Showing 102001 words to 105000 words out of 159134 words
Chapter 35 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt
Baba da Mama,ni son tsakani da Allah na ke ma Yusuf kaka,ba wai soyayyar sha'awa bace ko ta wani abu,Allah ne ya Daura min,gashi ta sanadi na auren iyaye na yana ƙoƙarin rabuwa,idan har haka ya faru ba zan taɓa yafe ma kaina ba"
Ganin yanda take kuka ne yasa Aunty Hulaira ta jawota jikinta"ya isa haka ba laifin ki bane,haka Allah ya tsara kuma duk abinda Allah zai tsara mana zai same mu ba mu isa mu kauce masa ba,so wannan ma mu ɗauke shi a matsayin haka"ta faɗa tana share mata hawaye,
"Shi yasa na ga su yaya suna jin haushi na"
"Yo ba dole su ji haushin ki ba sun ga kina ƙoƙarin sakawa a saki Uwar su"
"Kaka dan Allah ki kyale yarinya ta huta kin ga ba lafiya ne da ita ba,"
Tabe baki tayi"ku dai kuka sani,
Wai ni kan Salamatu in tambaye ki?
Bata bata amsa ba sai ido data Daura mata wanda hakan ke nuna tana jinta,
"Shi wannan yaron da kika nace ma anya ba Asiri ya maki ba"
Aunty Hulaira ce tace "Asiri kuma Kaka?
" To ki duba ki ga,in ba aikin asiri ba ta yaya za'a yi ace yarinya ta bijirema kowa,bata jin shawaran kowa saboda shi,ki duba ki ga fa har auren uwarta take kokarin kashewa amma baki ji tace ta fasa ba,ko kin fasa?
Ta faɗa tana tambayar ta
Ita fa wannan tsohuwar mugun surunta ke sakawa bata son zuwa gidan,cikin jin haushi tace"ba Asiriba kome zaki ce ina son Yusuf kuma ba zan fasa ba,sai dai zan roki Baba Mama ta dawo"
"Wai shi din ma ɗan gidan uban waye ne?
Aunty Hulaira ce tace" A jiya dai Aunty Fatima ta ce min yaron aikin Baban ta ne,shi ya samar mai komai har ta gidan da suke ciki,to yanzun haka a jiya yace zai ɗibar mai kaso mai yawa a cikin dukiyar shi wanda zai dinga kula da ita Salmar"
Abin mamaki,sai gashi nan take kuwa tsohuwa ta shiga washe baki"ai to in haka ne kenen abun ma da sauƙi tunda ba cikin talauci da kunci zaku zauna ba,tunda mahaifin naki ya ji ya gani zai iya, to in banda ma abin Fatima me na tayar da hankali har haka,bari to zo ai kuwa yanzun zata tattara ta bar min gida"
Sallamah suka ji sannan lokaci ɗaya tana tambayar"wa zai bar gida?
"Ke mana,domin ni yanda kika min bayani ina daukar yaron matsiyaci ne ashe ubanta yace zai masu komai"
Ita ba ta san sai yaushe bane idanun Kaka zasu dawo dai-dai akan kuɗi,gabaɗaya rayuwar ta idan kana son faranta mata to ka dauko harkar Arziki,duk har da saboda wannan shegen son kudin nata ta jefa ta cikin wannan yanayin da take ciki,
Mai da kallon ta kan Salma tayi"bi yo ni"
Tashi tayi tabi bayan ta zuwa ɗakin kaka data shiga.
Tana zaune kan gado,nuna mata kusa da ita tayi alamun ta zauna a wurin,
Zama tayi tana kallon fuskar mahaifiyar nata wanda a ɗan tsakanin kwana biyun nan ta rame sosai,sai dai ita bata lura ba sai yanzun,
"Ummu Salma" Ta kira sunan ta,
Kanta a duke ta amsa da "na'am" Domin kunyar haɗa ido take da ita,saboda gashi saboda ita auren ta na ƙoƙarin mutuwa,
"Dado kanki ki kalle ni"
Girgiza kai tayi hawaye na kara sauko mata"Mama dan Allah ki yi hakuri,ban San abinda ya faru tsakanin da Baba kenen ba saboda ni"
"Koma me ya faru dani wannan ba damuwarki bane,tsanina dashi ne,ni tambaya nake son na maki wanda zai kasance tambaya ce ta ƙarshe tsakanina dake a kan Yusuf"
Dagowa tayi tana kallon mahaifiyar nata,
Jinjina mata kai tayi"Ummu Salma"ta kira sunan ta a natse
Sai dai bata iya amsawa ba saboda yanda zuciyarta ke bugawa dan bata San wani irin tambaya mahaifiyar nata zata mata ba,
"A yau kina da damar da zaki sauya Kaddaranki,ki sauya rayuwar ki gabaɗaya,idan har zaki jure ma zuciyar ki kibar zabin ranki,ki dauki dayan ɓangaren," Ta faɗa tana kallon ta,
Ganin har ƴan mintuna sun shuɗe ne yasa tace"kina ji a ranki kin zabi Yusuf kenan?
