Showing 33001 words to 36000 words out of 159134 words

Chapter 12 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt

27 Sep 2025

9757

Suraj bane ake hakura da shi,Allah dai ya dawo dashi lafiya,amma wannan karon dole salon zai canja"

Da haka dai suka tafi,in da suka bar ta cikin tsananin mamakin su kuma,
Ganin tana kokarin faɗawa tunani ne yasa ta watsar da lamarin ko ma dai menene gara ta cika nata aikin ta bar gidan.

Ana gobe zai dawo Ammi ta saka suka shiga kyaran gida,duk da dama ko'ina a kyara yake ko yaushe amma na yau na da ban ne,
Ita da kanta taje ta kyara mai dakin shi,bata bari ko Amira ta shiga ba,

Ranar da zai dawo ma basu fara shirya abinci ba sai da akayi sallah Azahar,zuwa ƙarfe hudu da rabi gar sun kammala,
Wanka tayi ta nime wuri ta kwanta tana karanta littafin girkin da A'i ta bata,tana kuma tunanin hanyar da zata bi domin samun shiga dakin shi.

Jin diran motoci a harabar gidan ne yasa ta tashi daga kwancen da take ta buɗe wundan ɗakinta wanda zata iya hangan harabar gidan duk da yayi nisa sosai ba zata iya tantance mutanen dake wurin ba,
Motoci ne guda biyar wannan karon,sun ɗan jima daga bisani kuma taga sun guya sun bar gidan,
Komawa tayi ta kwanta,tana aiyana ƙila ya dawo ne,
Ganin har ƙarfe shida tayi ne yasa ta tashi ta fito daga shiyan su,kamar zata nufa shiyan kaka,sai kuma ta juya tayi hanyar Boys Quetta,
Tasan wannan lokacin duk mazan gidan basa nan,dan haka daga tsayen da take ta kunna wutar Sigari ta saka a baki,kyakkyawar zuka ta masa tana busar da hayaƙin tare da lumshe ido,
Duk da tasan ba ko yaushe take sha ba,amma a ƙalla a sati tasha sau biyu,to kuma gashi tunda ta dawo ko sau daya bata sha ba sai yau,shi yasa take jinta a sama,

Tunda ya nufo sashin su yake jin warin Taba,abinda yafi tsana a rayuwar shi,ko kaɗan baya so,
Mamaki ne ya kamashi domin bai taba tunanin a gidan a kwai mai shanta ba,dan bai taɓa jin makamancin warinta ba,
Duk da duhun Magriba ya gabato amma yana iya hanyan ko ina na wurin,

Idanun shi ne suka sauka a kanta,yanda take busa hayaƙin sama cikin ƙware da kuma yanda ta riƙe a hannu,wannan shi zai tabbatar maka da cewar ita din ba yar koya bace,
Gabaɗaya ya kasa yarda da abinda yake gani,Mace! To yana dai ji a labarai,

Jikinta ne ta bata kamar ana kallon ta daga ta wani wurin,dan haka da sauri ta shiga juye_juye,sai dai bata ga kowa ba,
Ajiyar zuciya tasauke ta yarda karan sagarin ta murje da ƙafa,kafin ta bar wurin.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*23*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*

Komawa shiyan su tayi,sai da aka yi Sallah Isha'i sannan ta fito zata shiyan Kaka,
Ta kusa shiga shiyan ne ta ji an finciko ta anyi baya da ita an jin gina ta jikin bango,
Kasancewar wurin akwai ƙarancin haske hakan yasa bata gane ko fuskar waye ba ne,sai da ta ji muryar sa yana sun sunan wuyanta,cikin muryar da zai nuna maka irin shaukin da mutum ke ciki yace"Baby na ina kika tafi kwana da kwanaki,sannan kin dawo kin kuma hana ni ganin fuskar ki"

Oh sai yanzun ta dago muryar shi,kauda fuska tayi,domin bata son ta nuna mashi halinta,in ba haka ba,wlh da in ta rike shi sai ya gudu da kafar shi,"Nurudeen bana son haka"ta faɗa tana ƙoƙarin barin wurin,
Riƙe mata hannu yayi yana ƙoƙarin jawo ta baya "akwai maganar da nake son na faɗa maki"

