Showing 54001 words to 57000 words out of 159134 words
Chapter 19 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt
lulluɓe da kallon nazari,dan daga dukkan alamu doguwa ce sai dai ba can ba,sannan siririya nan ma ba sosai ba,tana da shef sosai duk da a lulluɓe take,to ko ya fuskarta zai kasance tunda yaji abokin nashi yace tana shan sigret,ko ma dai ya take nan ba da jimawa ba zasu haɗu.
Buɗe mata gidan baya tayi"ki shiga nan ki zauna,sai da safe ni na tafi"
"Na gode Nafisa ba zan kuma manta dake ba"
Cikin jin daɗi ta ce"ai kuwa na gode"sannan ta ja mata kofa ta rufe,
Kyara zamanta da kyau tayi tana sauke ajiyar zuciya tare da cire mafayin dake lulluɓe a kanta,
Wani irin fitinannan kamshi ta ji yana tashi a cikin motar wanda ta saka ta lumshe ido ta buɗe,
Jin kamar numfashi a gefen ta ne yasa da sauri ta kalli wurin,
Yana zaune idanun shi a lumshe yana jan carbi,yayin da yayi tamkar bai san da mutum a gefen sa ba,
Kallon shigar dake jikin shi tayi tana tabe baki,wato da Jallabiya yazo ɗaurin auren shi,ɗan ƙaramin tsaki taja wanda bata yi tunanin ya fito ba,
Kamar mai ciyon baki taji yace"wannan ya zama karo na karshe"
Da ba dan ta kwantar da hankalin ta ba da bata fahimce me yake nufi ba,magana a gutsurew ba tare da an kai ƙarshen shiba,
Farhan ne ya buɗe mazaunin direba ya shiga yana daɗin "Amarya baki laifi ko da kin mari ango"
"Ba dai irin wannan ba"
Jin abinda tace ne yasa ya dan saki dariya kaɗan,"ke dai faɗi gaskiya Amarya,kin ga dai ga angon naki nan zaune a gefe yana ji,ko zaki gwada?
"To kai ɗin me zai hana ka kwada na baka baki"
Wannan karon ko dariya yayi sosai"lallai za'a je dake,to ya kuma muka ji da jama'a?
"Alhamdulillah"
"Allah ya baku zaman haƙuri,"
"Amin"
Tayar da motar yayi suna barin harabar gidan"suna na Farhar "
"Ni kuma Biba"
"Nice to meet you" Tunanin bata jin Turanci yasa da sauri yace yi haƙuri "ina nufin naji daɗin haɗuwa da ke"
"Karka damu ni ma haka"
Daganan basu kuma cewa komai ba har suka iso Sultan road,
Kamar dazu babban Get din da kanshi ya buɗe suka shiga sannan ya kulle kanshi,
Daga kai tayi tana kallon gidan wanda gabaɗaya kusan rabin shi da Glass aka yi shi,ba karya ya haɗu,ta faɗi hakan a zuciyar ta,domin ita a wurin ta ba wannan ne karo na farko data fara ganin ire-iren wadannan gidajen ba,tunda tayi zaman kasan waje kuma ta zagaya kasashe da dama,
Ganin uban gaiyar ya fita ba tare da ya ce mata komai ba yayi gaba yana taku dai daya kamar bai son yi,
Taji an buɗe mata ƙofar "fito Amarya"cewar Farhar,
Fitowa tayi" Na gode "
"Mu tafi ciki kafin ya kulle ƙofar"
Ita dai bata ce masa komai ba tabi bayan shi har cikin madaidaicin falon,
Ganin ya doshi sama ne yasa tabi shi har cikin dakin,
A zaune suka same shi a bakin gado dafe da kai,
Jin takun tafiyar na mutane biyu ne yasa ba tare daya dago ba yace,
"Me ta shigo min a daki "
"Me kake nufi?
" Kace ta fitar min a daki"ya fada wannan karon yana daura idanun shi akanta,
Wanda hakan yayi dai-dai da zame kyalen kanta data kuma yi gabadaya ta rike a hannu,
Hakan yayi sanadiyyar baiyanar kyakkyawar fuskarta da yake ƙyalli ba tare da ko digon ƙwalliya ba,haka kuma lallausar sumanta dake kwance a gadon bayanta saboda kalar ɗaurin dankwalin da tayi,
Ita ma tana daura nata idanun a cikin nashi......