Nan ma shiru tayi,
"Ki faɗa min abinda ke ranki Salma ba zan maki dole ba,kuma na maki alkawarin duk hukuncin da kika yanke a wannan lokacin to na karɓa"
"Mama kiyi haƙuri har yanzun na kasa cire shi a raina"
Nan take wani hawaye mai matuƙar zafi ta sauko daga cikin idanun nata,yayin da ta ji zuciyarta ya mata nauyi Kamar an daura dutse,
Cikin sauri ta dafa hannun ta"Mama kuka kike yi dan na zaɓe Yusuf,Mama k.....
Yatsa ta saka mata a baki alamun tayi shiru,tana girgiza mata kai,"Salma sai yau na tabbatar da Allah baka taɓa mashi wayau ko dubara,na yarda da hakan tunda gashi tsayin shekaru muna ta kokarin keɓe ku daga irin wannan amma sai gashi sai da Allah ya jarabcemu ta hanyar da bamu yi tsammani ba,"
"To Mama me yasa kike kuka?
" Ba zaki taɓa gane me yasa nake kuka ba Salma sai nan da lokaci mai karasowa,domin kuwa lokacin yazo,karasowa kawai ya rage,lokacin zaki fahimci abinda nake maki gudu,lokacin zaki fahimci illar hanyar da kika zaɓa,yayin da babu hanyar juyawa baya,kuma babu Alkalamin da zai goge haka daga cikin rayuwar ki da ƙwaƙwalwar ki,abinda nake ma gudu kenan Salma,ranar da zaki kasa jurewa,ina matukar tsoron amsar da zan baki,shi yasa tun kina da sauran dama nake roƙon ki daki janye batun wannan yaron"
Ganin irin yanda mahaifiyar nata ke hawaye wanda ke nuna asalin tsoron ta ne yasa ita ma nata hawayen kara yin yawa"Mama ki yi haƙuri "
Shafa kanta tayi"Allah ya maki Albarka,ya baki haƙuri da juriya a duk halin da kika tsinci kanki"
"Amin Mama"
"Shi kenan tashi mu koma gida,dama nayi magana da Baban ku ko"
"Da gaske zaki koma me Mama?
Dan dakatawa tayi tana share fuskarta" Eh,"
Rungume mahaifiyar nata tayi tana dariyar farin ciki,
Suna fitowa bata ko kalli in da kakar nata ke zaune ba ta saka kai zata fita,ji tayi tana faɗin "A sauka lafiya,Uwar soyayya"
Dan juyowa tayi kaɗan tana dariya kafin ta ƙarasa fita daga gidan,
Direban daya kawo ta shi ya mai da su gida,
Tun daga lokacin basu kara tayar mata da zancen shi Yusuf ba,sai dai sun sake mata fuska sun koma tamkar babu abinda ya faru,Baba kawai ke sanar da ita cewar sun yi magana da iyayen Yusuf sati mai zuwa za'a daura auren su,washegari kuma zasu tafi London din tare,
Ranar farin ciki kamar zai sheketa,ƴan uwanta sun tayata murnar samun muradin zuciyar ta,amma Mama ko kallon in da suke bata yi ba,kuma har ya kasance yau da ya rage saura kwana uku ɗaurin aure Mama bata ce mata komai ba dan gane da gyaran jikin amare da ake yi,
Aunty Hulaira ce ma ta kira ta take ce mata ko an gama bata magungunan mata data karbo kuwa,
Tace ita ba abinda aka bata,in ba maganin sanyi ba da Mama ta bata,
Taga bacin rai sosai a fuskar kanwar Maman nata,dan haka bin bayanta tayi ta tsaya a ƙofa bata shiga ba ganin yanda ita Aunty Hulaira ta shiga dakin Mama a hassale,
Tana ji take tambayar Mama"Aunty Fatima ina maganin dana siya ki ba Salma"
"Wani magani? Ta tambaya,
" Na kayan mata"
"Oh yana nan"
"Me kike nufi da yana nan,kin san irin kudin dana kashe domin hado waɗannan magungunan kuwa,sannan ace yarinya biki har saura kwana uku ba'a fara bata komai ba,haba sai kace wacce ba tada gata,ke in ba zaki bata ba Bani su nan na fara bata"