"To sake ni sai ka faɗa min"
"Kina da kyau"
"Na sani" Ta bashi amsa kai tsaye,
"An taba faɗa maki"
"Sosai ma"
Murmushi yayi"wannan ba abin mamaki bane idan aka yi duba da cancantar ki"
Kafin ta bashi amsa ne suka ji daga bayan su wani sanyayyan murya yace"Excuse me "

Ganin wanda yayi magana ne yasa gaba ɗayansu shan jinin jikin su,saboda shi rike yake da hannun ta,cikin sauri ya sake ta,yana matsawa gefe,ita ma haka,amma shi gogan ko a jikin shi,sai ma raɓawa da yayi ta gefen su ya wuce ya bar su da kamshi,
Ganin ya shige shiyan Kaka ne yasa da sauri ta juya ta bar wurin,dan Gara kawai ta koma shiyan su,ita bata san Me yasa a duk lokacin da zasu haɗu basa haɗuwa da sa'a ba,yanzun ba sai ya mata kallon mara da'a ba,
Wani zuciya nata ne ya bata amsa kai tsaye,dama da'a gare ki,nan take ta saki murmushi,domin rabon ta da wannan kalmar shekara biyar kenan daya wuce.
Tana shiga daki faɗawa tayi kan gado tana lumshe ido,kome take tunani?Allah kaɗai yasan abinda ke gudana a zuciyar ta,daga bisani kuma sai naga kamar hawaye na gangarowa daga idanun ta data lumshe,sai dai kafin na tantance sai gani nayi ta kifa fuskarta cikin filo,sai kuma a hankali shesshekar kuka ke tashi,wanda idan ba wai ba ka saurara sosai bane ba zaka taba tsammanin ana yin shi ba,ita wannan ba komai bane a wurinta face abinda ta saba komai tsayin dare sai yishi,in dai wannan kukan ne,
Jin alamar kamar za'a shigo ne yasa da sauri ta gyara natsuwar ta,tana goge fuska da sauri,
Amira ce ta shigo da sallamah"Biba wai inji Ammi ki fito ki yi wanke-wanke an kama"

Mikewa tayi"ok gani nan tafe"
Cikin natsuwa take aikinta har ta kammala yanda kasan ba ta da wani damuwa domin fuskarta a washe yake,
Ba ta yarda masalarta ko damuwarta ya nuna a fuskar ta,abu ne mai wuya,
Wannan tsakanin ta da zuciyar ta ne.
Tana kammalawa daki ta shige ta kwanta,dan ta kammala aikinta na yau sai kuma gobe idan Allah ya kaimu,

Washegari ma bayan an idar da sallah ne ta fito ta shiga gyaran gidan sannan ta daura break Fast,Waina da Miya tayi,wanda ya ji kayan haɗi,
Koda ta kammala har takwas ta wuce,dan haka daki ta koma tayi wanka,dan tana idar da sallah suke gaisawa da Mam,
Daukar na kaka tayi ta kai mata,
Koda ta dawo bata lura dashi zaune ba,sai da Ammi ta ce"Biba zubo ma Suraj Waina"

"Ammi wa yayi Waina? Ya tambaye ta,
Kasancewar tasan yana matukar so,cikin murmushi tace" Biba tayi,kuma gashi yayi laushi yanda kake so"

Daukar wayar shi dake gefen shi yayi yana mikewa"Ammi ki ce ta barshi kar ta zubo,yau bana jin cin waina "

Kallon mamaki take mai,domin tasan yanda yake son waina ko ya ko shi ne sai ya dauki guda daya ya saka Albarka,
"Yau kaine baka jin cin waina?
Murmushi ya sakar mata" Bari na tafi na gaida Kaka Ammi,zuwa anjima zan shigo"
Jin jina kai tayi,tana binshi da kallo,
Ita dai tana kicin tana jinsu,
Koda yaje shiyan Kaka ma haka ne ta faru,domin tana mai tayi ita ma ce mata yayi baya jin cin masa,