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*35*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Kafin ta saki wani lallausar murmushi wanda ya baiyana fararen haƙoran ta suke jere tas dasu,sai kuma dimful wanda ya baiyana a gefe ɗaya na kumatun ta,
A hankali take takowa da takalmanta masu dan tudu har ta isa gefen da kushin yake tama kanta mazauni a wurin kafin ta juyo da kallon ta kan Farhan wanda yayi suman tsaye yana binta da kallo"Farhan ka faɗa mashi shin ya manta matsayi na ne a wurin shi,dan haka bai da hurumin faɗar haka"
Mai da kallon shi kan Suraj yayi"tace baka da hurumin fadar haka"
"Ka faɗa mata ta zaɓa wani ɗakin acikin ɗakunan duk wanda ya mata ta zaɓa,amma ba na son tazo inda nake"
Kallon ta yayi sai dai kuma ya rasa me zai ce mata,saboda yarinyar ba karamin kwarjini ta mai ba,
"Me ya faɗa Farhan"a zuwan ita bata ji me yace ba
"Ummm cewa yayi babu komai kina ina zama duk in da ya maki"
"Yauwa na gode Farhan"
Cikin sauri yace"yaushe na faɗa maka haka,ke tashi ki barmin daki"
Turo baki tayi ta tashi tana takawa kamar zata bar ɗakin,juyowa tayi tana dawowa baya kafin ta juyo da gudu ta nufo in da yake,
Ko da ya dago kai kafin yace zai motsa sai jinta yayi ta fado jikin shi,gabaɗaya suka zube saman gado a kwance ita tana saman kirjin shi,
Kokarin ture ta yake daga jikin shi sai kwantawa tayi da kyau yayin da kirjinta ke gogon nashi,
"Idan kayi ƙoƙarin ture ni zan yi abinda baka so"
Kauda kai yayi yana furzar da iska,"ɗaga ni"
Girgiza kai tayi"a'a "
"What do you want?
Dan shiru tayi kamar mai tunani sai kuma ta juyo da kallon ta kanshi,yatsa tasa tana zagaye fuskar shi dashi," Do you hate me that much?
"Fiye da yanda hankali zai ɗauka"
"Har haka?
" Ɗaga ni"
Sauke hannun ta tayi a fuskar shi "ni ma na tsane ka sosai,fiye da yanda ka tsane ne,sai dai ba yanda zaka yi dani domin na zama matar ka,dolen ka,kuma na zama bindin ka,duk inda zaka tafi tare zamu rika zuwa,ka saka hakan a ranka"tana gama fadar haka ta sauka daga jikin shi ta doshi hanyar da suka shigo ta fita,
Dakin dake gefen nashi ta buɗe,nan ma a kyare yake babu abinda babu,dan haka zama tayi nakin gado tana ƙara nazarin dakin.
Shigowa yayi yana dan kalle_kalle a ɗakin,"ta wuce ne?
"Zo ka mai da min drip"
Hannun shi ya kama yana duba inda zai samu jijiya "tana da kyau sosai,na ɗauka zan ganta kamar sauran yan aiki,sai dai ita na daban ce"
Bai bashi amsa ba sai ma mai da idanun shi da yayi ya rufe,
Ganin haka ne yasa shima ya ja bakin shi yayi shiru,dan ya sani idan har yayi haka ba kara wata maganar zai yi ba,amma dai maganar gaskiya shine ta wuce da tunanin shi,sam bai yi tsammanin haka ba,sai dai daga dukkan alamu ita din ba ƙaramar yar duniya bace,yarinyar idanun ta a buɗe suke,shi wallahi da zai samu irin wannan bai ga abinda zai sa yayi wasa da damar shi ba,sai dai yasan halin Suraj,zai kuwa so yaga yaya wasan nasu zai kasance da yarinyar dan ita kanta hatsabibiya ce,
Yana gama saka mashi ya mashi sallamah ya wuce a kan sai sun haɗu gobe.
