Showing 63001 words to 66000 words out of 159134 words

Chapter 22 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt

27 Sep 2025

9744

kawai manta sunan garin nayi,yauwa bayan Kakan shi babu wasu yan uwa dake zuwa nan din a wancan lokacin?

"Eh kawun shi ne ko waye,kamar dai kanin Kakar shi ne naji yace a wancan lokacin shine yazo sau daya,kuma bai ƙara zuwa ba?

Da sauri ta mike tana turo mashi akwatin gaban shi," Ka dauki akwatin duka,duk abinda bai maka ba ka zubar"ta faɗa tana barin wurin,

Tsabar daɗi har da rawar murna sai da yayi,

Tana shiga daki da sauri ta jawo durowa ta falli takarda ta dauki Biro,
Rubutu ta fara kamar haka,
Kakan shi,sai kuma sata,alamar tambaya ta saka a wurin,to me aka sata,wani irin abu ne haka,sannan su waye suka aikata satan,

Shiru tayi ta shiga dogon nazari,to ita yanzun wannan takardar da aka ce ta dauko me amfanin shi,tabbas takardar ba gida bane,ko kamfani,takarda ne,wani irin buɗe ido tayi kafin a fili ta furta"ba dai yana da Alaka da wancan satan ba"girgiza kai tayi"inaa hakan ba zai yu ba,"har gitsa suman kanta tayi"Ya Allah me yake faruwa ne,shin wani irin aiki nake yi,wa kuma nake ma aiki,"sai dai fa idan har zargin ta zai iya kasancewa gaskita takardar nada Alaƙa da wancan aikin to shi kuma VIP kenan koma waye shi yana da masaniya a kan komai,
Ajiyar zuciya ta sauke,kai hakan ba zai taba yuwa ba,ai shi wancan aikin ma shekara goma sha daya,kenan da suka yi fashin,
Ita kuma wannan aikin nata data fara har auren bai wuce wata biyu,dan haka ba yanda za'a yi hakan ya faru,
Sai dai koma waye VIP sai ta binciko shi duk inda yake a duniya,haka koma menene waɗannan takardun suma sai ta bincikosu domin ta nan ne kawai zata iya samun duk wani amsoshin da take buƙata,kuma shine makamin duk wani yaƙi da zata gabza har ya kai ta ga duk wanda take son gani,
Sai dai babban matsalar shine ta yaya zata iya yin haka,ta ina zata samu wannan takardar.
Jin karan da wayar ta keyi ne ya dawo da ita daga dan gajeren nazarin da take yi,
Ganin me kira ne yasa gaban ta faɗuwa,dan cikin sauri ta ɗauki wayar tana karawa a kunnen ta,
"Me kika samu" Abu na farko da aka fara faɗa kenan daga ɗayan ɓangaren,

"Ina Ummita?

" Me kika samu? Ya kara maimaitawa,

Ta lura idan ba har ta bashi amsar tambayar shi bane ba zai taba amsata ba, "har yanzun ina kan bincikawa,amma ban samu komai ba har yanzun,sai dai ina ganin kamar waɗannan takardun basa cikin wannan gidan"

Tsaki taji an ja"to me nufinki a tunanin ki,shi din ya fiki wayau nisa ba kusa ba,sai dai ina da tabbacin duk wayau shi yana da lago,shi zaki nimo ki yi amfani dashi har ya kai ga faɗa maki in da suke,domin shi kaɗai yasan in da suke"

"Ta yaya zan yi haka?

" Ke matar shi ce kin fini sanin haka,na baki nan da kwana biyu,idan banji labari mai daɗi ba kome ya biyo baya sai ki yi maraba dashi,domin nima banda isasshen lokacin"

"Ummita fa?