Ta gaji da zama ita kaɗai,gashi duk yaran gidan sun tafi makaranta,dan haka fitowa tayi ta zauna ta gefen Barandar su,ganin kamar rana yana son ya takura mata ne yasa ta canja wurin zana zuwa ta takanin shiyan Goggo da Hajiya Rahama,daga inda take zaune tana iya hango duk mai shiga da kuma wanda zai fita,
A karamar wayar dake hannun ta take buga game,duk da ba wai daɗin shi yake ji ba,
A hankali ta fara jin sautin murya na tashi,cigaba da buga game ɗin ta tayi,iska ne ya kwaso magana ya faɗa kunnen ta,wanda wannan kalmar ce tasa ta natsuwa ta ajiye wayar hannun ta"gabaɗaya ya tare min numfashi,baƙin ruhi ne dashj,ba zai taɓa bari mu ci galaba akan shi ba,"

Ɗayan da suke magana mai sanye da dogon hijabi har katsa ne ta ji tace"kome yake taƙama dashi,wannan karon abin ba zai taba zuwa yanda zai yi tsammani ba,domin sai yayi kuka da idanun sa yana niman cito,alokacin da babu wani Mahaluki da zai yarda da shi,"

Tabbas wannan ba muryar mace bane kamar yanda take ganin mutum sanye da hijabi,Namiji ne,amsar da zuciyar ta ya bata kenan,amma yanda yayi shirin mata har da nikabi ba zaka taba kawo hakan a rai ba,
To su waye,dukkanin su sun juya mata baya,bata gane wacce macen ba,amma daga dukkan Alamu a gidan take,
Ganin jamar zasu juyo ne yasa da sauri ta bar wurin ta koma inda ta taso,zuciyar ta fal da tunani,to waye abin harin su,gaskiya akwai masala koma waye suke hari,ita dai gara tayi ta gama ta koma inda ta fito,dan zaman gidan sam baya mata daɗi ko kaɗan.

Tana kallo har mai hijabin yazo ya wuce,ta jima a wurin kafin ta tashi ta koma shiyan su dan locin yin girkin rana yayi,

Da yamma tana kammala aikinta shiyan Kaka ta tafi wurin Nafisa,dan ta gaji da zama ita kaɗai,sun sha hira tare da Kaka kafin a kira sallah,su suka shige dakin Nafisa har aka yi Isha'i,
Suna jin sanda jikokinta suka fara zuwa gaishe ta,wasu su zauna wasu su wuce,
Hadiza ce take ba Zainab labarin wani India film data kalla jiya,gabaɗaya sun karaɗe falon da surutu,
Fitowa tayi domin ta ɗaukar ruwan sha,ta buɗe firig kenan ta ji falon ya dauki wani irin shiru yanda kasan ba mutane a cikin shi,sai kuma ta ji sanyayyar muryan nan dai yana sallamah,
Sai da Kaka tayi dariya kafin ta amsa,
Shigowa yayi ya zauna a gefen ta,
Cikin zolaya tace "wai ya naji shiru ne kamar ba mutane a falon"
Dago shanyanyun idanun shi yayi ya sauke a kansu,yanda duk suka natsu,
Mai da duban shi yayi kan Kaka"Me ya faru?

Gabaɗaya sun cika ni da surutu,nayi magana sunce wai suyi shiru kamar babu mutane,to yanzun bansan me ya faru ba naga duk sun natsu kamar babu kowa ma a nan"ta karasa faɗa da murmushi,

Aunty Maijiddarh ce cikin salon yanga da makale murya tace"Kaka ai hira suke taya ki"

"Ke kuma me ya samu muryar ki na ji ta kamar a shaƙe,ko mura kike yi ne"cewar kaka tana tambayar Maijiddarh domin tasan yanzun dai ta gama magana da muryarta lafiya amma yanzun yanzun kuma ace ya shaƙe,

Da yake su ƴan mata ne shi yasa nan take suka fahimci abinda ke faruwa wato make murya tayi,dan tana gaban shi,
Ai kuwa mantawa sukayi suka shiga kyalkyata dariya,Zainab harda dukawa "kai Aunty Maijiddarh harda make murya kuma,wallahi ko kyau bai maki ba"

Ɗaukar ruwan dake gaban kaka yayi ya ƙafa a kai yayi Bismillah ya shanye,

"Biba ɗauko ma Surajo Fura a firij ya sha tunda ya shigo"

