Showing 135001 words to 138000 words out of 159134 words

Chapter 46 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt

27 Sep 2025

9750

kuma ta mike tana nufar banɗaki da gudu,
Cikin kankanin lokaci ta yi wanka ta shirya cikin doguwar riga na jallabiya,sai rigar sanyi mai nauyi da Ammi ta aika mata dashi,
Koda ta sauko duk suna falo harda Grandma,

Kallon Agogo Ammi tayi"yi sauri ki karya,kin san nan basu daukar African time "

"To Ammi" Cikin sauri ta dauki ruwan shayin da aka haɗa mata wanda ya dan sha iska,tana kurba tana tura soyayyen ƙwai,

"Ammi muje na gama" Ta faɗa ta karɓar keken da Grandma ke zaune tana turata a hankali,

Su suka taimaka mata ta shiga mota sannan Driba ya ja su,

A bakin wani tangamemen Kotu wanda ya amsa sunan sa suka parkar a wurin parking,

Koda suka shiga a wani babban ofishi suka zauna,ko minti goma ba su yi ba aka ce su shigo za'a fara kowa ya halarta,

A wasu manyan kujeru Alkalaine dattawa guda biyar,
Sai kuma wadanda bata sansu ba,amma abinda ya bata mamaki shine ganin Pa,Nadiya,da sauran yannin ta,sai Abbu,Shamsuddeen,Dady,Abba,Nurudeen,kai ikon Allah,
Dan can ba kaman nan bame da a cika koto,wannan shari'ar irin na Family ne kawai,

Kallon Ammi tayi"kalli su Abbu yaushe suka zo?

"Ki natsu" Ta faɗa ba tare data kalli in da suke ba,

Kallon mamaki take mata,sai dai bata ce komai ba,

Wani ne ya tashi da takarda a hannu ya fara magana kamar haka"wannan shari'a ce da aka fara shekara goma sha ɗaya da suka wuce,amma saboda rashin hujja da kuma rashin lafiyar ɗayan daga cikin hujjoji yasa yasa aka daga shari'ar har ta samu sauƙi,to yanzun gashi Allah yayi ta tashi cikin aminci,kamar yanda aka fara to yanzun za'a daura daga in da aka tsaya,sai kuma wasu daga cikin nan waɗanda aka gaiyato su a bisa yardar gwamnatin garin su,tare da wakilan gwamnatin,suma sun iso ne a safiyar yau"

Daya daga cikin Alkalan ne yace "Dr Aisha ko zaki iya fitowa ki kara fada mana abinda ya faru shekaru goma sha ɗaya baya"

Ammi ce ta tashi ta tura Grandma zuwa stage,ita sai dube dube take ko zata hango Suraj,sai dai sam ta kasa ganin shi,
Dole ta mai da hankali kan Grandma da zata fara magana.