" Nan da kwana biyu zaki ganta"

Kafin tace wani abu har ya katse kiran,to me yake nufi da nan da kwana biyu zata ganta,
Ita kan ta shiga uku,kwana biyu kam ya mata kaɗan ta ina zata fara,
Mikewa tayi ta nufin dakin shi,gara ta fara binciken dakin ko zata samu wani abu,
Tama yi tunanin zata ga dakin a rufe,sai dai a buɗe yake dan haka shiga tayi ta fara duba duk wani lungu da sako na dakin wanda tayi kusan awa biyu ba tare da taji ta gaji ba,har addu'a take akan Allah yasa ta samu wani abun,sai dai kamar yanda ta hargitsa dakin haka ta kyara dan ba abinda ta samu ko me kankantarsa,
Fitowa tayi ta jawo mashi kofa ta zauna nan bakin ƙofa,gabaɗaya ta rasa meke mata daɗi,ta rasa wani kalan tunani zata yi,a haka dai ta ƙarar da wannan ranar batare da yanke me ta kamata tayi ba,

Washegari da safe,ƙarfe goma wayar dakin ya shiga ƙara babu kakkautawa,
Cikin gigin bacci ta dauka tana karawa a kunne,
Muryar Bala taji yana fadin"Hajiya ki sauko kin yi baƙi "

"Ohh Bala barci fa nake yi"

"Ki yi hakuri ki sauko domin yan uwan Ubangida na ne suka zo,kamar ma harda iyaye"

Kashe wayar tayi tana jan tsaki, sannan ta shiga banɗaki tayi wanka cikin gaggawa ta saka doguwar riga na Atamfa wanda yaji aiki,

Tunda take saukowa daga saman bene suka kureta da ido,yayin da kamshin turaren ta ke sanar dasu isowar ta gare su,

Cikin jirmamawa ta shiga gaida su,duk da wasu sun amsa wasu basu amsa ba,
Ganin an kawo masu ruwa da abun motsa baki ne yasa ta zauna ita ma a daya daga cikin kujerun falon,

"Sannun isassah,muna saman kushin kina sama babu ko ɗan girmamawa"cewar Hajiya Rahama,

Hararan gefe tayi" Momy ai yanzun kin san level ya ƙaru "

Duk buɗe baki suka yi suna kallon ta"ah lallai level ya karu,baƙauye ya karo wulaƙanci "

"Sosai ma kuwa Goggo tunda gashi Baƙauyen ne ya samu nasarar shiga gidan sarki"

Duk sun gane inda ta dosa,dan haka mikewa suka yi "zamu tafi ina Suraj,ko shi yafi ƙarfin fitowa ya gaishe mu"

"Barci yake yi domin jiya da daddare yayi aiki ya gaji,bamu yi bacci da wuri ba"

Daya bayan daya suka fita suka bar falon ba tare da sun kuma ce mata komai ba,lallai ashe ita din Kura ce mai lulluɓe da fatan Akuya,jiya sun ga Video da aka mata a wurin wa'azi,shine kaka ta haɗa su taimasu faɗa akan ba su je sun dubo Suraj din da matar shi ba,amma ji amma da yar iska ta faɗa masu,

Ita kuma suna fita taja ƙaramin tsaki,domin ita wallahi ko kaɗan bata su take yi ba,
Wani tunani ne ya faɗo mata dan haka cikin sauri ta tashi ta shige daki,durowa ta buɗe ta shiga duba Asalin Jakkan kayanta ta dauko ta zazzage,
Wannan wasiƙar data taɓa satowa a ɗakin shi ta dauko,
Jikinta har rawa yake yi wurin lalubar number shi,kira biyu ya ɗauka ba tare da yace komai ba,

"Na samu wani abun" Ta faɗa da kwarin gwiwa,

"Ina jinki"

"Wasika ce dana samu a dakin shi,"

"Akan inda takardar yake ne?

" A'a sai da an ruba *Hadarin dake sararin samaniya yayi baƙi kirin,kuma daf yake da saukar da baƙin ruwa mai mugun dafi, da fatan za'a shirya ma ƙwaryar taran shi* abinda ke cikin wasikar dana samu kenan,

Dariya taji ya sheke dashi kafin yace"ai kuwa ruwan ma yafara sauka sai dai bansan ko da wani irin ƙwarya zai iya taran shi ba"

"Me kake nufi"

"Koma me nike nufi daga nan zuwa gobe zaki ji"

"To Ummita fa"ji tayi ya kashe wayar dif yayin da take jin sautin dariyar shi a ranta,haka kawai kuma sai taji gabanta na faduwa kafin wani irin tsoro ya shige ta," Me yake nufi?me zai faru a gobe?ita fa ta lura kamar daga jiya zuwa yau ta rame tsabar fargaba,ƙoƙari tayi ta cire abun arai,sai dai duk yanda tayi ta kasa sai ka ƙara shiga fargaba da take yi,

Ganin ta kasa jurewa ne ya ta fito daga falon tana kira Bala,

Da sauri ya karaso "Hajiya gani" Ya faɗa cikin girmamawa dan tun kyautar data mashi ya shiga kara girmamata,

"Kana da lambar Ubangidan ka na kasar waje?

