Showing 12001 words to 15000 words out of 159134 words

Chapter 5 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt

27 Sep 2025

9743

saba yi,wannan aikin na musamman ne wanda idan har kika samu nasaran cika shi,na maki alƙawarin cikar burin ki a wannan karon,dan haka ke kaɗai zaki tafi,sannan karki dauki kaya ko daya,a airport din matar da zata kawo maki sako zata hado maki da kaya harda wanda zaki canja ki saka,sannan ki yi taka tsantsan Good lock"yana gama fadar haka yawar ya tsinke.

Kallon Ummita tayi wacce tayi shiru tana turo baki,dan taji a binda yace,duk da tasan yawancin aikin su da Biba tana matukar shan wahala wanda ba wata wahala bane daya wuce tsoro,saboda Biba yar kasada ce,tana iya siyar da ranta ta jefasu cikin hatsari dan cikar aikin ta,kuma sai tayi cikin ikon Allah kuma ta samu nasara.

Komawa tayi ta zauna kusa da Ummita,tana tunanin wani aiki ne haka zai turata wanda zai ce karta dauki ko wani kaya,
Ummita ce ta katseta wacce tace"ni kuwa ina na taɓa jin wannan sunan Young USTAZ"jujjuya kai ta shiga yi tana jujjuya sunan a zuciyar ta,ganin ta kasa tunawa ne yasa ta mike,zan fita amma zan dawo kafin lokacin tafiyar taki tayi.

"Uhmm" Kawai ta bata amsa tare da komawa ta kwanta,tana tunanin dole ta yi masa wannan aikin ko don samun cikar burinta ita ma.

duk yanda taso ta samu tayi barci kafin lokacin tafiyar ta tayi bata samu tayi ba har Ummita ta dawo tasame ta,
Tare suka shiga kicin suka yi girkin abinci,sannan suka yi wanke-wanke,
Sai da ta ci abinci kafin tashiga banɗaki tayi wanka,koda ta kammala shiryawa biyar saura,dan haka Ummita ce taja mota taimata rakiya har airport,
Sai dai bata shiga ba,anan bakin kofa suka rungume juna"ki kula da kanki,Allah ya bada sa'a "

"Amin,ke ma ki kula da kanki"

Sake juna suka yi "ta yaya zan iya samun ki a waya"

"Idan na sauka zan siya waya da sim zan nime ki"

Jinjina kai tayi"sai na jiki"

Juyawa tayi tashige ciki,yayinda ita kuma ta juya ta shiga,

Ta san cewa ba tada komai a hannun na tafiya daga ita sai karamin hand bag wanda ake ratayawa,

Ji tayi daga bayanta an taɓa ta,juyowa tayi,sai dai wata mata ce wacce fuskarta ke sanye da nikaf,wani Bag ta damka mata a hannun ta irin na matafiya mai ɗan girma,sai wani envelope fari tare da ta takardun jirginta,
Bata ce mata komai ba ta wuce,ita ma bata ko juya ka kalle matarba ta ta saka kanta gaba,kai tsaye banɗaki cikin Airport din ta shiga,buɗe jakkan kayan tayi domin ta ciro wani kayan ta canja tunda yace in ta iso ta canja kaya,
Sai da ta kammala ciro kayan jakkan kaf kafin ta tsaya tana masu kallo mamaki,wannan wasu irin kaya ne,ko dai matar nan tayi kuskure ne,amma kuma ta saba in dai har zata aiki ita ke kawo mata jakkan kalan kayan daya kamata ta saka a wurin aikin,
Ƙare ma kayan kallo take yi,wasu riga da zani ne kodaddu wanda babu yabo babu fallasa,sai riga da siket wanda bai wuce kala uku ba,suma kuma data ɗaga su wasu manya dasu babu daidai jikinta,suma kuma duk babu sabo,duk da a goge suke,
Kai ina wannan ba kayanta bane,dan haka ba zata saka su ba,idan zaje can ta san dole zai nime ta ko ta yaya ne kafin ta fara aikin,amma ba zata saka waɗannan summokaran ba, danƙa bata canja kayan ba ta dauki jakkan ta fito,
Duk wani abunda ya kamata tayi sai da tayi kafin a basu dama suka shiga jirgi,wanda in da zata zauna a first class ne,