Da farko Ahalin mu sun kasance daya daga cikin sanannun mutane a garin Mardesh,saboda Arzikin da Allah ya basu,sai dai kuma Allah bai yi su da haihuwa ba,shi yasa idan har aka samu haihuwa a zuri'ar akanyi sati ana shagali,
Ahalinmu basu yarda da auren bare,sai dai auren haɗi,
Mahaifina ya auri mahaifiyata mai suna Mariya,a lokacin baya auren haɗi ne kuma ba sonta yake yi ba,sai da suka shekara goma da aure sannan Allah ya basu haihuwa na,ina da shekaru bawai a duniya,wani aiki na buɗe sabon Company su ya kaishi South Africa,anan ya haɗu da wata yarinya mai suna Linda,sunyi soyayya sosai da ita,ba tare da aure ba ƙaddara ciki ya shiga,sai da ta haihu sannan ne dangi suka samu labari,a lokacin an yi tsiya sosai domin cewa sukayi zasu kore shi acikin dangin mu,Mariya da Hassan,dan uwan mahaifina su suka tsaya mashi,sannan dangi suka hakura,da Sharadin zai musuluntar da ita ya aure ta,kasancewar yana sonta shi yasa ya amince,mahaifiyata tayi zaman hakura dasu sosai saboda mahaifina kiri kiri yake nuna yafi son Pa a kaina,sai dai mahaifiyata bata nuna komai ba,a lokacin dana cika shekara goma ta tara mahaifiyata ta rasu,mutuwar da ta girgiza mahaifina domin zazzaɓin sati ɗaya tayi,sai dai ko sannu bai ce mata ba,saboda a tunanin shi zata tashi,ya manta cewa mutuwa bata sanarwa,yayi daya sanin rashin kyautata mata,ko sau daya bai taba furta mata kalmar so ba,
Ba na son zama tare da Linda,dan haka na koma digan dan uwan Baba na Hassan na zauna tare da matarshi da kuma yar shi mai shekaru goma,
Ana cikin haka mahaifina ya fitar min da miji mai suna Usman,babu gardama na amince kasancewar sa mutum mai nagarta kuma ya san abinda yake yi,
Inada shakara biyu a gidan miji na kammala master's dina na fara aiki,
Bayan shekaru shida da aure na mahaifina ya kamu da ciyo mai tsanani a lokacin Pa yana da kusan shekara goma sha takwas a duniya,
Mahaifina yayi kira na nida mijina,
Dana same shi ne ya nuna min wani akwati ƙarami dake gefen shi yace na ɗauka na buɗe,ina buɗe sai ganin dutsen Diamond na yi tare da wani takarda,a kalla ko a wanan lokacin kuɗin Diamond din ya haura biliyoyin kuɗi,
Tambayar shi nayi Baba wannan na menene,
Sai cewa yayi tunda ya auri mahaifiyata bai taba mata komai ba,nima haka,wannan Diamond din dukiyar daya mallaka tare da gadon da mahaifiyata ta barmin ne ya haɗa ya siya wannan dashi,dan haka ya mallaka min shi har duniya ta nade,
Nati kuka sosai na kuma gode masa,a lokacin Linda dake labe da ɗanta ta fito ta nuna Babana akan wannan abinda yayi cin amana ne,to su mai ya bar masu,girgiza kai kawai yayi ya ce ya bar mata Company shi na garinsu,sai kuma wannan gidan da yake ciki ta je ta rayu ita da ɗanta,sai kuma kuɗaɗen da bansan adadin su ba daya basu,

Ni dai mun wuce tare da mijin na,ba'a dau kwana biyu ba Allah ya mai rasuwa,
Bayan kwana biyu da rasuwar shi ta tattara ita ɗanta suka koma Sauth Africa,
Ko wata hudu ba ayi da rasuwar mahaifina ba Allah ya bani ciki,nayi farin ciki sosai na kuma yi kukan murna,
Yan wata tara na haifi dana mai suna Abdul basir,
Yaro ne wanda ya taso da natsuwa da hankali,ga tausayi,
Ta gefe ɗaya kuma yarinyar Kanin Baba na Hassan tayi auren Shamsiya,

Abdul basir nada shekaru biyar Shamsiya ta haihu,in da a wurin haihuwa Allah ya mata rasuwa,mutuwarta ta girgiza dangi sosai,nayi kuka kamar me,domin mun shaku sosai da Shansiya,hakan yasa na roƙi mijinta wanda yake matsayin Ɗan'uwa a gari saboda auren dangi ne ita,akan su ba ni yar ina son zan kula da ita,babu musu aka gabi,saboda dukkan mu daya ne,sai dai da Sharadin ba zan taba shayar da ita Nono ba saboda auratayya na iya shiga tsakani,cikin sauri na Amince,bayan kwanaki biyar yarinya taci suna Hafsan (Ammi kenan) na riƙe Hafsat a matsayin ƴar dana haifa,kusan tare da Abdul basit muka yi rainon ta,dan barci kadai ke raba su har girma,dan saboda ita yaki yarda yaje wani gari yin karatu,

Shi kuma bangaren kanina lokaci lokaci na kan je na duba shi,shima ya zama babban mutum har yayi aure,

Lokaci ne yayi tafiya mai matukar nisa wanda a hankali har Allah ya nuna min girmar yarana Hafsat da Abdul,wanda tana da shakara goma sha takwas ta nuna babu wanda take so sama da ya'yanta,idan bashi ba bata jin zata aure wani,mukan dama abinda muke so kenan,ai kuwa ba'a dauki lokaci ba aka ɗaura masu aure,sai dai suna zaune ne tare da ni a nan garin Mardesh,