Washegari da safe koda ta farka ƙarfe tara na safe saura,ta jima bata samu tayi barci irin haka ba,dan haka banɗaki ta shiga tayi wanka da kalolin sabulan wanka masu kamshi da ta gani,wanda hakan ne yasa ta jima a cikin banɗaki,
Sai da ta tabbatar ta cire duk wani dauɗa da dake jikin ta lungu da tsako sannan ta dauro Alwallah ta fito,buɗe durowar dakin tayi,babu komai a ciki sai kayan maza,cikin Jallabiyoyin shi ta jawo ɗaya haɗe da boxe size ta saka sannan ta yafa gyale tayi sallah,
Tana idarwa falo ta fito dan ba karamin yunwa take ji ba,
Kallon wurin da ake shirya abinci tayi,ganin manyan kuloli tayi shirye a wurin,dan haka jawo kujera daya tayi ta zauna sannan ta shiga jawo ko wanne gabanta tana dubewa dan ganin me a ciki,
Lafiyayyen farfeson kaza ta zuba wanda ya ji sinadirin kanshi da ɗandano,sai kunun kyada,
Bata jima da fara ci ba ta ji takun saukowar shi,kallo daya ta mai ta dauke kanta tana ci gaba da taunar tsokar kazanta,
Cikin sauri Bala dake biye dashi a baya ya karaso inda take"malama daga ina,wacece ke?me kike yi anan,daga zuwa kuma sai taba abin mutane "
Kallon ƙasa da sama ta mai"tashi min a kai karka saka na kware"
"Wacece ke"
Ajiye naman dake hannun ta tayi,sannan ta karaso inda yake tsaye cikin sakin fuska,
"Mijina Abin Alfahari na barka da safiya,ya jikin naka?
Kauda kai yayi yaci gaba da takawa zama yayi kan kushin," Bala"ya kira sunan shi,
"Idan kuna bukatar wannan abincin ka kwashe,idan kuma baka buƙata ka fitar min dashi"
"To me zaka ci uban daki na?
" Ka samar min abu mai sauƙi,wannan kuma zata zauna damu na ɗan wani lokaci ka bata abinci yanda ya kamata,"
Zama tayi kusa dashi tana daura kafa daya kan daya kamar yadda yayi"Bala ni matar mai gidanka ne,dan haka dole ka jirmama ni kamar yanda kake girmama shi"
Cikin mamaki yake kallon ubangidan nashi,da mamakin yaushe hakan ya faru,da kuma yaushe yayi aure,sai dai katse mashi tunanin yayi ta hanyar fadin"Barshi"ya yi fitar shi,
"Ina sauran ma'aikatan gidan nan?
" Suna shiyan su"
"Ina bukar ganin su yanzun nan"
Bata fuaka yayi dan ya lura kamar so take ta rusa masa gwamnatin shi a wurin ubangidan nashi,
"Yanzun suna kan aiki ne"
"Kaje ka kira min su idan kuma basu zo ba a bakin aikin ka"
Dafe kirji yayi"bakin aiki na kuma,ta nan fa nake samu nake ciyar da iyalai na "
"Ba sai ka koma bara ba,dama akwai wanda nayi alƙawarin zam nimar ma aiki,yama fika dacewa da aiki,ka ga yanzun ni ce mata gida sai yanda nayi da mai gidan"
Cikin rawar jiki ya juya "bari naje na kira su"
"Dawo muyi magana tukunna"
Dawowa yayi wannan karon harda tsugunnawa dan ya lura in bai yi hankali ba wannan yarinyar da bata wuce sa'ar kanwar shi ba tana iya mai sage_geduwa gara ya bita a hankali,
"Idan har ka yarda zaka min aiki zan kara maka albashi akan wanda ubangidan ka ke baka"
"Wani irin aiki,sai dai ki sani in har na cutar da ubangida na ne ba zan karba ba ko nawa zaki ba ni"
Dan murmushi tayi"kwantar da hankalin ka dan ni ma ba zan iya cutar dashi ba,sai dai na kare shi,aikin ka shine kawai duk lokacin da kaga zai fita ka sanar dani,in da hali ma har in da zai je "
Ji yayi hankalin shi ya ɗan kwanta"in dai wannan ne ba kida damuwa Hajiya "
"To kaje ka kira min su gani nan fitowa"
"To hajiya"
Bayan kamar mintuna goma sai gashi ya dawo"Hajiya suna ƙofar falo"
Mikewa tayi ta fito a tsaye ta same su suna jiranta,ba tare da damuwar komai ba ta masu sallah,
Amsawa suka yi cike da tunanin wacece ita,domin wannan ne karo na farko da wata mace ta shigo nan ɗin,
"Ni suna na Habiba,matar mai gidan ku,nasan zaku yi mamaki,amma ba abin mamaki bane dan jiya aka ɗaura mana aure da shi"
Ganin duk sunyi shiru suna mata kallon mamaki ne yasa ta ɗan daga kafaɗa ta "akwai mai abun fada?