Sai da ta zauna kafin ta dauko wannan Envelope din ta buɗe,paper dake ciki wanda aka naɗe ta ciro tare da buɗe shi,
A hankali ta fara karanta bayanai dake ciki,wanda the more tana karantawa the more ɓacin ranta na ƙara baiyana,
The worst part of it,shine wai a gidan malamai VIP ya tura ta aiki wannan karon,wanda zata tafi a matsayin mai aiki a cikin gidan,
Har da cewa ta saka wannan kayan ta kwantar da hankalin ta ba wanda wani ya saka bane,duka sababbi ne,an zuba masu wani abu ne wanda ya kodar dasu ya maida su tsofaffi,kuma dole sai tayi taka-tsantsan,karta kuskura tayi abinda zai yi exposing dinta,har da wani cewa dole tabar duk wani shaye-shayen da take yi saboda ba karamin gida zata je ba,dole ne ta dauko mashi abinda ya faɗa mata a cikin gidan ta.

Tunda take bata taba jin bacin rai ba akan aikin ta irin na yau,
wai yau ita Biba ce zata wani gida a matsayin ƴar aiki,
A gaskiya da ba dan jirgin su ya tashi ba da ba abinda zai hana ta sauka tace ta fasa wannan aikin,duk da tasan cewa bijirewa VIP ba karamin matsala bane domin shi ɗin mutum ne mai matukar hatsari.

Tafiyar ba wani mai dadewa bane suka sauka a garin Kano,wanda tana fitowa airport din taji an kira sunan ta,

Juyawa tayi sai ganin wata mata tayi fara tas wacce fatarta yaji bilicin ya gaji,sai taunar cingan take yi,
Kai da ganinta kaga yar duniya,

Karasowa matar tayi inda take tare da karɓar jakkanta,
"Biyo ni" Kawai tace mata tana yin gaba,

Bin bayanta tayi har wurin parking in da ta saka jakkan cikin wani adaidaita sannan ta shiga ta zauna,

Ganin haka ne yasa ita ma ta shiga,sannan mutumin ya tayar suka bar wurin,
Sunyi tafiya mai nisa kafin su isa wani unguwa wanda tun daga bakin layin zaka tabbatar da unguwar talakawa ne,ko ta ina ka juya hayaniya kawai kake ji yana tashi na jama'a,
Har kofar wani gida wanda bai da kofa ya, tsaya sannan suka fito,
Kuɗi taga ta ciro ta bashi sannan ta ƙara daukar jakkan suka shiga cikin wannan gidan wanda tunda suka shiga ta fara ganin ƴan mata kala-kala yara da manya wasu kallo daya zaka masu ka fahimce daga kauye suke,

Wani daki suka shiga daga cikin jirin ɗakunan dake cikin gidan,

Wata budurwa ce ta ajiye jakkan gefe ta fita wanda dama suna shigowa cikin gidan ta amsa,

Kare ma dakin kallo tayi cikin yanayi ta ɗan kyankyami domin sam gidan bai kwanta mata ba,ita macce ce mai tsafta da son gayu,dan haka gefe ta samu ta ɗan zauna,

Cire mayafin ta matar tayi tana wurgi dashi,ruwa ta dibo a kofi ta sha sannan ta ajiye ma Biba a gabanta,wanda ganin kofin ruwan kaɗai yasa ta fara jin tashin zuciya,

Zama tayi kusa da ita tana faɗin "wash Allah" Kallo ta tayi "kina jina,ki sake jikin ki domin sai nan da kwana biyu zaki fara aiki a gidan zuwa lokacin mun san dole zasu buƙaci mai aiki"

Bata rai tayi "kina nufin zan zauna a nan har na tsayin kwana biyu?

" Eh domin dole ne akwai wasu abubuwan da zan koya maki,da kuma karin bayani dangane da halin ko wani mutum na cikin gidan har zuwa bangaren da zaki yi aiki"

"Wai a matsayin mai aikin me zanje"

"Shara da wanke-wanke,wata kila harda girki"

Wani irin zaro ido tayi tana dafe kirji"shara! Ni Biba! Wallahi I hate it,na tsane shara, ta ina kuma na iya girki,? Hannu ta Daura a kai "this is the worst ever"

Dariya matar ta fashe dashi......