A lokacin da muka fara fuskantar barazana ta farko shine a lokacin da Hafsat ta haife Suraj,yana da wata biyu,aka kara turo min wasika akan na bayar da wannan Diamond din dana mallaka a wurin Baba na ko a kashe iyalaina,
Da fari na shashantar da maganar,amma da abun ya kai har cikin gidan da nake ake shiga a ajiye mun wasika duk yawan Jami'an tsaro yasa na fara tsorata,na faɗa ma mijina,shine ya bada shawara akan mu dauke takardar Diamond ɗin wanda idan har mutum yayi nasarar satan Diamond din in babu wannan takardar na shaidar mallaka babu ta yanda za'ayi ya iya fitar dashi ko da tsayin shakara nawa ne,haka kuma ko fasashi akayi to tabbas wurin siyarwa da kwaji sai an gane na Ahalin mu ne,

Dan haka muka tattara muka dawo garin London da zama har da su Hafsat,shi kuma takardar muka bada ajiyar shi ba tare da sanin kowa ba haɗe da Diamond ɗin,

Tun daga lokacin sai muka samu sauƙin komai har sai da jikana Suraj ya kai shakara goma,

Wata rana na dawo gida daga wurin aiki na taradda Hafsat zaune a falona tana kuka,
Hankali na ya tashi dan haka da sauri na karasa in da take na rungume ta ina tambayar ta lafiya,
Cikin kuka take sanar dani cewar Abdul basit yana cin amanar ta ba zata iya zama dashi ba ya sake ta,
Jin wannan kalmar daga bakinta yasa hankali na yayi kololuwa wurin tashi,domin saki abu ne da ba'a taba yi ba a dangin mu,
A lokacin nayi rarrashin duniya amma taki hakura,na kira shi shima nayi tambaya har nayi fushi yaki ya fada min abinda ya faru,sai ma kuka da yake yi akan na riƙe ta tayi hakura ba zai iya rayuwa babu ita ba,

A lokacin da nayi kokarin kara bata haƙuri sai nuna min hotunan shi tayi wanda yake tare da mata cikin tsiraici,abin yasa zuciyata girgiza,sai kuma kalmar da ta faɗa na cewar idan har ina kallon ta a matsayin Ƴar dana haifa na saka ya sake ta,

Juyowa nayi gare shi,cikin mutuwar zuciya dana gangan jiki,sai dai kafin ince mashi wani abu,ya buɗe baki da kyar cikin kuja ya furta mata ya sake ta saki ɗaya,sannan ya tashi ya fita,tunda ya bar gidan bai ƙara dawowa ba,sai dai muna waya dashi lokaci-lokaci,bayan tayi Idda da watanni biyar wanda har lokacin muna tare kuma babu abinda ya canja a tsakanin,ta kawo mana wani a matsayin wanda take so wanda ni bansan in da ta haɗu dashi ba,wato Abbu Safwan,nasan zata fuskanci matsala daga wurin dangin mu,amma da taimakona ta aure shi,duk da har raina ba wai ina kaunar shi ba ne,
A ranar da aka ɗaura auren su a ranar aka sace Suraj...




🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*83*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*


Hankalin mu ya kai kololuwa wurin tashi,lungu da tsako yan sanda nima suke sai dai babu labari,Kakanshi ne yace ai mu kwantar da hankalin mu ayi trackin din Suraj ta hanyar zoben dake hannu shi wanda ya bashi a matsayin kwatar karin shekara,
Da wannan muka yi amfani wurin gane in da suka kai shi a cikin wani sohon gini na wani unguwa,ba karamin fafatawa akayi da yan sanda da barayin ba kafin su samu nasarar dauko shi,inda suka kashe mutum biyu cikin barayin,suka kuma kama mutum daya,
Da ka tambaye shi dalilin kama Suraj din sai cewa yayi suma kwangilar sace shi aka basu,kuma basu san wanda ya saka su ba,abinda da yasa kuma suka karɓi aikin saboda na kuɗi ne masu yawa aka saka a kan duk kungiyar data samu sa'ar sato shi,
Wannan bayanin nasu yasa Hafsat ska kuka tare da roƙo na akan dan Allah na basu Suraj su tafi dashi Nigeria,ba zan iya hana ta ba saboda ina matukar son ta,duk da muma na jin yanda zamu rabu da jikan mu,ta gefe ɗaya kuma ga mahaifinsa,sai dai shima ko ba komai Hafsat kanwa ce a gare shi,zai iya yin komai domin faranta mata,shi yasa ko da na faɗa masa hukuncin daya yanke bai Musa ba,domin dama shi ba mai jayayya bane a gare ni,
Dan haka a washegari ranar suka wuce dashi,

