Showing 51001 words to 54000 words out of 159134 words

Chapter 18 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt

27 Sep 2025

9756

faɗin "An ɗaura,An ɗaura"

Maida kanta tayi ta haɗa da gwiwar ta tana karanto duk wani Addu'a da yazo bakin ta,jin irin yanda gabanta ke tsananin faɗuwa,abubuwan da suka faru da ita a baya suna ƙoƙarin dawo mata sabo a cikin ƙwaƙwalwar ta.

__________Acan waje kuwa wurin ɗaurin aure..



🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*33*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*


A masallaci tun ganin lokacin kiran sallah ya kusa Abbu ya kira shi a waya,
Yana ɗauka yace"sai na tuna maka da batun ɗaurin aure "

Cikin sanyi murya yace"zan zo yanzun nan Abbu"

Ba tare da yace komai ba kuma ya kashe wayar,duk da yanda yaji muryar shi wani iri abin ya ɗan taɓa zuciyar shi,dan daga dukkan alamu kamar bai da lafiya,yana son Suraj sosai,domin yaro ne mai matukar biyayya,tunda suke dashi bai taɓa saɓa ma umurnin shi ba,ko yaci masa musu akan wani,kawai dai yau he is very disappointed akan abinda ya aikata,kuma dole ne sai ya nuna mai kuskuren shi a kan haka.

Kallon Farhan yayi dake ƙoƙarin cire mashi Drip,"ka fitar min da kayan da zan saka"

"An gama ran Ango ya daɗe"

Ba tare da yace mai komai ba ya tashi ya shiga banɗaki dan yayi wanka,yana gamawa ya dauro Alwallah gabaɗaya sannan ya fito,

Kujeran madubi ya ja ya zauna dan baya jin karfin jikin shi,mai ya shafa kawai sai turaren da ya feshe jikinsa dashi,
Kallon kayan dake ajiye saman gado yayi,ƙaramin tsaki yaja sannan ya buɗe durowa ta jawo wani farin Jallabi da farin hula ya saka,sai wani dan karamin Carbi daya riƙe a hannun shi,
Tsarki ya tabbata ga Allah,domin yanda kasan wani Balarabe haka ya fito,
Tunda yake saukowa daga sama ya buɗe baki yana kallon shi cikin mamaki,ganin yana ƙoƙarin wucewa ba tare da yace mai komai bane yasa da sauri ya tashi ya bi bayan shi "me haka zan gani Suraj,ina kayan dana fito maka dashi?

"Basu min ba" Ya bashi amsa a takaice,

Nuna shi yayi"ta ya za'a yi kaje ɗaurin auren ka da wannan kayan sai kace mai shirin zuwa bada sallah"

Buɗe mota tayi ya zauna a gidan baya ya jawo kofa ya kulle,

"To waye zai ja motar ba dai ni ba,ina matsayin abokin ango"

Ba tare da yace mai komai ba ya buɗe motar ya fito,kai tsaye motar Farhan dake parke a gefe ya kuma buɗe gidan baya ya shige,

Dafe kai yayi yana kallon motar,shi dai duk yanda kayi dashi sai ya bullo maka ta wata hanyar,
Buɗe wurin zaman direba yayi ya zauna ya ja motar yana gunguni,

Lumshe idanun shi yayi yana jin zuciyar shi na faman yi mashi zafi,har ɓalle idan ya tuna da ita da kuma abinda ta mai,idan har yarinya is capable of doing something like that,to me ne ba zata iya aikatawa ba,wama ya sani ko maza nawa ta haɗa baki dasu irin haka,
Tuna hakan kuma da yayi ne yasa yaji zuciyar sa na tashi sosai,da sauri ya dafa Farhan "tsaya"

Dan juyowa yayi"me kace"
"Ka tsayar da mota"
Samun gefen hanya yayi ya parker,
Da sauri ya fito ya tsaya a gefe ya shiga Kwara Amai,
Sai abun yayi kamar zai tsaya,amma da yayi tunanin Kiss din,nan take Aman ke dawowa har ta hanci yi yake yi,
Shi kanshi Farhan abin ya fara damun shi,goran ruwa ya dauko masa ya kuskure baki tare da wanke fuska,sannan ya taimaka masa ya shiga mota,
Kallon shi yayi zazzaɓin ƴan awoyi amma duk ya fada,fuskar shi yayi ja idan ka sanshi to zaka shaida bai da lafiya dan ko a muryarsa kana iya shaida hakan
"Muje Asibiti?

