Showing 90001 words to 93000 words out of 159134 words

Chapter 31 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt

27 Sep 2025

9761

Nan ya shiga sanar da ita abinda ke faruwa har karshe kamar yanda Hashim ya sanar dashi"

"To su waye ta gani ta bi,me kuma ya faru a cikin gidan,me take son ta fada maka?

" Ammi koma dai menene ba karami bani na tabbata"

"Gobe zan zo insha Allah zan biyo jirgi,sannan ka kwantar da hankalin ka insha Allah zata ji sauki za'a dace"

"Allah yasa Ammi" Daganan sallamah suka yi ya kashe wayar ya kwanta,sai dai duk yanda ya so yayi barci ko ya huta kasawa yayi,dan haka tashi yayi ya jawo jakkan ta ya buɗe,hannu ya saka a ciki sai gashi ya ciro wayar ta,sannan ya zazzage jakkan gaba ɗaya saman gado,
Takardu ne a ciki sai man baki da sauran kayan kwalliya dai na mata,sai makullin gida, mai da komai yayi cikin jakkan ya adana,
Ranar bai samu yayi bacci ba domin kukan shi da godiyar shi ya rinka mikawa ga Allah,
Ba ya so ya rasa ta ko ta rasa wani ɓangare na jikin ta,

Washegari ma ko kafin su Abbu su tashi bacci shi har ya wuce Asibiti,sai da suka duba dakin shi a kulle shine suka kira shi ya sanar dasu ai tun ƙarfe bakwai na safe yana Asibiti,

Abbu ne yace"ka kuwa karya "

Dan shiru yayi kafin yace"yanzun zan karya dan na ga akwai wurin cin abinci a asibitin "

Cikin yana yi na dan faɗa faɗa yace"kasan ƙarfe nawa yanzun kuwa?

Kallon agogon hannun shi yayi wanda ya nuna ƙarfe goma da rabi na safe "Sorry Abbu"

"To ka dai dinga kiyayewa muma gamu nan zuwa"

"To sai kun iso" Ya faɗa yana sauke wayar,

Lekawa yayi ta glass din dake tsakanin su a I.C.U,tana kwance yanda kasan gawa babu ta inda take motsi sai na'urorin dake aiki a kanta wanda har saman kanta aka mammanna wasu karafe ƙanana,

Ji yayi an dafa shi daga baya,
Juyawa yayi,ganin Doctor ne yasa ya sauke numfashi,
"Kana son ka shiga ka ganta?

Girgiza kai tayi" Ba sai na shiga ba"

"Ka tabbata?

" Umm,yaushe za'a shiga aikin?

"Nan da ƙarfe biyar na yamma"

Lumshe ido yayi ya buɗe waɗanda yake ji sun mai matukar nauyi "ina fatan dacewa"

"Da yardar Allah"

"Zan je na dawo zuwa anjima"

"Ba damuwa ranka ya daɗe"

Juyawa yayi ya wuce,sai da ya je yaci abinci sannan kai tsaye ya wuce unguwar da Hashim ya mai kwatance,har ƙofar gidan kuwa aka kaishi,

Da makullin daya dauko a jakkan ta dashi yayi amfani ya buɗe har cikin falon,

Sai da ya gama ƙare ma falon kallo wanda yake tsaf sannan ya shiga dakin da ya gani a buɗe,

Daga dukkan alamu a nan take kwana,dan ga dakin nan da kayan ta har a saman kushin,daga dukkan alamu bata kyara dakin ba ta fita,
Gaban madubi ya tsaya wanda ke dauke da man shafawarta sai turarukan jiki,
Daukar daya yayi ya buɗe ya fesa a iska ya lumshe ido yana shakar ƙamshin,tabbas shi ta saka shekaran jiya data zauna a jikin shi,

Wani takarda mai ɗan girma ya gani a saman madubin,bangon littafin ya ja hankalin shi har ya shafa littafin,