*waye VIP*
*Menene burin Biba*
*Shin masu karatu wani irin abu ne Biba zata je daukowa a gidan su Young Ustadz*
*wani irin aiki ne koma zata yi a kanshi*
*Shin zata samu nasara a kan matashin malamin namu*
*Zai gane ta kuwa*
*me zai faru a gidan*
*Shin tukunna ma zata amince tayi wannan aikin*
*wacece BIBA*
*Me Asalin ta da labarin ta,me ya fito da ita gida*
*shin zata koma kuwa*🤷‍♀️ ohhuuu,ni ma ban sani ba sai mun haɗe a *Paid Group*



Taku har kullum Jiddarh Umar🦚.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*11*

*Na mai da Littafina mai suna a sama na kuɗi,tare da JAURO,idan kina son daya 300,dari uku,guda biyu kuma da Yar Tsanar Zinari tare da Jauro,dari biyar 500,ko wani daya dari uku*
*Hauwa Umar,Zenith Bank, 2284905309*
*ko katin waya na MTN,tare da turo shedar biya ta 08141644865*

Dariya matar ta fashe dashi,"ai kuwa haka dai zaki daure kiyi tunda kin riga kin zo,batun girki kuma karki damu yanzun akwai takardar girke-girke kala-kala sai a siya maki ki tafi dashi,dan ina ganin haka zai fi sauƙi "

Shiru kawai tayi mata dan gaba ɗaya ranta a jagule yake,ta yaya kamar ita ace wai aikatau zata,kuma a gidan Malamai,ya za'a tasake,dan gaskiya ba zata iya daina shaye-shaye ba,ga wasu kaya kamar na gidan yari wasu manya-manya dasu,
Ajiyar zuciya ta sauke tana karewa dakin kallo,

Matar ce wacce ko sunan ta bata sani ba tace"bari na saka a kawo maki abinci"

Girgiza kai tayi"ki bar shi kawai dan yanzun zan tafi ne"

Kallo mamaki take mata"zuwa ina?

"Hotel zan kama,ranar da zan tafi aiki zan zo,tunda kin ce sai nan da kwana biyu"

Taɓa baki tayi,dama tasan hakan na iya faruwa tun daga ganin farko data mata, "babu matsala,bari na kira mai Adaidaita na ya kai ki"

"Ok "kawai ta ce mata,

Bata wani jima ba sai ga mai Adaidaita ya iso,ita matar ita ta faɗa mashi sunan Hotel ɗin da zai kai Biba,wanda yana kaita tun daga ganin tsarin ginin tace bai mata ba ya canja mata wani,
Aikuwa lafiyayyen Hotel ya kai ta,wanda anan ta sauka kuma taimashi biya mai ƙyau,ta bashi sakon akan ya faɗa ma matar in da ta sauka.

_______Tunda ya dawo daga Wa'azi Abuja kwana biyu kenan bai ƙara fita ba,sai Abbu da ya tafi Jos wa'azi.

Yau tunda ya dawo masallaci sallah Asuba ya zauna a shiyan Kaka inda anan suke karatun safe zuwa ƙarfe bakwai kafin su tashi sannan ayi shirin Boko,

Tunda ya shigo ko wacce ta kama kanta,daga wacce ke turo baki har masu gyangyadi duk natsuwa suka yi,
Samun daya daga cikin kushin din falon yayi ya zauna yana jan carbi,yana kallon yanda Malamin su ke biya wa ko wacce,da kuma yanda suke biyawa,
Sai da lokacin da suke tashi yayi kafin malamin ya masu addu'a,
Ɗaya bayan daya suke gaida shi suna fita,bai amsa ba sai dai ɗan gyada masu kai da yake yi,har suka gama fita,

Daya daga cikin jerin ƴan matan da suka fita su uku ne ta dafe kirji tare da sauke a jiyar zuciya,

Duk kallon ta suka yi"lafiya kuwa Zainab "

Lumshe ido tayi ta buɗe "ke dai bari Sis Bilki wallahi duk sanda naga Yaya Suraj sai naji gabana yana faɗuwa,ban san me yasa ba,amma wallahi bala'in kwarjini yake min"

"Lah Ashe bani kaɗai nake jjn haka ba,sai dai wani lokaci haushe yake bani saboda bai sake mana fuska,kullum fuskar shi a haɗe,in dai ba an nuna shi a TV bane yana wa'azi shi ne wani lokaci zaka ga yana murmushi,amma fa su mama cewa suka yi wai yana da fara'a,ni dai bana gani,kufa?ta faɗa tana kallon su.

