Showing 21001 words to 24000 words out of 159134 words

Chapter 8 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt

27 Sep 2025

9736

ta na Camera ya zama gaskiya,

Kicin ta shiga ta dauko abin cire yanar gizo-gizo tare da dogon kujera,
Hawa tayi tana yi kamar mai cire kura amma kuma dubawa take yi,
A haka ta gama zagaye lungu da sako na shiyan sai dai ko alamun camera babu,
Ɗauko kujerar tare da sandar tayi ta shigo falon tana tsaki,"kai jama'a a duniya ba kada maƙiyi daya wuce zuciyarka,"

Jin muryar Ammi na kiranta ne yasa da sauri ta juyo tana amsawa,

"Je ki Ɓangaren Goggon su ki kira min Amira,ta zo ta tayani gyara dakin Abbu kafin ya iso dan yana hanya,ki ce tayi sauri"

"To Mam"
Fita tayi tana bin ta inda Nafisa ta nuna mata nan ne ɓangaren goggon su a dazu,
Tana isowa ɗan hanyar da ya raba shiyan Goggon da hanyar shiga shiyan Samarin gida ta kusa cin karo da Nurudeen,
Da sauri ta matsa baya tana rabewa gefe dan bashi damar wucewa,"Sorry ban kula da kai ba"

Murmushi yayi "koda ma kin bige ni kin bi ta kaina ai babu damuwa domin kin isa kiyi"

Ita sai bata bashi amsa ba,

Ba zato sai ganin shi tayi a gabanta yana daf da ita wanda har suna iya juyo numfashin juna,
Riƙo hannun ta yayi yana juyawa cikin wani irin salo irin na mazaje waɗanda suka kware wurin yaudarar zuciyar ƴan mata"Ya hannun naki Bib,da fatan ya dai na maki zafi"

Kafin ta buɗe baki ta bashi amsa ne suka ji taku a bayan su,
Shi dai bai juya ba,amma ita da sauri ta juya,sai dai ganin mai wutowa ne yasa ta dauke numfashi tana Freezing domin ba karamin bugawa zuciyar ta tayi ba,

Ko kallon in da suke bai yi ba,saima raɓawa ta gefen su da yayi ya wuce abun shi,
Da ido ta bi shi har ya ɓace ma ganin ta,
Ji tayi ya shafa fuskarta,"karki damu da wannan dutsen,shi bashida wata sha'awa a rayuwar shi,kar ki ji tsoro domin ba mu bane a gaban shi"

Cikin sauri ta ture shi baya tana matsawa sannan ta juya cikin sauri ta bar wurin,
Tana jin gabaɗaya zuciyar ta a jagule,
Tura kofar falon tayi tare da yin sallamah,wanda bai fito sosai ba,
Jin shiru ne yasa ta shiga cikin falon inda ta tarad wasu yan mata su Uku zaune sai hira suke cikin kwanciyar hankali ga kayan ciye-ciye a gaban su,
"Sannun ku,,Amira Ammi na kira"ta faɗa tana juyawa ba tare da ta jira jin amsar su ba,

Har ta kusa barin falon taji an daka mata tsawa tare da cewa" Ke jakar ina ce da zaki shigo mana falo babu sallamah,babu gaisuwa kawai sai ki faɗi abinda ke bakinki ki wuce kamar wata Tunkiya "

Cikin mamaki ta kalle yarinya da ke fadar wannan mummunan kalami a kanta wacce bata wuce tsaranta ba, wato Zainab,dama haka take da fadin Rai,

Nuna kanta tayi da hannun ta"da ni kike"dan ta juya gefe da gefe bata ga kowa ba,

Takowa tayi gaban ta "in ba dake ba da wa zanyi,wai me yasa ku ƴan aikin nan kuncika raina mutane ne,ko dan kunga ana sake maku"

Hadiza dake zaune ne tace "baƙi ga irin kallon da take maki ba"

Amira ce ta tafi "ku kuma da kanunan magana...

Kafin ta ƙarasa ne suka ji muryar goggo na fadin " Meke faruwa "tana karasowa inda suke.