Jirjiza kai yayi kaɗan yana lumshe ido,

" Jikin ka ba ƙarfi,kana bukatar Medical attention "

"Kai ni masallaci"

Yana ƙoƙarin kara yin magana ne wayarsa da ke ta kara tun dazu bai sani ba ya kara daukar kara,
Kallon wayar yake yi da sunan Ammi ya fito baro_baro,
Sai da yaja numfashi ya busar yana kauda kai kamar ba zai ɗauka ba sannan ya danna wurin amsawa,
Sallamah tayi ya amsa "kazo ina son ganin ka"

"Idan an fito masallaci zan shigo"

"Ok"
Kashe wayar kawai yayi,
Suna isa lokacin har an fara kiraye-kirayen sallah,mutane nata Daura Alwallah,dan haka masallaci suka shiga,kusa da Abbu dake jan carbi ya samu wuri ya zauna kafin a tayar da sallar,
Abbu ya bada sallah har aka idar,bayan Addu'o'i ne ya sanar da daurin aure,kafin aka shiga fitowa da kwandunan goro Sweet da Dabino,
Kowa mamaki ya shiga yi irin wannan daurin aure na Ustaz Suraj,kafin kace me nan take mutanen da suka hallaci sallah a wannan masallacin sun fara Daura magana a social media,cikin kankanin lokaci magana ya zagaye gari wasu su ƙaryata wasu kuma su yarda,
Ana gama daurin aure dady ya dafa Kafadarsa ba tare da yace komai ba ya fita daga masallacin,
Ganin Abbu na magana da mutane yasa ya zame jiki ya bar masallacin ba tare da ya koma ko takan Farhan ba yayi shigewar shi cikin gida,
A hankali yake takawo hannun shi dafe da kanshi dake matukar Sara mashi,
Ji yayi an riƙo shi ta baya wanda hakan ne yasa ya juyo "me yasa zaka amince ka aure ta bayan kasan ina sonta,me yasa zaka dinga cin amana ta ka zagaya kana bata mata rayuwa,sam bata dace da mutum irin ka ba,ba zan kyale ka ba,sai na saka ka sake ta da bakin ka na aure ta"
Ganin bai da niyar ce masa komai ne yasa cikin jin haushi kuma ya sake shi ya wuce,

Shi bai ma sani ba idan da akwai ta yanda zai juya komai da ba'a kawo wannan matakin ba,duk da kalaman Nurudeen ɗin ya bashi mamaki jin yana sonta,karamin tsaki yaja kawai tare da nufar shiyan Ammi,

Zama yayi kawai a kan kushin yana jan carbi ba tare da ya shiga ciki ba,

Amira ce ta fito ta ganshi nan zaune,
Kasancewar taga idanun shi a rufe ne yasa ta koma dakin Ammi ta faɗa mata isowar shi,cewa tayi tace ya shigo,
Tana fitowa zama tayi kusa dashi"yaya"ta kira sunan shi,

Buɗe idanun shi yayi wanda har yanzun suke a firgice ya daura a kanta ba tare da yace mata ko mai ba,

"Da gaske ka auri Biba,an daura maka aure da ita yanxun kamar yanda naji a masallaci?

" Ummm "ya bata amsa a takaice,

Bata fuska tayi tana bata rai" Dama Aunty Maijiddarh ce,yaya Biba fa yar aiki ce ba tayi koda karatun Boko ba,amma Aunty Maijiddarh tayi Degree a bangaren Arabic,gata wayayyiya,amma wannan ko baki kayi ta yaya zata fitar da kai kunya,bana tunanin ma ta iya koda karatun sallah ne,ku malamai wani lokaci ana gaiyatar wurin walima ko wa'azi tare da matan ku,ko kuma su a gaiyace matan naku,gata baƙauyiya ko saka kaya bata iya ba,kalli ma wasu irin manyan kayan da take sakawa kamar wata Goggo,kai kuma duk da kana malami amma kai ɗan zamani ne,ɗan Gaye,gaskiya ni dai yaya an cuce ka sam baku dace ba,bata min ba"

Yasan duk abinda ta faɗa gaskiya ne,duk da akwai wata a kasa tsakanin shi da yarinyar ba haka bane zai sa ya bada kofar da ƙannen sa zasu wani samu dama a gare shi"ita din Aunty kice ki dai na fadar haka a kanta"

Buɗe baki tayi"Aunty kuma?Allah y.....

