ran shi,
Tana da yara uku maza ɗaya mace,
Abba Al-Mustapha shine babba yana da mata daya mai suna Hajiya Rahama,suna da yara uku,Yaya Ibrahim,sai Aunty Hajjo wacce tayi aure yaranta biyu,sai karamar su Zainab,
Abba Al-Mustapha Custom ne.

Na biyu kuma shine Abbu Sufyan,na faɗa maki ya taɓa aure amma sun rabu da matar wanda suna da yaro ɗaya da ita,shine Shamsuddeen,daga baya kuma ya aure Malama Hafsat wacce ta haifa mashi yara biyu,Yaya Suraj sai ƙanwar su Amira,
Abbu Babban malami ne kuma ɗan kasuwa,shi kuma yaya Suraj duk da babban malami ne kamar mahaifin shi amma yana aiki ne da EFCC yana amsan Albashi mai tsoka.

Na uku kuma Dady Ahmad shi kuma Soja ne babba,bai cika zama a gida ba yaran shi biyar,Nurudeen,sai Aunty Atika wacce wata biyar kenan da akayi auren ta,sai Aunty maijidda,sai Salman da Bilki "

Na huɗun su kuma Goggo Hasiya,ita ta taba aure sai dai a yanda na samu labarin mijinta ya ɓace ba'asan inda yake ba,sai dai wasu na cewa guduwa yayi ya barta da ya'yanta,wasu suce sace shi aka yi,Allah kaɗai yasan gaskiya sai su,tana da yara biyu,Hadiza da Khadija, duk suna zaune ne a nan gidan ita da yaranta,sannan kuma kiyi hankali da ita dan masifaffiya ce na karshe,
Sannan ko wani shiya suna da ma'aikata,
Wannan shine labarin mutanen gidan,Halin su kuma a hankali zaki fahimce halin ko wanne daga cikin su,sai dai abinda zan faɗa maki shine kiyi hankali da Nurudeen da Ibrahim,domin ba kananan yan son aci duniya bane"

"Me kike nufi"
"Karki damu a hankali zaki gane me nake nufi"

Ajiyar zuciya ta sauke tana mikewa "kinga tashi mu tafi,gashi har after Nine O'Clock na safe,bari na je na fara shirin daura girki,na gode da labarin ki"
Dafata tayi "babu damuwa"
daga nan kowacce ta wuce ɓangaren da take aiki,

Har zata shige daki sai kuma ta dawo ta tsaya a tsakiyar falon tana kare ko'ina kallo,haka kurun zuciyar ta ke raya mata akan ta duba ta gani kar ya kasance tunanin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login