Girgiza kai tayi"shi yasa tun farko na ce maki karki siya,amma baki karɓi shawarata ba,Salma ba zata sha wannan maganin ba"
Katse ta tayi"zata sha mana domin abune da zai taimaka wurin ɗaga darajar mace"
"Ba zaki gane me nake nufi bane Hulaira,Salma bata dace da shan maganin mata ba,domin idan har tasha ina mai tabbatar maki za'a samu babban matsala irin wanda bana fata,ko yanzun ya ta kare,da kanta fa take sanar da ni irin karfin sha'awar da take dashi,to ina ga tasha wani kayan mata,"
"To ai hakan abu mai kyau ne,kin ga su sabbin aure ne,sannan suma mazan yanzun ba haka suke zama ba,idan tasha sai kiga komai yazo masu yanda ya dace"
Dafe goshinta tayi,domin ta tabbatar idan zata kwana yi masu bayani ba fahimtar ta zasu yi ba,"na maki alƙawarin idan aka kaita ɗakinta da sati biyu ba tare da an samu wani matsala ba to da kaina zan kai mata kayan matar har inda take,na maki alkawari amma dan Allah karki kuma cewa komai "ta faɗa da alamun roƙo,
Ajiyar zuciya ta sauke mai ƙarfi" Shikenan ba damuwa na yarda dake,sai dai dan Allah Aunty Fatima ki cire komai a ranki dangane da wannan aure kawai ki masu fatan zaman lafiya,da samun ya'ya na gari"
Maganar ta na karshe ne ya sata ɗan yin murmushin takaici "Ya'ya,Umm,to!Allah ya basu masu Albarka"
"Yauwa ko kefa,Amin"
Da hakan zancen ka kare suka dauko wani hira,
Ita kuma juyawa tayi ta wuce tana tunanin dalilin da zai hana Mana bata maganin yanzun har sai nan da sati biyu wai kuma shima in ba matsala,Umm ta rike maganin ta domin ita kam tuni suka yi ciniki da wata mata a online mai sai da kayan mata yau kuma kayan zai iso tun daga Sokoto,in ita ba zata gyarata ba ai Gara ta gyara kanta.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*63*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Duk wannan haukar da take yi tun daga farko har zuwa yau da yake ɗaurin auren ta basu taɓa yin waya da Yusuf ba,komai Baba ke mata,dan haka ita abun be dameta ba,
Ranar Sati da misalin karfe goma na safe aka ɗaura auren,wanda ya samu halarta manyan mutane daga wurare daban-daban,domin a garin Minna mahaifinta ba ɓoyayyen mutum bane,
Kasancewa yanda auren yazo da kuma yanda yan uwan basu so yasa ba'a yi wani program ba,sai gagarumin Dinner da Baba ta shirya masu a Lebo Kutigi,da karfe takwas na dare,
To fa shine suka haɗu a cikin motar da aka shigo ɗaukarta dashi da zasu tafi wurin Dinner,
Tayi shiga na Alfarma,tayi kyau na ban mamaki,yanda kasan ba a kasar Nijeriya ba,kasancewar ta Fara tas,yayin da kayan dake jikinta na doguwar riga ya kasance ruwar toka mai haɗe da dan karamin hijabi,shima Kot ne a jikin shi ruwan toka,
Tunda aka buɗe mata marfin mota ta shiga aka maida aka kulle,ta juyo tana fuskantar shi,domin bata San da wani irin fuska zai tarbe ta ba,
Shima ita yake kallo kamar mai nazarin wani abu,kafin kuma lokaci guda ya sakar mata da murmushi,ya mika mata hannun shi alamun ta riƙe,
Wani irin ɓoyayyen ajiyar zuciya ta sauke tana daura hannun ta a saman nashi,
"Kin yi kyau sosai Beauty"
Juya idanun ta tayi cikin tsananin farin ciki tace"na ɗauka ba zan samu irin wannan tarbar daga gareka ba"
Sumbatar hannun ta yayi "nariga nama Mahaifinki Alkawarin zan kula dake na mai dake gimbiya a gida na"
"Kana nufin Baba?