" Hadiza kenan,to bari kiji,ko jiya naga yana ma Khalifa wasa yaron Anti Hajo,mune dai ya rai na,insha Allah sai ya haɗu da mata dai-dai dashi,wacce zata zaunar dashi tace yayi ta dariya shi kaɗai "cewar sis Bilki.

Gabaɗayan su dariya suja kwashe dashi kamar wasu sababbin mahaukata,dan maganar Bilki ba karamin dariya ya saka su ba,
" Ba Amin ba Bilki,ke a tunanin ki a kwai maccen da zata iya juya wannan,balle har ta kawo mashi hauka,haka ma baki ji abinda yace ma kaka bane a ranar daya dawo,wai shi har yanzun bai ga maccen data iya motsa zuciyar shi ko da kaɗan bane,kin ga ko akwai matsala,ni dai kam zan so naga Allah ya nuna min wannan yarinyar data motsa zuciyar shi,ta saka shi kuka ace,sai mu ga Young Ustadz yana rokon asoshi,"

Nan ma wata Uwar dariyar suka fashi dashi Zainab harda faduwa sabar dariya,
Daga bayan su suka ji ance "idan kun gama gulmar sai ku bani hanya in wuce"

Da sauri suka zabura tare da juyawa suna kallon ta suna matsa mata,

Ganin zata wuce ne yasa da sauri duk suka riƙo mata hannu "Aunty Maijidda baki dai ji me muka faɗi ba ko?

Kallon su tayi daya bayan daya yanda duk suka riƙe ta tare da Zuba mata ido suna jiran su ji me zata ce,
" Naji mana?

"Me kika ji?Hadiza ta tambaya.

" Komai da komai,ina nufin tun daga farko har in da kuka tsaya,yanzun ku sake ni bari naje na sanar dashi domin ya fara Addu'ar niman tsari a kanku"

Ƙara cakume ta suka yi suka shiga roƙon ta akan ta rufa masu asiri ba zasu sake ba,

"Ok,ok naji ku sake ni,amma duk sanda na karajin kun ma Suraj irin wannan addu'ar ni da kaina zan faɗa mashi"

"Insha Allah ba za mu sake ba"

"To ku sake ni mana na wuce"
Duk sake ta suka yi ta wuce tana girgiza kai,tana jinjina zancen yaran a zuciyar ta,domin gata nan zaune a gida har yanzun ta kasa aure tana zaman jiran shi amma shi ko kallon ta bayayi,kuma kowa a gidan ya sani,
Shi kuma yi yake kamar bai san da halittar ta ba acikin gidan,dan haka bata fatan ma a samu macen da har zata motsa masa zuciya,dan a wannan lokacin bata san wani irin hali zata shiga ba,ko kuma me zata iya aikatawaaikatawa ba.

Tashi yayi ya shiga cikin ɗakin kaka in da take zaune tana jan carbi,zama yayi kusa da ita ya na tankwashe kafa"barka da safiya tsohuwa"

Saida takai karshe sannan ta ajiye carbin "Surajo da fatan ka tashi lafiya?

" Alhamdulillah"

"Allah ya maka Albarka, ya nuna min auren ka"

"Amin tsohuwa"

Hararanshi tayi"sai kace yana da niyar yi"

Ɗan murmushi yayi "ina da niya mana Tsohuwa," Mikewa yayi Abbu yasa ni aikin duba masa wani littafi bari naje,"

"In ajiye maka abin kari"

"No A'a dan zan fita ne kuma ba zan dawo da wuri ba"

"Allah ya tsare,amma ka tabbar ka karya da wuri dai"

Murmushi kawai yayi ya fita.

Dakin shi ya buɗe ya shiga ajiye carbin hannun shi yayi a inda yake rataye sharbi,
Dakin da yake ajiye littatafai ne ya shiga sannan ya fara dudduba littafin,sai dai baya wurin,dirowoyin dakin ya fara jawowa yana dubawa nan ma baya ciki,
Tsayawa yayi yana tunanin to ina ya ajiye littafin,
Fitowa falo yayi ya jawo wani karamin durowar dake gefen kushin,
Tsayawa yayi yana kallon abunda ke ciki wanda shi yana manta dashi,
Hannu yasa ya dauko pos din harda wayar,