Haka kawai yaji yana son buɗewa yaga me a rubuce,
Bin umarnin zuciyar shi yayi ya buɗe wanda shafin farko kyakkyawar rubutunta wanda yake jere bisa tsari yaga an rubuta *MY DESTINY* ( *Kaddarata* )da manyan harafi,
Ya dau sakanni yana mai maita sunan a zuciyar shi kafin ya buɗe shafi na biyu,
Abinda ya gani a rubuce ne yasa ya mai da takardar ya rufe ya ɗauka sannan ya rufe gidan ya koma Hotel din daya sauka,
Yana shiga daki hawa saman gado yayi ya zauna tare da kara buɗe littafin wanda daga dukkan alamu tarihin asalin rayuwar ta ne a ciki wanda shi kanshi zai so yaji wacece asalin Biba da kuma Ummu Salma,me alakar dake tsakanin suna biyun nan,menene ya faru da rayuwar su da kuma kaddaran dake bibiyar su.....

🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*55*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*

Shafi na biyu daya bude a cikin littafin,ya shiga bin abinda ke rubuce daki daki makar haka:A ranar Laraba sha biyu ga watan Agusta shekara ta dubu biyu da ishirin da huɗu,da misan ƙarfe goma na safe,iska ne mai matukar daɗi ke kadawa yayinda tsuntsaye ke tashi daga wannan bishiyar zuwa wannan,ta gefe ɗaya kuma idan har na kalli gajimare abin na matukar kayatar dani,saboda ina son kallon sararin samaniya ko dai lokacin haɗari ko kuwa lokacin da taurari ke baiyana,na kan tsince kai na cikin tsananin farin ciki kamar yau,
Tafiya nake ina juyawa yayin da kaina ke kallon sama,sabanin sauran mutane dake tafiya suna kallon gabansu ko gefe,

Ji nayi cikin zafin nama da karfi an jawo ni baya,wanda sai da nayi tangal_tangal kafin na tsaya da kafafuna,
Cikin masifa ya fara faɗa "wai ke wata irin yarinya ce da magana daya baya mata,ta yaya zaki saka kai a Titi ba tare da kin duba ba,kalla yanzun saura kaɗan mota tabi ta kanki amma ko sani baki yi ba"

"Na sani Mana yaya"

"Kin sani shine zaki shiga titi haka?

Dafa shi tayi" To me yasa zan wani damu da kallon Titi ba yan ina tare da ku"

"Me kike nufi"

"Ga ka ga Yaya Abdulmajid,ai kune ido na bana bukatar yin amfani da nawa"

Karamin tsaki ya ja yana jinjina shirme irin na Ummu Salma "

Jan kunnen ta yayi da ƙarfi "ai kuwa shi yasa baki gajiya da faɗawa kwalbati"

Ihu ta saka tana kiran sunan "Ya Majid"

Da sauri wanda aka kira da Majid din ya juyo yana sallamar Abokan shi da suke tare ya karaso in da suke"me ya faru "ya tambaye dan uwan nashi dake ke rike da kunnen ta har yanzun,

" Sauran kaɗan mota ya bige ta"

"Kai kana ina har mota zai bige ta,hankalin ka na ina,shi yasa nace ai ka bita a baya kana kallon hanya," Kwace ta yayi"sake ta ai duk laifin ka ne"

Buɗe baki yayi yana bin su da kallon mamaki,duk da wannan ba shine bane karo na farko ba,in dai zata fita sai an haɗa ta da wani a cikin su,saboda tsabar kanta bai iya tsayawa wuri daya,idan kuwa ka bari taji ciyo ka shiga uku ko a wurin mama da sauran su,

Yana biye dasu a baya har suka shiga cikin unguwar su wanda yake na matsakaita ƙarfi ne,
Tunda suka shiga layin su duk inda suka gifta in da akwai manya a wurin sai sun gaida su,
Su kuma suna amsawa cikin sakin fuska,

Da haka har naga sun doshi Get din wani makeken gida wanda kaf unguwar babu gida mai girma da tsaruwa irin shi,
Kwankwasa karamin ƙofar gidan suka yi sai gashi mai gadi ya fito ya buɗe masu,

Ko asalin cikin gidan abin kallo ne ba sai na tsaya faɗa maku ba,
Tana ganin sun shiga cikin gidan ta fisge hannun ta da gudu ta karasa cikin falon gidan tana kiran sunan Mama babu kakkautawa,