Katseta yayi"ina Ammi?

Tsabar takaicin rashin bata amsa da baiyi ba yasa da hannu kawai ta mai nuni da hanyar dakin Ammi,
Bai ce mata komai ba shima ya Mike ya wacewar shi ɗakin,

Da sallamah ya shiga,tana zaune saman darduma ta amsa mashi,
Shigowa yayi ya zauna dan nisa da ita kaɗan yana tankwashe kafa,
Da hannu ta mai alama da ya matso,
Matsowa yayi zuwa in da take,
Tsira mashi ido tayi na wasu ƴan sakanni,yayin da kanshi ke duke,
Hannun ta daya ta daura saman fuskar shi "are you ok?

Jinjina kai yayi" I am fine"

"But you are not"

Dan murmushi ya kakaro "I will be ok in time"

Ajiyar zuciya ta sauke"kayi haƙuri wannan ne kawai mafita"

"I hate it"

"Ni ma haka,sai dai at this stage dole ita kadai zata iya tunda ita ta fara,we have to Trust her,we have no option,you have to endure it,can you do it for me? Ta faɗa idanun ta na cika da hawaye,

Hannun ta dake saman fuskar shi ya rike ya sumbata" Insha Allah,for you and grandma"

"Thank you and im Sorry it all my fault from the beginning"ta faɗa hawaye na ƙara bin fuskarta,

Rungume ta yayi " Haka Allah ya tsara tun farko,ke ma ba yin kanki bane,ya kamata ki bar faɗin haka a yanzun"

"Har sai ranar da komai ya zo karshe sannan zan huta"

"Komai ya kusa zuwa insha Allah"

"Ya kamata ka tafi Asibiti tare da Farhan"

"Na ji sauƙi"

Girgiza kai tayi"ka kula da kanka shine abu mai muhimmanci"

"Zan kula Ammi,"ya faɗa yana ƙoƙarin mikewa,

" A ina zaku zauna?

"Sai yanda su Abbu suka tsara"ya fada yana mata sallamah tare da barin dakin cike da tunanin me zai je ya tarar dakin Kaka.

🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*34*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*

Bakin shi dauke da sallamah ya shiga falon bayan sun amsa mai,

Sai da ya zauna kusa da Kaka sannan ya gaishe su,amsawa suka yi ba cikin walwala ba,shiru yayi kawai kanshi a duke ba tare da ya kuma cewa komai ba,

Abbu ne ta kalli sauran mutanen dake falon,sannan ya ce"Alhamdulillah Allah mun gode maka daka tsara mana wannan ranar a haka,ina fata wannan ya zamo izina a sauran yaran gida,me kokarin aikata irin wannan kuskuren sai ya kiyaye ya kuma san me zai iya faruwa dashi,kai kuma Suraj mun maka haka ne bawai dan ba musanka ba,sai dan muna son kare mutuncin ka dana wannan gidan shi yasa,sannan iyayen ita yarinya sun zo kuma an daura aure cikin mutunci dan haka dole mu gode ma Allah "

Duk jinjina kai suka yi cikin gamsuwa da maganar shi,
Dady ne yace"to yanzun ina zai zauna da matarshi "

Goggo ce ta amshe maganar da faɗin "me kuma zasu zauna su yi mana a gida?ai shi yanzun ba ƙaramin yaro bane tunda har yasan ya saka mace a ɗaki,dan haka ya tattarata suje can gidan shi su karata tunda Allah ya hore mashi,mu kuma ya bar mu muci gaba daba ya'yan mu tarbiyya yanda ya kamata"

"Sosai ma maganar ki gaskiya ce,ni yanzun gashi can an bar yata da jinyar zuciya,dan haka abun ya isa haka,muma a ba ya'yan mu wuri su sha iska"cewar Hajiya Saudat,