Girgiza kai sarkin gida yayi" A'a Hajiya "
"Well to ni ina da abun faɗa,na farko bana son gulma da kananun magana,sannan ina son girmamawa,ma'ana a dinga bani girma na,na uku kuma ina fata zamu zauna lafiya tare da ku"
"In sha Allah Hajiya"
"To sai kumin introducing kan ku"
Babban cikin su ne ya matso gaba"ni suna na Sarkin Gida,kuma ni ne babban su mai kula da duk wani harka na cikin gidan nan,sai wannan Bala shine mai yi ma uban gida girki,sai kuma direba,da masu kula da tsakar gida ta tsaftar gidan "
"Hakan yayi kyau,dan haka kuna iya tafiya"
"Mun gode" Suka faɗa a tare,
Komawa cikin falon tayi ta zauna tana sauke ajiyar zuciya,wayarta dake hannun ta shiga dannawa tana kwada number Ummita ko Allah zai sa ta sumu,sai dai abu ɗaya kawai ake maimaita mata shine wayar a kashe take,
Tsaki taja cike da tunanin a wani hali take ci,gabaɗaya wannan yanayin yana hana ta samun natsuwa,
Ji tayi kararrawar kofa yana ƙara alamun ana niman izinin shigowa,
Tashi tayi ta buɗe ƙofar,
Kallon_kallo suka tsaya suna ma juna kafin Zainab ta buge kafadarta ta shiga ciki,sai Amira sannan Aunty Hajjo dake,
Da Bala da sarkin gida ne suka shigo dauke da wasu manyan Akwataiya guda shiga suka jera a tsakar falon sannan suka fita,
Mai da kallon ta kansu tayi,sun yi wani zaman taƙama a falon yanda kasan na gidan su,
Cikin sakin fuska tace "Aunty Hajjo ina kwana,Amira sannan ku da zuwa"
Sai dai duk cikin su ba wanda ya bata amsa,
Sherawa tayi ta shiga kicin ta dauki masu gorunan ruwa da lemu,
"Kin ga dauke mana a gaba dan ba mu maki kama da wadanda suke ni ma ba"
Ita fa ta lura da take taken su,ba su san duk wannan abun da take masu na marmari bane,amma ba komai a hankali zasu san juna,
Aunty Hajjo ce tace"wannan ba rigar Suraj bane kika saka"
Murmushi ta saki cikin jin kunya tace"da Asuba ne da muka yi wanka tare to shi ne ba ni da kayan da zan saka shine ya saka min nashi"
Gabaɗaya miyon bakin su daukewa yayi,wanka fa tace tare da Suraj din kuma har da saka mata kaya,kenan ba dai har yayi wani abu da ita ba,kai Namiji ba shida amana,
Ganin halin da suka shiga ne yasa ta saki wani shegen murmushi tana ɗan dago kai,
Sai dai cikin rashin sa'a idanun ta ya fada cikin nashi dake tsaye rungume da hannu yana sauraran abinda ta faɗa.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*36*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Ganin irin kallon da yake jifanta dashi ne yasa tayi ɗan tsam kafin kuma ta kyara tsayuwarta tana ɗauke idanun ta cikin nashi"ummm gama Yayan naku ya zo,bari na baku wuri "ta faɗa tana hawa bene ba tare da ta ƙara juyowaba,
Dan rigima a maimakon tayi ɗakin ta sai shigewa ɗakin shi tayi ta kwanta saman dago tana juyi" Gaskiya wannan gadon yafi laushi,wancan sai saka ciyon baya,ai sai dai kayi haƙuri amma nan dakin zan dawo da kwana".