Cikin shagwaba Zainab tace " Goggo wannan mai aikin ne muna zaune kawai sai shigowa tayi babu sallamah,sai ce mana tayi sannun ku,kamar taganmu a gadon asibiti "

"Ni dai matsamin ki ga in wuce" Cewar Amira"goggo na tafi Ammi na kira na"

Hannu kawai ta daga mata,
Kallon Biba take daga sama har katsa"ya sunan ki,awani bangare kike aiki,nawa ake biyanki "

Kallon matar tayi ido cikin ido babu alamun tsoro ko dar a tare da ita"suna na Biba,ina aiki ne a ma Ammin Amira"

"Waɗanda kike ma aiki basu faɗa maki matsayina dana ƴaƴana bane a wannan gidan?

" Ba'a faɗa min ba"
Saukan wani lafiyayyen mari taji a lafiyayyen fatar fuskarta mai taushi wanda nan take shaidan yasunta biyar suka fito kwance a fuskar ta,
Nuna ta tayi "amma daga dukkan alamu baki samu tarbiyya daga wurin iyayenki ba,to ki sani idan har bikida tarbiyya ni nan zan tarbiyantar dake, wawuya,jahila,dakikiya kawai,fitar min a shiya,karna kara ganin kafarki a shiyana"

Idanun ta sunyi jawur na azaban Marin da tasha wanda tunda take a ba a taɓa Marin ta ba sai yau,
Bata son ko kaɗan ta nuna gazawarta ta hanyar zubar da hawaye,shi yasa ta juya kawai zata fita,

Dakatar da ita tayi "ke,zo ki basu haƙuri"

Juyowa tayi,ta kalle yaran da ake cewa tana ma haƙuri,girgiza kai tayi ta kalli goggo "Never" Ta fadin haka ta bar falon,
Juyawa tayi ta kalli ko ina,nima take ta samu inda zai fi mata sirri domin amayar da abinda ta hadiya,
Ta gefen ɗakunan samari ta samu dakali ta zauna,

Hawaye ne ya fara zuba a hankali a hankali,kafin kuma ta rufe bakinta tana fashewa da kuka mai taba zuciya tana gunji,wanda da kaji yanda sautin kukan ke fita kasan cewa wanda ke yinshi tabbas kuka ne na kadaici da kuma tuno wani abu mai ciyo a rayuwarka irin wanda ka kasa mantawa dashi,
Babu abinda ya mata ciyo irin kiranta da jaka, tunkiya,da wannan yarinyar tayi, sai mamarta data kira ta da Jahila,kalmar mara tarbiyya bai mata ciyo ba,domin ta san tun daga lokacin data saka kafa tabar gida,tun daga lokacin ta fita a jerin masu tarbiyya,

Duk gatan da suke takama suna samu,to wallahi bai yi koda rabin gatan da take dashi ba,ilimin da suke takama suna dashi na Boko idan suka ji a inda tayi karatu da abinda ta karanta sai kusa haɗiye zuciyar su da mamaki,haka kuma ilimin Addini,sai dai kawai ta ajiye su a gefe ne kawai domin basu da amfani a gare ta,domin tayi Alkawarin duk abu abu wanda ta sanadin iyayenta ta same shi to ta ajiyeshi har abada,ko da menene.
Domin koma yaya ne su suka hallakar da rayuwar ta,kai,bama tason ta tuna komai dangane dasu har a badas
Ta sanadin su gashi waɗanda basu kai matsayinta ba suna wulantata,

Tayi kuka sosai wanda sai da fatan idon ta ya kumbura,idanunta sukayi jawur,
Ta kwashe kusan mintuna talatin kafin ta fito wurin dan komawa shayansu,

Tana fitowa shi kuma yana jawo kofar dakin shi ya wuce,wanda daga dukkan alamu cikin sauri yake,
Taga lokacin da yake kokarin saka katin buɗe ƙofar shi a aljihu,sai da cikin rashin sani katin ya faɗi, shi kuma bai lura ba ya wuce,