" A'a ba ni da shi sai dai Sarkin gida ba zai rasa ba saboda ko wani abun ya taso"

"Yi sauri ka kiramin shi"

Har zai fita sai kuma ya juyo"amma baki da number ne Hajiya?

"Ohh kai dai da wannan tambayar,to numbobin waya tane suka goge"

Dan dariya tayi"ok ok na gane,in ba haka ba ai da sai nayi mamaki"ya karasa faɗa yana fita,

Tama kasa zaune ta kasa tsaye,ganin ya jima ne yasa ta fita dan gara ta bishi ta amsa da kanta,dan gani take kamar ko wani dakika ta kara kamar barazana ce a gareta,
In da tasan sarkin gidan ya cika zama nan ta nufa,yana ganin ta ya mike yana amsar takardar da yake mika ma Bala,
"Hajiya da kanki,ai da sai ki bari na zo"

"Kaga sauri nake bani number"

Mika mata takardar yayi"wadannan sune numbobin da yake amfani dasu guda uku,
Daya na Paris ne,dan yace a kwai aikin da zai tafi yi a can,amma ban san ko yaje ba,in dai yana can to zaki ga number dana rubata Paris,sai biyu kuma na Germany wanda idan yana can shima yafi amfanin da layukan,kuma idan yana nan ma wani lokaci yana amfani da dayar"

Da sauri ta juya tana fadin "na gode"

Daki ta koma har da saka key,sannan ta zauna ta shiga loda number ta farko a wayar,
Har ta kammala tana ƙoƙarin danna kira wani tunani ya fado mata,to yanzun idan ma ta kira shi me zata ce mai,me zata faɗa mashi,me kenan take kokarin aikatawa,
Da sauri ta sauke hannun ta daga kan wayar,amma kuma kaso casa'in na zuciyar ta ba karfafa mata guiwar koran shi,
Ta ma rasa me zata kama,shin ta kira ko karta kira.


*fans Yar tsanar zinari na niman shawara,shin ta kira Suraj ko karta kira shi*.....

🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*40*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*

Kafin ta sani sai ji tayi ana Sallamah,
Da sauri ta kara wayar a kunne sai dai sam ta kasa magama,dan jin muryar shi kaɗai da tayi yasa taji faduwar gaban ta ya ƙaru a maimakon raguwa,

Shima daga nashi ɓangaren jin shiru ne yasa shima yayi shiru yana sauraran yanda take sauke numfashi a hankali,
"Idan kinsan ba kida ƙwarin gwiwar yin magana me na kira?

Cikin mamakin abinda ya faɗa tace" Ya akayi kan nice "

"Tambayar da kika kira kimin kenan?

Turo baki tayi" To nama fasa faɗa tunda abinda zaka ce ke nan"

"Shiken " Ya faɗa yana ƙoƙarin sauke wayar,

"Wait, wai kai mai yasa baka iya lallashin mutum bane?yanzun baka son kaji me zan faɗa?ka sani ko abunda zai amfaneka ne?

Dan murmushi taji yayi wanda kaɗan sautin haka ya sauka a kunnen ta," Daga dukkan alamu yau Mage a tsorace take,me ya faru?

Dan shiru tayi kamar mai nazarin abin da zata faɗa,ta kwashi kusan mintuna goma ba tare data iya furta komai ba,yayin da shi kuma yayi shiru shima yana sauraren yanda Lokaci-lokaci take sauke numfashi ba tare daya ce mata komai ba kuma bai kashe wayar ba,
Sai da ta gaji da saƙawa da warwarewa kafin tace"ina ganin kamar akwai abinda ke shirin faruwa"
Jin shiru yayi ba tare da an bata amsa bane yasa ta cire wayar a kunnenta ta duba,ai kuwa har lokacin yana kan layi,hakan yasa ta maida wayar kunnen ta"kana jina kuwa?

Nan ma sai da aka dauki ƴan sakanni kafin taji yace"Umm "

A hassale tace "to baka ce komai ba?