Sai da tayi wata biyar hudu sannan muka kwaso muka zo dubata har da Abdul basit,a gidan da muka saka aka yi mana ana muka sauka,
Munyi farin cikin ganin ta ita da Suraj cikin farin ciki da ƙoshin lafiya,gata kuma har Allah ya azurta ta da samun ciki,
Mun kai wata biyu a garin sannan muka koma London,bamu kara dawowa ba sai ta haihu,
A gaka rayuwa ke tafiya mana sai dai kuma shi Abdul basit yaki yarda ko kadan yayi wani aure,idan yaga na damu sai yace mai nike buta aduniya daya jika,kuma gashi sun bani shi da Hafsat,in yi hakuri ahi ba zai iya aure ba tunda har Hafsat bata iya zama dashi ba,to babu macen da zata iya zama dashi,
Haka kuma idan nace to ya fada min gaskiyar lamarin shi da ita,nasan shi ba mai niman mata ba ne,me ya faru,sai yace shima bai sani ba,amma yaji daɗi da nuna yardar da nayi dashi,Hafsat kuma bai san in da ta samu waɗannan hotuna ba,sai dai yasan komai dadewa gaskiya zata yi halinta ko yana raye ko baya raye,idan ya faɗi hakan na kan kwabe shi da fadin ina zai je ya bar ni,

Wani narar Alhamis da ba zan taba mantawa ba,
Abdul basit ya shigo garin daga Airport zuwa gida aka dauke shi,sannan aka kira mu akan in har muna son ɗan mu dole mu amso wannan Diamond din mu kawo gida,idan kuma muka daka faɗa ma Jami'an tsaro to tabbas zasu kashe shi,

Dan mu yafi mana komai da muka mallaka,dan haka cikin rawar jiki muka je Banki bayan dogon cike cike muka amso sannan muka dawo gida, sai dai kafin mu shiga ciki sai ga kira daga Hafsatkamar ba zan ɗauka ba,sai kuma na dauka,cikin Kuka take shaida min Abbu Safwan yaci amanar mu,tambayar ta na shiga yi akan wani amana ne yaci,na daiji ta ambaci sunan Abdul basit daganan mijina ya karɓe wayar ya kashe tare da faɗin yanzun ba lokacin wannan maganar bane, ,muna shiga falo anan muka same shi daure da saman kujera sun masa jina jina,yayin da fuskokinsu ke sanye a cikin bakin safa,
Mutum shida ne,sannan muryoyin su ba asalin nasu bane sun yi amfani da abin canja murya,
Cikin kuka na isa gare shi ya rungume shi una kuka,ina kuma rokon da su kyale mu ga abinda suke bukata nan,sai dai cikin rashin imani babban su yana karbar akwatin Diamond din a hannun Usman ya harbe shi a tsakiyar goshi,
Wani irin razanannan ƙara na fasa,sai ina ƙoƙarin barin jikin Abdul basit naji ya kira suna na,abu ɗaya ya faɗa min shine Ummi Suraj,kafin ya karasa shima sai saukar harbi naji a jikinshi ta ko'ina,na ruɗe,na rasa wurin waye zan tafi,shi wurin mijina da nake ganin shi kwance acikin jini babu rai,ko kuma wurin dana da yake zaune cikin jini wanda yake zuba kamar an yanka dabba,
Kamar yanda nake kallon idanun Abdul basit dake kallo na a haka har idanun suka lumshe alamun rai yayi halin sa,
Na rasa hankali na domin sai kiran sunan su nake yi,da wannan suka yi amfani wurin ganin sun buga min ƙarfe a ciki a maimakon harbi,a cewarsu ba zasu yi asaran bulet din su ba wurin karasa ni, wannan ma kawai ya ishe ni,nan suka wuce suka barni,ba tare da sun san Allah ya yi ba zan mutu a hannun su ba,sun kashe min miji da dana a gaban ido na,sai dai kuma duk da haka na gane mutum data a cikin su,wanda yake tunanin idan yayi badda kama ba zan iya shaida shi ba,sai dai ina rokon Koto da kafin na faɗi waye wannan ina son ba ma Hafsat dama ta fito ta faɗi abinda ta sani game da wannan lamarin.