Cikin sauri ta fito daga kicin hannun ta rike da Cokalin miya,
Dafe Kwankwaso tayi tana kare masu kallo,
Itama dafe kwankwaso tayi tana kallon Mama tana kyafkyafta ido,ganin Mama na ma Ya Abdul majid signal akan ya kamo mata ita ne yasa ta zabura zata gudu dakin ta,duk bin bayanta suka yi yayin da suka shiga zagayen falon suna dariya,har Mama ta samu nasarar kamata a ɗaura a kafaɗa tayi kicin da ita,
A wannan lokacin shekara ta goma sha huɗu a duniya,ba ta da wani nauyi sai tsayi,
Wurwurga kafa ta fara tana rokon Mama "dan Allah bana karki shigar da ni kicin,bana son kicin"

"Ni kuma bana son kira kamar wata batatta"

"Mama kiyi haƙuri ba zan kara kiran ki ba"

Direta tayi a gaban sink din kayan wanke-wanke, "ga aikin ki nan"

Turo baki tayi tana fashewa da kuka,dan ita a rayuwa ba aikin data tsana irin ace tayi shara tayi wanke-wanke,kallon Abdul Majid da Abdulmalik take tana mika masu hannu,

Dan marairaice fuska Abdul Majid yayi"Mama na taya ta?

Girgiza kai tayi "No"

"Pls Mama,let us help our little sister"

"Kuje ku kyara min dakin Baban ku yanzun"

Badan sun so ba dole suka tafi,
Ganin sun wuce ne yasa dole tayi shiru domin ta san a wannan lokacin Mama ba kula ta zata yi ba,
Dan haka Safar hannu dasuke amfani dashi wurin wanke-wanke ta saka sannan ta buɗe fanfo ta fara,

Kiran da aka ma Mama a waya ne yasa ta dauka tana barin kicin din,

Kamar jira suke ta fita sai ga Abdulmajid ya shigo "kawo safar hannu"

Zarewa tayi ta bashi,nan da nan kuwa ya shiga taya ta wankewa tana daurayewa har suka kusa kammalawa,
Jin takun tafiyar Mama ne yasa da gudu ya fita kicin din ya bar ta bayan ya cire safar,
Da sauri ta maida shi a hannun ta tana ƙara marairaice fuska,

Kallon kayan tayi ta kalle ta"ke waye yazo ya tayi ki"

Kumbura baki tayi"babu kowa"

Girgiza kai tayi domin tasan karya take yi,wannan saurin ba nata ba ne,

Sai da ta saka ta kammala ta wanke wurin sannan ta bari ta fita,

Ɗakinta ta shiga wanda ya ji ado da kayan more rayuwa irin na matasan yan mata waɗanda ake ji dasu,

Hayewa tayi saman kushin ta ɗauki wayarta tana buga game,
Ba adau wani lokaci ba sai ji tayi ana ƙwanƙwasa mata ƙofa,
"Come in" Ta fada da ƙarfi,

Turo kofar Mama tayi"ki fito ki ci abinci"

"Na koshi"

"Bana son jin haka maza ta so mu je"

Ajiye wayar tayi ta fito,ko da suka fito har yannin ta sun fito ko suna zaune sai Baba da shima shigowarshi kenan,
Da gudu ta karasa inda yake ta rike hannun shi"Baba na barka da fitowa"

Murmushi yake saki "barka mai gimbiya,da fatan kin tashi lafiya"

"Lafiya glau"
Zama suka yi a saman babban Darduma na falon,duk barka da fitowa suka mai,
Mama ce ta zuba ma kowa abincin kari,
Cikin natsuwa suke ci babu mai magana har suka kammala ita ta kwashe kayan ta mai da su kicin sannan mai aiki tazo ta wanke,

Dawowa falon tayi ta zauna a tsakiyar yannin ta,"Baba ina son in siya wani takalmi dana gani ana tallah a online "

"Nawa zai maki?