"Ina jinki"

"Ai Nasan kana jina"

Kamar wanda baya son maganar yace"me zai faru?

Wannan karon ta kasa rike bacin ranta dan haka cikin masifa tace "ban sani ba,idan ka ga dama duk in da kake sai ka kiyaye idan kuma ka yi sake ka rasa rayuwar ka kai ka sani"ba tare data jira taji mai zai ce ba ta kashe wayar,dan ba karamin haushi ya bata ba,haka kawai tana ƙoƙarin taga ta ankaran dashi amma ya tsaya yana nuna mata miskilanci,tsaki ta ja,tana ƙoƙarin tashi ne taji saƙo ya shigo wayar ta,kamar ta share sai kuma ta bude "I know you need me a life"
Abinda saƙon ya kumtsa kenan,
Ta maimaita ya kai sau nawa amma ta rasa gane ina ya dosa,
Yinin ranar tayi shine ba'a cikin natsuwa ba,domin hankalin ta a tashe yake,bata san me zai faru da ita ko shi ko Ummita ba,idan har suka ci nasara akan shi kamar sun samu nasara ne a kanta,idan kuma wani abune ya samu Ummita bata masan me zata iya aikatawa ba nan gaba,
Abunda ta jima rabonta da tayi shine yau ta tashi tana yi,wato Sallah Nafila wanda rabon da tayi ta kai shekara uku zuwa huɗu.

Anashi ɓangaren kuwa yana gama tura mata sakon ya maida kanshi ya jinginar yana rufe idanun shi yana nazarin kalamanta,sai dai baya son ya kawo komai a ran shi,
Jin ana kiran Fasinjojin da zasu tafi Nigeria ne yasa ya tashi ya ƙarasa,dan yanzun jinginsu zai tashi,wanda zai sauka ne a Legos,
Bayan kammala duk wani bincike aka basu dama suka shiga jirgi,bakin shi dauke da Addu'a,ƙarfe shidda na yamma jirjinsu ya sauka a Legos,
Duk yanda yaso ya kwana a gida dole hakura yayi ya kama Hotel saboda ma'aikatan airport din sun tabbatar mashi da babu jirgin Kano sai dai zuwa gobe da safe ƙarfe goma,
Dole ya hakura,
Babban daki ya kama na kwana daya a babban Hotel din daya sauka,wanka ya fara yi sannan yayi ordan Abinci yaci,
Ganin lokacin sallah Isha'i yayi ne yasa ya fito daga dakin bayan ya kulle ya fita domin duba ko akwai inda zai samu masallaci kusa,dan sam baya son yin sallah shi kaɗai a gida ko a daki indai ba ya kama bane,
Tafiya yake yana ɗan duddubawa kafin Allah ya taimake shi ya samu,lokacin ana ƙoƙarin tada sallah,duk da yake masallacin na Yarbawa ne hakan be dame shi ba domin Allah daya suke bauta ma,dan haka yabi su Jam'i har aka idar sannan ya koma masaukin shi,har ya kusa isa daki yaji kamar ana magana ana kuka ta wani lungu,kamar dai ya share sai kuma ya matsa ta wurin yana lekawa,
Wani mutumin ya gani daga dukkan alamu ma'aikacin wurin ne,dan sanye yake da kaya irin na masu aiki a kicin,
Waya yake yana sharban hawaye,
Ganin Suraj din tsaye yana kallon shine yasa ya yanke wayar da sauri yana tambayar shi da harshen Turanci,"ko akwai abinda yake buƙata ne?

Girgiza mashi kai kawai yayi alamun babu,har mutumin zai wuce sai ya dakatar dashi,yana tambayar shi me ya same shi yake kuka"

Kamar bazai faɗa ba amma ganin yanayin Suraj din kamar mai kuɗi kila yana iya tausaya mashi yasa ya faɗa mashi Ƙanwar shi ce ta mutu wata biyu kenan tana Matuwari,shida maman shi dan Baban su ya mutu,kun kasa tara kudin da za'ayi bikin Binne ta,to yanzun gashi a ƙauyen su har an fara yima Mamar shi gori,shi yasa abun ke damun shi,kuma ya roki alfarma wurin aikin shi a bashi rancen dubu hamsin amma sun haka shi"ya karasa faɗa wasu hawayen na zubo mashi,