Amsawa tayi da to sannan ta buɗe firig din da har ta rufe ta jawo kwanun dake ɗauke da lafiyayyen fura da aka dama shi da Kindirmo,

Tana daukowa ta kawo gabanshi,sai da ta duka sannan ta ajiye,
Har ta juya baya sai ji tayi yace "ke"

Duk da ta ji yace ke,amma hakan bai sa ta juyo ba,sai ma cigaba da taku da ke yi,

Zainab ce tace"ke Biba baki jin Yaya Suraj na magana"

Juyowa tayi ba tare da tace komai ba,hakan ne ya tunzura shi,domin ba abunda ya tsana irin yayi magana a kyale shi,dan ne zuciyar shi yayi,ya nuna ta da yatsa"zo ki dauke wannan abun a gaba na"

Ba ita kaɗai ba har ta kaka kallon mamaki take mai,
"Ni fa na dama da hannu na, na kuma ajiye maka"

Kallon kaka yayi"daga yau in dai har kina son ki ba ni abu na ci ko na nasha,to kar ki ƙara barin masu aiki su taɓa,ko da kuwa ɗauko min ne,"

"Me yasa" Ta tambaye shi mamakin ta na ƙaruwa, domin abune da bai taba yi ba,

Kallon ta yake ido cikin ido"Saboda kazamai ne,and I hate it"

Nan take ta ji idanun ta sun cika da hawaye,domin babu wani cin fuska daya wuce wannan,a kalle ka ido cikin ido a kira ka da kalmar da ko haɗa hanya ba ku yi da ita,wato ƙazanta,ganin baida niyar dauke idanun shi a kanta ne yasa ta ɗauke idonta a kanshi,tana ƙoƙarin haɗiye hawayen ta,domin ba zata taba bari su zubo anan ba,

"Amma Suraj naga daga Biba har Nafisa duka su suna da tsafta sosai,na yarda da tsaftar sune shi yasa ma suke zaune tare da mu"

Mi kewa yayi tsaye yana ƙara daura idon shi akan fuskarta"ki ƙara binciken ta "yana gama faɗar haka ya bar falon,

" Waye zan ƙara binci ka"cewar kaka tana kallon shi yana barin falon,sai dai bai bata amsa ba ya wuce.

Juyo da kallon ta kan Biba tayi wacce ke tsaye tamkar wacce aka dasa"me ke faruwa "ta tambaye ta,

Girgiza kai kawai tayi ta juya ta koma dakin Nafisa,
Duk da kallo suka bita,kafin kuma ta maida kallon ta kan kwanun Furan ta,
" Mejiddarh zo ki ɗauka kusha tunda shi wanda akai ma gwanin ta ba'a burge shi ba "

Riƙe baki tayi"ni! Wallahi Kaka bana sha,haka kurum,tunda kika ga Yaya Suraj ya faɗi haka shi yasan abinda ya gani,kinga na ma wuce"ya faɗa tana ƙoƙarin barin falon,

"Zainabu zo ki ɗauka Kuje kusha"

Dariya suka saka "a'a tsohuwa ki dai sha abin ki"
"To yanzun ni ya kuke son nayi da wannan Furan?
Ai tuni duk sun fita sun bar ta cikin Mamakin su,to amma me shi Surajo yaje nufi ne,

Fitowar Biba ne yasa ta dago tana kallon ta,
Dukawa tayi kaɗan" Kaka na wuce sai da safe"

"Zo ki zauna Biba" Ta faɗa tana nuna mata kusa da ita,

A hankali ta tako ta zauna kusa da ita ta zauna in da ta nuna mata,

"Ki yi hakuri da halin Suraj,shi haka yake,sai dai ina son ki san shi mutum ne mai matukar sauƙin kai,bai cika shiga harkar da ba nashi ba,balle na masu aiki,wannan shine karo na karko da ya taɓa faɗar haka,shi mutum ne mai matukar kyankyami,bansan me ya gani tattare dake ba haka wanda ya saka shi fadar haka,amma dan Allah koma menene ki yi ƙoƙari kiyayewa kin ji?