Abba Mustapha da tunda suke magana bai saka masu baki ba, yadan yi kyaran murya,kiran sunan shi yayi wanda hakan ne yasa kowa yayi shiru yana jira yaji me zai ce "Suraj"

Dago kanshi dake duke yayi ya amsa a hankali "Na'am Abba"

"Shin ko Kanada abun faɗa"

"A'a Abba"

"A kan hukuncin da muka ɗauka fa,shin baka ganin bamu maka adalci ba,gashi ko dangin mahaifinka bamu ni ma ba"
Dan guntun murmushi ya saki wanda ya ɓoye sirrin dake ranshi,tare da raunin shi,"ku din ma iyaye na ne,duk hukunci da kuka yanke zan karbe sa hannu biyu"

"Na gode da girmamamu da ka yi,yanzun ka ɗauki matarka ka tafi da ita gidan ka,idan akwai abunda kake buƙata ka kirani ka sanar da ni"

Mikewa yayi,domin dama dauriya ce kawai yake yi,"na gode Abba "sallah ya masu sannan ya fita,

Kallon sauran yaran dake falon yayi" Ku tashi ku tafi na sallame ku"

Duk tashi sukayi suka fita kowa da kalan abunda yake sakawa a zuciyar shi,

Kallon Abbu Sufyan yayi"dazu banji daɗin kalamanka ba sam Sufyan,kai a matsayin uba kake a wajen shi,shi kuma yana maka kallon mahaifi,amma ka bari bacin rai ya rinjaye ka,ka faɗa maganar da sam bata dace da bakin ka ba,ka kushe shi da zuri'ar shi,ka aibantashi a gaban ɗan ka,yayin dashi kuma ka yabe shi da kasancewar shi jinin ka,karka manta ko kai bakafi karfin Allah ya jarabceka ka,ina so kuma ka tuna waye Mahaifin Suraj wacece Kakar shi da kuka kira da jikin yahudawa,kai kanka kasan waye ita,idan da Ace tana kusa,wane kai Sufyan,sai dai kawai kaci Albarkacin Auren mahaifiyar jikanta,Kaka kema kin sani,amma ɗan ƙaramin kuskure ba tare da dogon bincike ba idanun ku sun rufe,a gaskiya kun ban kunya,ba kaɗan ba,ban taba tsammanin a gaban mahaifiyar yaron zaku iya fadar haka ba tamkar ku kuke taimaka mata kamar ta dogara daku,bayan a ko wani lokaci idan taga dama tana iya rabuwa da nan ɗin,idan kana taƙama aƙwai yarinya a tsakanin ku,to kamin ta same ta sai da ta sami wanin ta,"mikewa yayi"ni na tafi sai da safen ku,yauwa kaka ki saka ta fito tabi mijinta dare na yi dan na lura kamar ma ba lafiya gare shi ba"yana fama fadar haka ya fita ya bar su nan zaune cikin tarin nazari,

Kaka ce tayi kiran sunan Nafisa dake dakin kakan tana kyara mata wurin kwanciya,
Cikin sauri ta zo ta tsugunna "ki ce ma Habiba ta fito mijinta na jiranta"

"To kaka"

Ajiyar zuciya Abbu Sufyan sa sauke tare da mikewa "Mama sai da safe"

"Allah ya tashemu lafiya"
Tare da Dady suka fita kowa yayi nashi shiyan,

Kai tsaye dakin ta ya nufa bakin shi dauke da sallamah,
Har yanzun a zaune take saman darduma sai dai ba komai take yi ba,daga dukkan alamu nazari wani abu take yi,
Zama yayi kusa da ita ya yaro hannun ta,
Murmushi ta sakar mai kamar babu komai a zuciyar ta,"barka da shigowa"

Bai iya bata amsa ba sai dukar da kai da yayi yana tunanin ta ina zai fara"kiyi haƙuri"

"Akan me?ta tambaye shi,

Jin abinda tace ne yasa ya dago kai" Dan Allah kiyi haƙuri akan abunda ya faru dazu,bai kamata na faɗa abinda na faɗa ba"