Suraj mutum ne mai tausayi,wanda ba shida rowa ko kyashi,bashi da nuna Ƙabilanci ko Addini,idan zai maka abu da zuciya daya zai maka ya wuce ba tare daya waiyaye abun da ya maka ba,
Dan haka cikin tausayawa yace,ba tare daya tambaye shi nawa ne kudin ba,yace"Bani Account number ka"

Cikin sauri kuwa ya karanto mashi,rubutawa yayi a wayar ba tare da yace mashi komai ba ya juya yayi tafiyar shi,shima mutumin da kallon mamaki ya bi shi har sanda ya buɗe ƙofar dakin wanda kuma a daidai lokacin yaji Alart, yana dubawa Dubu dari biyu ya gani,
Da fari bai yarda ba,sai da ya kara karanta sakon yakai sau biyar sannan ya tabbatar,ai kuwa tsalle ya kama shi kadai yana kukan murna da jin daɗi,bai taba tsammanin a Musulmai akwai mutanen kirki irin wannan mutumin da yaga sunan shi ya bayyana a Account din wai Suraj ba,abinda ƴan uwan shi suka kasa mai,shi kam ba zai taba mantawa da wannan mutumin ba,ai kuwa washegari da safe zai bar garin ya komai ƙauye,dan ƙanwar shi bikin gata za'a mata.

Da sallamah ya shiga dakin duk da yasan ba mai amsa mashi,zama yayi kan kushin yana cigaba da jan carbinshi ya ɗauki wasu yan lokuta a haka fakin ya mike,kai tsaye banɗaki ya shiga ya leka sai dai babu komai a ciki,haka kurum yake jin wani irin a jikin shi kamar akwai abinda ba daidaiba a dakin,sannan kamar kanshin dakin ya canja mashi,har kasan gado ya duba sai dai bai ga komai ba,
Mikewa yayi yana tunanin gara kawai ya fita ya masu magana a canja mashi ɗaki ko kuma yama bar Hotel din gabaɗaya,dan zuciyar shi ya fara bashi Something is not right some were,Gara ma kawai ya tafi,
Har ya kai hannu zai buɗe Sif din kaya yaji ana danna karrawar dake nuna alamu ana buƙatar shigowa,da yaso ya share har ya dauko kayan shi,wanda ba komai bane sai karamin jakkan shi mai ɗauke da wasu takardu nashi,
Jin yanda ake danna kararrawar babu kakkautawa ne yasa yaje ya buɗe ƙofar,
Tsayawa yayi yana kallon su cikin mamaki yayin da mamakin shi ya karu a sanda daya daga cikin su yaja hannun shi ya saka mashi Ankwa yana fadin"you are under Arrest,Abisa laifin kisan kai"

Wannan karon abin yazo mai ata inda bai taba zata ba,kisan kai kuma,kisa fa!inna'lillahi wa'inna ilaihi rajiun,abinda yake ta maimaitawa kenan,

Shiga cikin dakin suka yi yayinda sauran mutum uku suka da suke riƙe da shi har cikin dakin,
Kallon ikon Allah kawai yake yi,har zuwa sanda daya daga cikinsu ya buɗe Sif din,ta iya yuwa su basu shiga Shock ba,amma kam shi yayi suman wucen gadi yayi,
Domin Gawar Mace ce makale a jikin Bangon Sif din yayin da jini ke zuba a jikinta kamar yanzun aka yanka ta,haka kuma an cire idanun ta da Harshen ta,
Duk kiran sunan Jijos kawai suke kasancewar su Arna,
Ko mintuna biyar ba'a yi ba,sai ga masu binciken gawa da Ƴan gidan Jaridu sun shigo dakin yanda kasan wadanda dama a shirye suke,
Nan take aka shiga ɗaukar shi hoto tare da gawar,
Abin karin girgiza a wurin shine Jakkan shi da aka buɗe aka samu Idon matar da kuma harshen ta a ciki,
Tunda yake bai taba shiga tsananin tsoro da tashin hankali ba irin wannan,da ba ɗan karfin Addu'ar da yake yi ba da tuni shima ya yanke jiki ya faɗi,
Daya daga cikin ma'aikatan ne ya ɗaga gabjejen hannun shi ya koda mai lafiyayyen

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login