Samun kanshi yayi da zama kan hannun kushin din,haka kawai zuciyar shi ke raya mashi ya kunna wayar,
Dubawa yayi yaga wurin kunnawa sannan ya kunna,
Kafin ya kawo ne ya buɗe pos ɗin,wanda ATM card dinta ne da aka rubuta Habiba Abdulmajid,sai master card,da kuɗi a ciki yan dubu daya daya,wanda bai damu daya kirga ko nawa bane, wani karamin kwali ya gani ɗan madaidaici,ciro kwalin yayi wanda yana buɗewa sai ganin karan Sigari yayi a ciki,wato Taba,ya jima yana jujjuyawa tare da tunanin yanzun mace ce ke shan wannan abin,tunda dai gashi a jakkanta ya gani,kafin ya maida komai a cikin jakkan ya rufe,

Duba wayar yayi babu wani key da aka saka mata,wurin App ya fara dubawa wanda babu wani App a wurin sai irin wanda waya ke zuwa dashi,sai kuma WhatsApp da Facebook, ko TikTok babu a wayar,
Komawa baya yayi ya shiga wurin hotuna,

To ni dai bansan me yake gani a wurin ba ko kallo sai dai ji da nayi yana sauke numfashi akai-akai,sai kuma naga da sauri ya fita wurin yana kashe wayar gaba daya tare da mai su in da ya dauko,
Mikewa yayi ya buɗe firig tare da daukar goran ruwa mara sanyi sosai yashi,
Kafin ma ya ajiye goran hannun shine yaji wayar shi na vibration a Aljihu,
Yana dubawa ne yaga sunan kanwarshi,ɗauka yayi wanda kafinma yakai ga yin sallamah yaji kukanta da ihunta,
Cikin sauri yashiga tambayarta lafiya,meke faruwa,

"Yaya, Suraj dan Allah kazo part ɗinmu da sauri Ammi ta zame ta faɗi,kuma ta kasa tashi"

Bai ma gama sauraron abinda take fadaba tunda yaji tace Ammi ta faɗi ya fita cikin sauri wanda har yana dan haɗawa da sassarfa ya nufi part ɗinsu.

Koda ya shiga falon yaga basu ciki,har zai haura sama yaji kamar kuka a kicin,dan haka can ya nufa,
Ta samu ta mike da kyar hannun ta na cikin na Amira sai dai ta kasa ajiye kafar a ƙasa sai cije baki take yi,
Da sauri a karasa in da suke yana rikota "Subhanallah,Ammi sannu,ba ki dai ji ciyo ba?

Cije baki tayi" Suraj kafa ta,zafi yake min bana iya ajiye ta "
Tsugunnawa tayi ya duba kafar wanda yake na hagu ne,Babban yatsar kafar yayi ja har ya fara kumbura,

Yana mikewa kawai sai ji Ammi tayi ya dauke ta kamar wata yarinya yana tafiya da ita,
"Suraj sauke ni,so kake ka kada ni "

Bai kulata ba sai da ya fito da ita falo ya zaunar da ita kan kushin,sannan yace"Ammi bari na kira me kyaran kafa dan kamar kin samu targade ne"

Kyara zama tayi tana jinjina mai kai"amma kar ka sanar da Abbu ku dan hankalin shi na iya tashi"

"Insha Allah"ya faɗa yana zaro wayar shi a Aljihu.

Wata number ya kira wanda bai jima yana ƙara ba aka ɗauka,sallamah kawai yayi yace" Idan ba damuwa ina buƙatar ganin ka a gida yanzun,"ban ji me aka ce mashi ba sai ajiye wayar da naga yayi ya koma wurin Ammi yana mata sannu,

Kallon Amira yayi wacce ke hawaye"me ya faru a kicin ɗin?

Share hawayen idon ta tayi "Yaya man gyaɗa ta taka shine ta zame"

Cikin mamaki yace"man gyaɗa kuma,garin ya man gyaɗa ya zube har ta zame,ko dai gangancinki ne"

"Wallahi yaya ban san yanda aka yi ba,amma ko jiya da muka gama girkin dare sai da na share kicin dinnan sannan na goge ko ina nayi wanke-wanke,ni bansan ta in da man gyaɗa ya fito ba har ya zuba a ƙasa,tunda ba a kicin muke ajiye kayan abinci ba"

Shiru yayi yana ɗan nazari,ganin bai fahimce ko mai bane yasa yace"is ok, kukan ya isa haka "

Jin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login