" Eh Baban mu,Kin San yanzun ya zama namu har da ni"
Dariya ta saki cikin jin daɗi,
Da haka suka isa wurin Dinner aka gudanar da komai cikin kwanciyar hankali da wadata,aka kuma rabu cikin Arziki,yayin da suka yi sallamah da mutane da dama domin gobe da safe ƙarfe takwas jirginsu zai tashi zuwa London.
Sai da ya ajiye ta a gida sannan shi kuma direba ya mai da shi gida,
Har ta yi wanka ta kwanta dan lokacin ƙarfe sha-biyu na dare ake nima sai gashi ta ji an turo kifar dakin ta,
Daga kai tayi ta kalle ta,ganin wacce ta shigo ne yasa ta mike zaune tana kiran sunan ta"Mama"
Dan murmushin yake ta sakar mata tana zama kusa da ita,
Kallon mahaifiyar nata tayi yanda idanun ta suka kumbura alamun ta ci kuka,to ko ita da take amarya ta lura ba tayi kuka ba kamar yanda Mama tayi,
Shafa kanta tayi"ba kiyi barci ba?
"Tanzun na fito wanka shi ne na kwanta"
"How was the party?
Murmushi ta saki" Komai ya tafi dai-dai "
"That good"
Dan shiru sukayi na dan lokaci,kafin ta katse shi tun da faɗin "gobe d safe zaku tafi"
"Eh haka Baba yace"
Ajiyar zuciya ta sauke a karo na ba adadi "Nasan ba lallai bane gobe na samu lokacin da zamu yi magana shi yasa na shigo yanzun dak da Nasan kin gaji"
Girgiza kai tayi "is ok Mama ina ji"
Lumshe ido tayi ta bude kafin ta fara da kiran sunan ta,"Ummu Salma"
Kasa amsawa tayi sai zuba ma Mama ido da tayi
"Ina son a ko wani lokaci ki dinga tunawa kina da Mahaifiya mai ƙaunar ki,da yanni maza masu son ki,kina da Ahali masu matukar kaunar ki,ko me zai faru dake ki dinga tunawa dasu kuma zasu tsaya maki a ko wani hali,idan har kina niman wanda zaki fadama damuwarki ni mahaifiyar ki ina nan,zan saurareki na kuma baki mafita,"
"Mama wani abun zai faru ne?ta tambaya cikin dan yanayi na tsoro,
Rike hannayen ta tayi" Babu abinda zai faru,kawai dai ina faɗa maki ne saboda karki manta damu,
Abu na gaba,shine mai muhimmanci,Salma banda bincikan mijiki,karki cika bincike akan lamuran shi,ki yi hakuri da duk abinda kika gani domin ke kika zaɓa,kuma dauriya da juriya da dauke kai ya zama dole a gare ki,a duk lokacin da kika ji zuciyar ki na rayo maki wasu abubuwa ki yi sauri ki kama kiran sunan Allah domin shi kaɗai ne zai taimake mu,"
Shiru kawai tayi tana sauraren wannan nasiha na Mama wanda kwata_kwata bata gane kanshi ba,bata gane in da ta dosa ba,ita a nata tunanin nasiha ya kamata ta mata akan yanda zata kula da tsafta da girki da kuma kyaran jiki ta yanda zata rinka dauke hankali mijinta,sai gashi tana mata Nasiha kamar wacce zata shiga rayuwar kunci,
Ganin irin kallon da ƴar nata ke mata ne yasa ta kuma shafa kanta"na San yanzun baki gane mai nake nufi ba,amma a hankali zaki gane,ki kwanta ki huta sai da safe"ta faɗa tana sumbatar ta agoshi,
"Ok Ma," Ta faɗa tana gyara kwanciyar ta yayin da Mama ta kashe mata wutar dakin ta fita.