" Dubu hamsin "

"Zan tura maki,ke ma ban manta da Alkawarin mu ba"ya faɗa yana kallon Mama,

Kiran da aka mashi a waya ne ya katse su,
Sun dai ji yace" Shigo"

Ba jimawa kuwa sai ga wani matashin saurayi ya shigo cikin falon da sallamah,daga dukkan alamu shi din ɗan gidan matsakaita ne daga ganin yanayin kayan jikin shi,kana kuma iya saka shi a sahun talaka amma ba tubus ba,
Kyakkyawa ne baki ba laifi dan alokacin rashin kuɗi ya hana kyan shi fitowa,

Dukawa yayi ya tsugunna har kasa yana gaida su,Baba da Mama ne suka amsa mashi sannan ya gaida su da suke kallon shi dan ba Kasafai Baba ke bari wani ya shigo har cikin falon shi haka ba,

"Wannan shine *Yusuf*,shekaran jiya ya fara aiki a kamfani na na Suger"

Kallon yaron Mama ta kara yi,nan take fara'ar dake fuskanta ya ɓace "gaskiya wannan yayi ƙarami"

"Na dauki wadanda basu kai shi komai ba kuma sun iya balle shi,kuma a matakin manager zan Daura shi"

"Allah ba da sa'a ta faɗa tana mikewa tare da barin wurin,
Sallamar shi Baba yayi akan ya jira shi a waje yanzun zai fito.

Ranar ƙarfe hudu suka kuma zuwa islamiya wanda da ma hakan yake duk ranar sati da Lahadi sau biyu suke zuwa islamiya,
Tana zaune a aji ana karɓar hardansu na Kur'ani sai ga Malam babba ya aiko a kira ta,
Sai da malamin dake ajin ya karɓi hardan ta sannan ya bari ta fita,domin haka dokar su take,to yanzun haka tana izufi Arba'in da biyu ne a harda,
Tana shiga ofishin shi da sallamah ta gaida shi cikin Girmamawa,
Nuna mata gefen shi yayi"Me alaƙar ki da waɗannan "

Kallon su take daya bayan daya kafin ta zare ido tana kokarin karasa kusa da ɗayan,
Dakatar da ita yayi"baƙi Bani amsa ba"

"Malam wannan yaya na ne,sai wannan kuma saurayi na ne"

Kallon ta sauran Malam dake ofishin suka yi,
Daya daga ciki ne yace"kai jama'a lallai duniya ta zo ƙarshe,yanzun ke ƴar ƙarama dake har kinsan ki nuna wani a matsayin saurayin ki ba tare da kinji kunyar idanun mu ba?

Bata fuska tayi"Malam to ai naga ku kuke faɗa mana ƙarya haramun ne,yanzun kuma dan na faɗi gaskiya sai ace nayi rashin kunya?dama fadar gaskiya na zama rashin kunya lallai duniya ta zo karshe"ta faɗa tana dafe gemunta da hannu,

Dariya Malam babban yayi,dan yanda ta karasa maganar dole ya baka dariya,kallon su yayi"me ya hada ku faɗa a kanta"

Ɗayan yaron ne da bai wuce shekaru sha biyar ba yace"Malam muna hira ne a ajin mu shine kowa ke fadin sunan budurwa shi,ni kuma da aka tambaye ni na kira sunan ta,shine fa ya taso ya ƙoda min Mari wai akan wani dalili zan ce ita duburewa ta ce "

Maida kallon shi kan Abdulmajid Malam babba yayi"da gaske hakan ne ya faru?

Dukar da kai yayi "haka ne Malam"

"Yaya" ta kira sunan shi cikin jin haushin abinda ya aikata,

Dagowa yayi yana hararan ta"Do you tell me?

"Amma ai dama zan faɗa maka"

"To be mun ba"

"But I Love him"

"Sama da ni?

Lokaci ɗaya kuma ta saki murmushi ta tako har gaban shi ta rungume shi" Ai kai rayuwata ce,duk kuma abinda rai bai so ai barin shi yafi"

"Da gaske"

Jinjina mashi kai tayi "sosai,dan haka karka kara faɗa da wani"

Murmushi ya saki shima"good Girl "

Sake shi tayi"Malam kayi haƙuri yaya na bazai ƙara faɗa ba,"

"Ke ce bakin shi?