Ganin ya wuce ne yasa da sauri ta karasa ta dauki katin tana jujjuya shi,
Wani irin murmushi ne ya subuce mata wanda nan take ta manta duk wani damuwa daya shiga zuciyar ta a shin mintunan nan,
Rungume katin tayi a kirjin ta,tana murmushi,sai kuma ta ciro ta kai baki ta sumbata,tare da lumshe ido jin ta shaki wani ni'imtaccen kanshi "mugu,kai Allah na gode maka,ko na komai in dai na samu na dauko na ɗakin shi a dakin Abbu bazai min wuyan samu ba" Karrama rungume katin tayi wanda tana zuwa ta saka a na'urar,nan take kuwa kofar ta buɗe,
Cikin sauri ta shiga ta maida ƙofar ta kulle,
"Wow" Ta faɗa tana kallon tsarin falon yanda yake a tsaftace,ko ina sai kamshi yake tashi,
Ta jima tana kalle_kalle a dakin kafin ta shiga aikin take mashi kaya,wanda tundaga falon har zuwa ɗakin barcin shi bata ga komai ba,
Wani fitowa data jawo a dakin barcin shi,babu komai aciki face damin kuɗi wanda a kalla taga na Country biyar a ciki,harda daloli,
Maida durowar tayi ta kulle ba tare data ko taba ba,
Cikin mintunan da basu wuce goma sha-biyar ba ta gama hargitsi komai na dakin harta zanin gado a wurge yake a kasa amma bata ga koda alamar abinda take nima ba,
Ji tayi ranta ya baci,so take ta ƙara dubawa,sai dai kuma ta riga taja lokaci,
Dan haka ta yanke shawarar ta fita kawai wata rana zata ƙara samun dama,
Kar ya zo ya Kamata,

Kallon dakin tayi yanda gabaɗaya ta fitar dashi kamannin shi,
Girgiza kai tayi,data tsaya kyara mashi dakin ya kamata,Gara ta gudu ai ba zai san ko waye ba.

Da wannan shawaran tayi amfani ta doshi kofa domin fita,sai dai tana saka kati kofar ya shiga key ya kulle bam,
Ƙara kwada sawa tayi bayan ta juya katin ko bata saka dai_dai bane,
Sai dai ga mamaki ta duk yanda tayi domin kofar nan ta buɗe taki buɗewa sai ma nuna mata key da yake yi,
Tun tana yi da wasa har ta fara tsorata ta hau jan ƙofar tana tura shi iya karfinta ko zai buɗe,
Sai dai ina kofa ko motsi bai yi ba,
Tsoron ta daya,yanzun idan ya kamata me zata ce mashi ta zo yi dakin shi,ƙila ma asirin ta ya tonu,
Wasa_wasa tana cikin wannan halin har awa daya ya shige,har gashi na biyu na ƙoƙarin shudewa,
Ga uwar yunwa da ke addabar ta kamar hanjin cikinta zai tsinke,
Nan lamarin ya wuce tunanin ta ne yasa kawai ta zauna nan bakin kofar tana fashewa da kukan nadamar shigowa dakin tare da kife kanta a jikin ƙofar tana rusa kuka............
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*16*

*Na mai da Littafina mai suna a sama na kuɗi,tare da JAURO,idan kina son daya 300,dari uku,guda biyu kuma da Yar Tsanar Zinari tare da Jauro,dari biyar 500,ko wani daya dari uku*
*Hauwa Umar,Zenith Bank, 2284905309*
*ko katin waya na MTN,tare da turo shedar biya ta 08141644865*


Tun tana yi da ɗan ƙarfi har ta koma yi a hankali daga nan barcin wahala ya ɗauke ta wanda bata masan iya adadin lokacin data ɗauka ba,

_____koda suka je suka dauko Abbu a filin jirgi zuwa gida,ya daɗe a shiyan Amme suna hira,har Abbu yayi wanka suka ci abinci tare,sai wuraren ƙarfe daya sannan ya fito ya nufi bangaren su,yana jin Ammi na aiken Amira akan taje ta dubo mata Biba tun dazu bata ganta ba,Abinci ma sai tare da ita Amiran suka lalaba suka yi tunda ba makaranta,

Ganin ya laluba aljihunshi bai ji katin buɗe ƙofar shi bane yasa kawai ya saka numbobi ya buɗe ƙofar dashi,

Yana tura ƙofar yaga ya buɗe kaɗan sannan kamar a kwai abu mai dan nauyi daya tare kofar wanda ya hana shi buɗewa yanda ya kamata,
Yana sako kafar shi bayan taku biyu,yaji kafar shi ya sauka a kan abu mai laushi,
Da sauri ya daga kafar yana matsawa baya a tsorace dan Allah yasa bai gama sauke kafar shi ba,duk a tunanin shin ajikin mage ya saka kafar shi,shi yasa yaja baya yana kiran sunan Allah,dan ba karamin tsoron mage yake ba.