Kowa ka gani a cikin koton jikin shi yayi sanyi yayin da dayawa a cikin su hawaye suke yi na tausayin matar,ta ɗayan bangaren kuna idan ka juya zaka ga waɗansu sai sharan zufa suke yi,duk sanyi irin na garin,domin basu taba tsammanin irin wannan ranar zata zo masu da wuri ba,acikin bazata,

babu wani tashin hankali da ya wuce irin wannan kisan a gaban idan ka,har balle a ce mutane masu muhimmanci a gare ka,

Nan daya daga cikin Alkalan yace Hafsat ta fito,
A hankali Ammi ta fito wacce idanun ta sun yi jajir saboda kuka dan tunda Grandma ta fara bada labari take kuka domin tuna irin zama na amana da suka yi da Abdul basit da irin soyayyar da ya nuna mata,ita ce zata masa laifi amma dan kawai a zauna lafiya shi zai bata haƙuri ya haɗa harda lallashi,ko kadan baya son abinda zai taɓa ta,ba zata taɓa yafe ma duk wani mai hannu a cikin kisan shi ba koda waye kuwa,share hawayenta tayi tana tsayawa a kan stage,

"Kamar yanda Ummi ta faɗa kun san komai daya faru har aure na da Abbu Safwan,A lokacin dana kira Ummi a wannan ranar naji wani sirri dan gane dashi wanda ya tashi hankali na har na kasa daurewa na kira ta,
Abinda ya faru kuwa shine na kammala girki rana shi kuma yana dakin shi wanda tunda nake dashi ban taba shiga dakin ba,idan na tambaye shi me a cikin ɗakin n sai yace min ai takardu ne kawai a ciki,ni kuma ban kawo komai a raina ba,
To naje faɗa mashi cewar na kanmala abinci shine na samu tana cikin wannan dakin kuna kofar a buɗe take,dan haka ba tare da tunanin komai ba na kutsa kai,dai-dai lokacin shi kuma yana waya yana faɗin,
Ku kashe Abdul basit din,domin na lura har yanzun hankalin ta na kamshi,karku damu da batun takardun domin nasan ita da ɗanta sun san inda takardun yake,zan ci gaba da lallabasu har su kawo min shi cikin hannu na,
Sai kuma ya kuma cewa ai wannan dalilin ne yasa nake matukar girmamaka Oga,domin cikin ruwan sanyi ka saka ta rabu da mijinta ta hanyar hotunan karya,gashi yanzun ka aura min Jari domin ita din jari ne a gare ni,ai in faɗa maka ko yanzun kasuwa ta tashi dan koli yaci riba,

Jikina na rawa na juya na bar dakin ina kuka shine na fita ta baya cikin tsananin tashin hankali na kira Ummi dan in shaida mata,
Na fara mata magana shine ta kashi wayar na kira na kira kuma ban samu ba,nan na tsugunna ina ta rusar kuka na rashin sanin abin yi,

Daga baya na naji ance"kin gane gaskiya kenan ko?

Cikin firgita na Dago kai ina kallon shi,ba kowa bane face mijin Goggon yara,wato Habib mijin kanwar su,
Na tsorata da ganin shi,saboda babu abinda ke haɗa ni dashi sai gaisuwa,

Cikin kwantar da murya yace ki yarda dani ni nasan komai tun kafin auran ki,ni cikakken dan jarida

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login