Hadiye hawayenta tayi"insha Allah kaka zan kiyaye "

"Yauwa Allah ya maki Albarka"
"Amin,sai da safe"
"Allah tashe mu lafiya"

Tana shiga daki ta saka sakata,
Fadawa tayi kan gado tana fashewa da kuka,tunda take a rayuwar ta ba'a taba mata irin makamanciyar wannan abun ba sai yau,babu wanda ya taba faɗa mata haka,a kowani rana tana wanka sau uku a rana,ta goge baki sau uku,a jikinta ba ta barin ko da digon suma ne,in dai batun tsafta ne sai dai ta nuna ma mutum ba dai a nuna mata ba,kayan wanka ta ma odar take yi daga Indiya,amma shine wannan Ustazun saboda baya tsoron Allah zai kalli cikin idanun ta ya fada mata bai yarda da tsaftar ta ba,wannan abu yafi komai bakanta mata rai,kallon idanun ta da yayi,
Insha Allah sai ta shayar dashi madaran mamaki,ta yanda zata ga yaya zai yi da rayuwar sa a wannan lokacin,
Ranar haka ta kwana cikin baƙin ciki, da Alwashi.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*24*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*


Washegari haka ta tashi cikin rashin walwala,a haka ta kammala aikin ta na gida,ranar ko shiyan kaka bata shiga ba tana dakin ta,sai da rana ta fito tayi girkin rana,tana kammalawa ta jira in da ake jerawa,
Ammi ce ta kira ta dakin ta,
Amsawa tayi tana shiga dakin da sallamah,wani kwali ta nuna mata da kuma makulli,"dan Allah dauki wannan kwalin da makullin ki buɗe dakin Abbi ki ajiye wannan a falon sa,yau ƙafan nan so yake ya takura min"

Ai ji take gabaɗaya ta nime bacin ranta ta rasa,har ma bata san sanda ta saki wani murmushi ba,"to Ammi"

Har takai hannu zata ɗauka sai suka ji sallamar shi,amsawa Ammi tayi,tana faɗin "yauwa ga ɗan Albarka nan ya shigo,kinga barshi Biba bari nasa kawai yakai min"

Nan take taji wani kololo ya sauko ya mata saye,wannan fa shi ake kira anga samu anga rashi,
"Ammi bari nakai maki kawai" Ta faɗa tana addu'ar Allah ya bata sa'a ta amince,
"Jeki abinki ai kina ƙoƙari Allah dai ya maki albarka"

Kasa amsawa ma tayi ta fita tana barin dakin cikin tsananin jin haushin shigowar shi,gabaɗaya ya bata mata jin daɗin ta,
Dan haka inda suke ajiye su Omo ta nufa ta dauki wani gora da naga an rubuta Fresh a jiki ta buɗe ta zuba da yawa a cikin bokitin da suke morping daki dashi,ta zuba ruwa kaɗan,sannan ta saka mopa ta fito falo da sauri,
Ta dai-dai ƙarshen matakala tana tsamo mopa ko matsewan kirki bata yi ba ta saka a ƙasan wurin ta shiga kogewa,ta yanda sai da ta tabbatar wurin ya juku yanda take so sannan ta maida kayan in da ta dauko ta koma gefe ta tsaya ta naɗe hannu,

Tunda ya fito daga ɗakin Ammi ta kure shi da ido tana taunar yatsanta a hankali,Allah_Allah take kawai ya sauko,
Jikin shi ne ya bashi ana kallon shi,duk da ya saba da kallo domin ba baƙon shi ba,amma yasan a gidan ba mai mai irin wannan kallon mai shiga jiki,dan haka dan juyawa yayi ya kalle ta inda yake jin nan din ne,ai kuwa idanun shi ne suka sauka a kanta,sai dai kuma hankalin ta bawai a kanshi yake ba akan takun da yake yi yake,bin inda idanunta ke kallo yayi,kafin ya dauke kanshi,
Faɗi take ai Gara kai ma ka karye ko zan samu damar cika aiki na in huta,
Kirgawa take yi saura huɗu,saura uku,saura biyu,saura d....

Ɗan ƙara ta saki tana yarfe hannu jin zafin cizon da tama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login