Tsayawa yayi cikin tsananin mamakin ganin ta a wurin yana kallon ta,ya kuma kalli kofar,ta yaya ta shigo ne,ta ina,

A hankali ya saka kafa ya tsallake ta,
Jin yanda ta sauke wani ajiyar zuciya mai ƙarfi irin wanda ke nuna mutum yana cikin kuka barci ya dauke shi irin shi tayi,

Hakan ne yasa ya juyo ya kalle ta ba tare da yayi niya ba,
Idon shine wannan karon ya sauka akan fuskar ta,wanda yasha mari,ganin kamar shaidar hannu a fuskar ne yasa a hankali ya kara taku ɗaya daga inda yake zuwa gare ta,
Tsura ma fuskar ido yayi,tabbas shaidar mari ne wanda ga alamun kwanciyar yatsu biyar nan a faran fatan fuskar ta,sai kuma idanunta da suka kumbura,

Dauke idon shi a kanta yayi wanda nan take kuma suka kara sauka akan yanda falon ya canja kamanni ba kamar yanda ya fita ya bar shi ba,
kalle ta yayi ya kalli falon kafin ya shige dakin shi,in da ya iske nan ma haka ɗin ne,
Dafe ƙwanƙwaso yayi yana nazarin ɗakin kafin ya fara tattara duk wani abunda aka cire daga muhallin shi yana mai dawa daidai,ganin lokacin sallah Azahar ya gabato ne yasa yashiga bayi yayi wanka,dan daga masallacin yana son ya fita ne.

Daga inda take kwance kamar wacce aka tunatar da inda take haka ta Mike a firgice,ba tare data tsaya gama wastsakewa ba ta tura ƙofar dan ganin ko zai buɗe,sai dai cikin tsananin sa'ar ta sai gashi kofar ya buɗe,
Ai bata jira komai ba yanda kasan wacce aka kora haka ta tashi ta fita da gudu tana sauke ajiyar zuciya,

Ba tare data Ankara ba kawai sai ji tayi taci karo da mutum,tana kokarin faɗuwa shi kuma ya torota yana maida ita tsaye a kan ƙafafun ta,

A hankali taji muryar shi yace "ki dinga kula,ki daina guda ɗan bashi da amfani"ya fada yana kare mata kallo,dan gaba ɗaya a hargitse take,gashi ko ɗankwali babu a kanta,ga ido a kumbure,

Kallon shi kawai tayi ta saka kai tana yin gaba,dan yanzun bata shi take ba,duk da ta gane shi,wato Shamsuddeen ne.

Binta yayi da kallon mamaki,kafin ya kalli ƙofar dayaga ta fito,

Baya son zuciyar shi ta raya mashi wani abu,amma kunsan yanda zuciya take,har ya kai bakin kofar dakin shi,ya juya yayi kofar dakin Suraj,
Yana tura ƙofar yaji ya buɗe,dan haka shiga yayi,
Tsayawa yayi yana karema falon kallo kafin idon shi ya sauka a kan ɗan kwalinta dake yashe ata bakin kofar,
Shiru yayi ya zuba ma ɗan kwalin ido,
Sai kuma yaji yana son ya shiga cikin dakin,

A hankali yake takawa har ya isa bakin ƙofar ɗakin,
Kiran sunan shi yayi"Suraj "

Daga inda yake zaune a gaban karamin miro yana shafa mai ya amsa yana juyowa,
Shi kuma jin an amsa ne yasa ba tare daya jira komai ba ya shigo cikin dakin,
Sai kuma naga ya tsaya turus kamar wanda yaga wani abu,
Kallon Suraj ɗin yayi wanda yake ɗaure da Tawul iya kugu,jikin shi ba riga daga dukkan alamu kuma daga wanka ya fito,
Sai kuma ya kalli kan gado wanda yake a hargitse zanin gadon ya tattare ya koma gefe ɗaya,ga filalla duk sun yi gefe,dan daya gama gyara dakin ya rage saura gado,sai kawai ya wurga filallan a kan gadon kafin yaje ya dawo ba.