Washegari suna idar da sallar Asuba Baba ya haɗa su daku har da yannin ta ya masu nasiha akan su rike zumunci,su haɗa kan Ya'yan su,koda yana da rai ko beda rai,
Kallon Salma yayi cikin zolaya yake faɗin "Gimbiya idan kin haihu wani suna zaki saka ma ɗan ki"
Dariya tayi tana juya ido"Baba idan na haifi ɗa namiji zan saka masa sunan Muhammad,saboda sunan Manzon Allah,kuma suna yana tasiri sosai akan yaro "
"Laa to ba zaki saka suna na ba"
Da sauri Mama tace"A'a tunda har suna na tasiri akan yaro ai Gara dai Muhammad ɗin,"
"Mama to ai sunan Baba ma yana da kyau,tunda shima sunan ɗan Manzon Allah gare shi,Abdullahi"
Girgiza kai tayi tana canja zancen"to idan mace ce fa"ta tambaye ta,
"Umm,to zan saka mata Nana Habiba,ina son sunan sosai"
"Sai na kira ta da BIBA"
Dukan wasa takai masa"kai Yaya Abdulmajid me kuma Biba,ni Nana Habiba nace "
"Kunga ni idan na yi aure sunan Mama da Baba zan saka ma yara na"
"A'a,bamu bukatar haka,kawai ku saka masu wani sunan amma ba namu ba"
Bata fuska yayi"Mama"
Murmushi tayi"eh"kallon Baba tayi daya zuba mata ido,domin shi ya fahimci inda zancen ta ya dosa,sai dai su yaran ba zasu taɓa ganewaba,sai dai ko kaɗan bai ga laifin ta ba,ƙoƙari take a matsayinta na uwa taga ta inganta rayuwar ahalinta,"ko ba haka ba Baban su? Ta faɗa tana tsare shi da ido,
Jinjina kai yayi"no need,kawai kome kuka haifa Allah ya albarkaci rayuwar su "
Da Amin suka amsa,
Daganan tashi sukayi domin su yi wanka su shirya su rakata filin jirgi,
Zuwa ƙarfe bakwai da rabi suka baro gida gabaɗayan su,har da Mama da Baba,dasu Aunty Hulaira yan rakiya,
A can suka sami Yusuf da ƴan uwan shi suna jiran isowar su,
Gaisawa suka yi cikin mutunci sannan Yaya Abdulrahman ya amsa Tikitin su ya shiga gudanar masu da komai har zuwa lokacin da jirgin su zai tashi,
A lokacin da zata wuce bata wani damu ba,sai lokacin data kalli idon yannin ta sannan ta fara hawaye,domin tasan zata yi kewar su,sai dai in sun kawo mata ziyara,amma ita da dawowa sai nan da shekara biyu idan ta kammala karatun ta,
Komawa baya tayi ta rungume su daya bayan daya tana,a kan Abdulmajid ta tsaya tana rike da hannun shi"Yaya kayi haƙuri "
Shima share hawayen shi yayi "we are all with you"
Rungume shi ta kuma yi"na gode "
Shafa kanta yayi"Allah ya albarkaci rayuwar auren ki"
Da Amin ta amsa ta kara rungume Aunty Hulaira da Mama har ma da Baba,kafin su shiga inda Asalin zasu shiga jirgi yayinda Yusuf ke rike da hannun ta,*Ban sani ba sallamar da nayi dasu a wannan lokacin na haɗa ne gabaɗaya har da farin cikina na bar masu a nan,yayin da na fara taka matakalar jirgi haɗe da wani mataki na littafin ƙaddaran rayuwata,tun daga wannan lokacin da ba zan taɓa mantawa da shi ba komai ya fara juyawa,a ranar Lahadi ƙarfe takwas daidai,*
Kujerana na kusa da nashi ne,dan haka hannun mu na cikin na juna domin shi wannan ne karo na farko daya taɓa shiga jirgi,ni kuma ba zan ma iya tuna adadin sau nawa na shiga ba,
A haka har jirgin mu ya sauka a birnin London.
Address din da Baba ya bani dashi nayi amfani na tare Taxi na faɗa masa ya kaimu,duk wannan abin yana riƙe da hannu na,saboda shi baisan gari ba,kuma zuwan shi na farko kenan wannan ƙasar,
Har bakin tangamemen Apartment din mu aka sauke mu,wuri ne ba kaɗan ba,dan gidan zai tasarma hawa goma sha biyar,dan lambar dakin mu shine na dari da goma sha uku,muna hawa na tara ne,
Dan Linta mukayi amfani zuwa sama,in da ƙofofi ne a jere wasu na