Girgiza mai kai ta yi,fuskarta a sake tana Daura hannun ta saman nashi,cikin tabbatarwa wanda ya hakan ke sashi shiga shakku tace"A'a,ya ya wuce,ba kayi kuma ko wani kuskure ba,ka tunatar dashi ne matsayin shi a gareka,ba kayi kuskure ba is normal thing"

Baki ya buɗe yana ƙoƙarin yin magana ta sanya mashi yatsanta a baki alamun yayi shiru "karka damu da sai ka ban haƙuri,wallahi har cikin raina ban rike ba,kuma na gode maka a bisa haƙuri da kayi dashi na tsayin shekaru har izuwa yau daka aurar dashi,na kuma gode da kuka bashi damar matsawa ko zai kara fahimtar rayuwa,domin yanzun shi ba yaro ba ne,na gode"

Rungume ta yayi a jikin shi,sai yanzun yake ainahin danasani akan kalamansa na dazu,yaso ta nuna bacin ranta ta yanda zai bata haƙuri a wuce wurin,amma sai gashi ita ke bashi haƙuri ta bar shi da nauyin zuciya,
"Ki bani dama ta ƙarshe"

"Har abada ni matar ce idan ba ka yanke Alakar dake tsakanin mu ba,da kanka,ka kwantar da hankali ka har yanzun kallon uba yake maka"

Babu yanda ya iya da ita amma She make him fill guilty,in sha Allah da kanshi zai gyara abinda yake ƙoƙarin batawa.

*_________* tana zaune kan gado bayan ta gama sauraren duk bayanin da suka tattauna a kai sa ga Nafisa ta shigo,
Kallo take kare mata daga sama har kasa "Masha Allah Biba,yanda kikasan kamar ba ke ba,gaskiya ke yar sa'a ce gashi daga zuwa aikin kin yi ram da daya daga cikin yaran gida,dan Allah ni ma ki ban sirrin" Ta faɗa fuskarta dauke da farin ciki,

"Wai ba cewa akayi ki kira ni ba?

" Umm haka ne,kin ga taso Angon ki na waje yana jiran ki,"

Ganin ta taso tana kokarin fita ne yasa ta jawota baya"ke tsaya ba haka ake yi ba"Mayafinta dake a kafadarta ta dauka ta yafa mata a kai ta sauko dashi far ya rufe rabin fuska,"wai ina Maman ki da yar uwarta?

"Sun wuce"

Dan budo ido yayi"ta yaya zasu wuce basu tsaya sun kai ki ba?

"Mu a garin mu Ango shi kaɗai yake tafiya da Amaryarsa ba tare da kowa ba,"

"Wow gaskiya abun yayi kyau,to amma ni dai muje sai na rakaki har bakin mota"

"Aukuwa na gode muje"
Tare suka fito,
Wurin Kaka ta tsugunna tana mata sallamah"karki damu mun riga munyi magana da ƴan uwan ki kuma sun faɗa mana Al'adun ku,shi yasa na ce ki fito ki bin angon ki,sannan batun kayan sawarki na ba Teloli su uku domin ayi saurin haɗawa zuwa gobe,in sha Allah za'a kawo maki kayan Lefen ki"

Nan ma godiya tayi mata,

"Tashi kije yana jira Allah ya baku zaman lafiya da zuri'a ta gari"

Wannan karon kam bata ce Amin ba dan bata buƙatar ko fatan haɗa zuri'a da shi,dan ba wannan bane a gabanta,

"Kaka bari na raka ta wurin mota sai na nawo"

"To hakan ma yayi"

Tashi suka yi suka fita tana riƙe da hannun ta "Biba dan Allah duk dadin da kika samu karki manta da ni,tunda yanzun kin zama matar manya"

"Dan Allah karki dame ni da wannan maganar sai kace wacce zasu tabbata tare"

"Me kike nufi,tare zaku tabbata tunda mijinki ne"

Girgiza kai tayi"ba zaki gane ba"
Ganin sun isa bakin motar ne yasa dole tayi shiru,

Kallon Farhan Nafisa tayi dake jingine a jikin mota"dan Allah wani mota zan saka Amarya?

Da hannu ya mata nuni da wani karuwar Jeep baka dake ɗan nisa dashi kaɗan,

Nufar wurin suka yi yana bin wacce fuskarta ke

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login