Ganin yanda yake ƙare ma dakin kallo ne yasa yace"Bismillah zauna,bari na saka kaya"

da sauri ya jirgiza kai"A'a ba zama zanyi ba,dama naga kofar ka a buɗe ne shi yasa na leko naga ko kana ciki"

"Ina ciki"

Juyawa yayi"to bari na tafi"har ya juya sai kuma ya juyo ya kalle shi "amma kuma" Ko tunanin ne yayi oho sai cewa yayi kuma"ba komai barshi "ya faɗa ganin yana kallon shi,ya juya ya fita yana mamakin wannan kuma wani irin sabon lamari ne yake shirin faruwa dasu kuma acikin wannan gidan kuma da wanda ba'a taba tunani ba,
Dole ya faɗa ma Kaka,ko kuma ya sanar da Abbu kafin abun yayi tsanani.....




*in Allah ya kaimu zanci gaba*
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*17*

*Na mai da Littafina mai suna a sama na kuɗi,tare da JAURO,idan kina son daya 300,dari uku,guda biyu kuma da Yar Tsanar Zinari tare da Jauro,dari biyar 500,ko wani daya dari uku*
*Hauwa Umar,Zenith Bank, 2284905309*
*ko katin waya na MTN,tare da turo shedar biya ta 08141644865*


Allah ya taimake ta koda ta shiga cikin falon babu kowa,cikin sauri ta shige ɗakin ta tana sauke ajiyar zuciya,ko ba komai ta godema Allah da dakin ya buɗe ba tare da mai dakin ya dawo ba,
Banɗaki ta shiga tayi wanka sannan ta canja kaya ta fito falo,zuwa lokacin an dan jima da idar da sallar,
Tana fitowa anan ta iske Ammi zaune tare da Shamsuddeen sai shi uban gaiyar wanda yake rike da carbi yana ja,shi kuma Shamsuddeen Amira na zuba masa abinci a plate suna dan hira da Ammi,

Tana zuwa tsugunnawa tayi a gabansu "Mam barka da Juma'a"sannan ta kalle su cikin dukar dakai tace" Barkan ku da Juma'a "

Dago kai Shamsuddeen yayi yana kallon ta,

"Yauwa barkarmu da rana mai falala,sai dai kuma ina kika je ne Babi tun dazu na aika cigiyar ki a cikin gidan nan sai dai ace ba'a ganki ba,ina kika je?

Wannan karon ba Shamsuddeen ba har ta shi kanshi da idon shi ke lumshe yana jan carbi sai da ya dakata na ɗan wasu lokutan dan jin ne zata ce,yayin da shi kuma Shamsuddeen ɗin yake satar kallon dukkan su,

Ba tare da dar ba tace"Mam kiyi haƙuri a lokacin da kika aikeni kiran Amira ne bayan na kirata ina hanyar shigowa saiga kiran Uwar ɗakina akan Mamata ba tada lafiya daga ƙauyen mu har an shigo da ita cikin gari yanzun haka tana Asibitin Koyarwa na Aminu Kano,
Mam kiyi haƙuri hankalina ne ya tashi shi yasa na tafi ba tare da izinin ki ba"ta faɗa tana share guntun hawayen daya zuba a idonta,

Idonun shi dasu rufe bai masan yanda akayi suka buɗe ba tsabar mamakin irin karyar da wannan ƴar yarinyar ta haɗa a lokaci ƙanƙani,sai tsintar idanun shi yayi a kanta,

Yayin data gefe ɗaya kuma Shamsuddeen ya kusa kamewa a zaune yana tunanin kodai ta manta dazun ya ganta tana fitowa ɗakin ƙanin shi.

"Subhanallah,ai ban sani ba dana hada ki da wani kuje tare,yi hakuri bar kuka,insha Allah mamarki zata samu lafiya da yardar Allah,
Yanzun ya jikin nata?

Jan majina tayi cikin muryar ban tausayi tace" Da sauƙi"
"Meke damunta ne har haka"

"Likita yace hawan jini ne ke damun ta"

"To ba komai kar ki damu,zuwa anjima Shamsuddeen in baka komai sai ka kai ta ku dubo Mamar nata"

Da sauri

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login