___ƙara daure fuska yayi wanda dama yake a cunkushe saboda rashin walwala,
Takowa yayi ya zauna a daya daga cikin kujerun,
Nan take suka shiga gaida shi,sai dai bai amsa masu ba sai kallon Aunty Hajjo da yayi"barka da Safiya"
Bata bashi amsa ba sai ma cikin ɓacin rai da tace"Abinda wannan yarinyar ta faɗa gaskiya ne?
Kauda kai yayi be bata amsa ba,to me zai ce mata a gaban kanne shi,
"Suraj tambayar ka fa nake yi,ni da nake son su Abba su huce a maida saka ranar ka da Maijiddarh,amma ji abinda yarinyar nan ke fada"
"Me zai hana ki bincike ta"yayi maganar kamar ba a bakin shi ya fito ba,
" Yaya"Amira ta kira sunan shi cikin jin haushi"dan Allah karka ja mana raini a wurin wannan yarinyar "
Wani mugun kallo ya watso mata"ita din Aunty ki ce idan har ni yayan ki ne,kar na kuma jin zancen rashin girmamawa daga gare ki"
Mikewa yayi yana dosar hanyar barin falon"bana son kananan magana "ya fada yana karasa faɗa.
Ajiyar zuciya ta sauke" Banga me zai hana na kyara ma yarinyar nan zama ba,ku tashi muje "
Haka suka bar gidan cikin bacin rai.
Sai zuwa ƙarfe biyu data gaji da kwanciya ta fito,shine ta kara cin karo da Akwatunan da suka kawo dazu,
Ɗauka tayi ta kai dakin shi ta jera sannan ta shiga budewa,ba laifi an zuba kaya sai dai ba masu irin tsadar nan ba,dan kudi Kaka taba Aunty Hajjo ta hado kayan saboda irin sana'ar da take yi kenan,shine ta zubo waɗannan,gabaɗaya kayan har akwatin idan aka duba kuɗin su basu wuce dubu dari bakwai ba
Karamin tsaki taja,ai ko dan kunnen da take sakawa yafi karfin gabaɗaya kayan balle yanzun data samu yancin akanda da take gidan su,dan haka yanzun sai abinda taga dama,
Daukar pant daya da Bran tayi sai doguwar riga da takalmi flart shoes ta saka,gyalen dan karamin Jallabiya data saka ta yane kanta dashi,
Dubawa tayi cikin kayan kwalli sai dai duk ciki ba kalan product din da take amfani dashi,dan haka man baki kawai ta shafa,ka karamin kyau kayan ya mata ba,dan kalar Ashe ne ma'ana ruwan toka.
Tana cikin fesa turare taji shigowar shi,sai dai bata juya ba dan tana iya ganin Reaction ɗin shi ta cikin madubi,
Murmushi ta saki tana juyowa cikin takun dai daya ta iso gaban shi "Mijina nayi ƙyau"
Ganin baida niyar kulata yasa ta ɗan bata rai "gaskiya Suraj idan ka bata fuska baka cika yin kyau sosai ba,ka dan dinga murmushi mana" Ta karasa faɗa da murmushi a fuskarta,
"What ar you doing? Ya tambaya yana karema dakin kallo harda gadon shi da ke hargize,
Itama bin dakin da kallo take bi" What? Ta maida masa tambayar shi,
Nuni yaimata da akwatunan dake jere da kuma gadon dake a yamutse har zanin gadon ya fado kasa,"what is the meaning of dose thing here?
Bata fuska tayi"ai gadon dakin can ne yake saka ciyon baya shi yasa na dawo nan,idan kuma kaima nan ɗin ta maka We can share this room,kaga sai mu dinga kwana tare akan nan zai fi armashi ko? Ta faɗa tana faɗaɗa fara'ar fuskarta,
Dafe Kwankwaso yayi yana ɗan furzar da murmushin takaici "what is your name ma