" Umm "ta fada maimakon ta cewa A'a,

Dan waro ido yayi" Umm"

Shiru ta mai dan wannan tambayar Malam Buhari ne dama kuma shi ba shiri suke yi ba,

"Ku biyo ni dole zaku karɓi hukunci domin makaranta ba wurin wasa bane,ba kuma wurin dambe ba ne"

Tashi suka yi suka bi bayan shi har ofishin shi,ganin ya dauko ƙato bulala ne yasa ba shiri ta shiga rokon shi akan dan Allah yayi haƙuri karya Duke yayan ta,

"Ki koma aji domin dole sai an hukun tasu".

🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*56*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*


Kin tafiya tayi ta tsaya a wurin har Malam Buhari ya dauko bulala ya shiga zuba ma Yaya Abdulmajid,a duk bulalan da zai sauka a jikin shi ji nake tamkar a jiki na yake sauka,shi ake duka amma ni make faman zuba kuka shi kuma yana faman faɗin "ya isa haka ai babu zafi ma,ki dai na kuka"

Shi kuma mugun malamin sai ƙara dukarmin yaya yake yi,
Jin irin kukan da nake yi har da hadawa da ihu ne yasa Malam babba ya fito daga ofishin shi yace dukan ya isa haka ya bar su,
Dole ya bar su badan ya so haka ba,dan yaran haka kawai suke bashi haushi saboda yanda yake ganin su ko yaushe a tare,
"Malam ban fa yi mashi wani bulala ba,kawai makirci ne irin na wannan yarinya ita kullun haka take in dai za'a daki daya daga cikin yannin ta sai ta zo ta tasa mutum da kuka kamar ana yanka su"

Murmushi Malam babba yayi yana kallon yanda take cigaba da kuka tana duba tafin hannun yayan nata,shi kuma sai cewa yake"ai hannun ba yamin zafi,ki bar kuka haka"

"Tashi ku koma aji"

Mikewa suka yi suka fita sai da ya raka ta har bakin ajinsu ya tabbatar ta shiga sannan ya koma nashi ajin,

Ko da aka tashi islamiya tare suka jero sun saka ta a tsakiya kamar ko yaushe,
Abdulrahman ne yace"wai ke yaushe zaki daina wannan fushin ne,na ga shi wanda aka daka har ya hakura amma ke sai fushi kike yi"

"Yaya wallahi malamin nan haushi yake bani,kome nashi na mugunta ne,amma bari sai nayi maganin shi"

"Me zaki mashi? Cewar Abdulmalik,

" Sirri ne"

"Don't just go and do anything stupid" In ji Abdulrahman,

Kin bashi amsa tayi sai ma ƙara sauri da tayi ta yi gaba ta bar su,dole da sauri suka bi ta,

A ƙofar gida suka haɗu da Yusuf yana zaune,
Yana ganin su ya tashi ya mika masu hannu suka gaisa,
Abdulrahman ne yace"me kake yi a ƙofar gida?

"Ba komai kawai dai na shigo ne mu gaisa Mama tace kuna islamiya"

"To ai daka zauna ciki,shigo mu je"

Bin su ciki yayi sai da suka shaida ma Mama sun dawo kafin su shiga nasu falon dashi,

Tana gama cire kaya dakin su ta shiga bayan ta canja wani,zama tayi cikin su suka shiga yin hira,
Kallon Yusuf tayi "Ka iya game?

" Wani iri?
"Motal comebat"

Girgiza kai yayi"A'a "

"Yana da daɗi sosai bari na koya maka"

Jona TV tayi ta haɗa da kayan game,nan suka shiga bugawa tana yi tana nuna mashi,
Sai da lokacin sallah yayi sannan suka fita masallaci ita kuma ta shige daki,

Washegari tunda Asuba ƙarfe biyar kafin ayi sallah ta tashi bacci ko wanka bata yi ba ta buɗe ƙofa ta nufe shiyansu,bubbuga masu ƙofa ta fara da karfi tana kiran Ya Abdulrahman,ya Abdulmajid,ya Abdulmalik,haka ta shiga kira tana buda ƙofa wanda ƙaran haka ne ya tayar da Baba ya fito yana haskawa dan jin ko lafiya,
Ganin ita ce yasa yace"Gimbiya lafiya?me kike yi a nan yanzun"

Turo baki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login