Showing 78001 words to 81000 words out of 159134 words
Chapter 27 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt
tayi wanda ya nuna ƙarfe Uku na dare,
Komawa tayi bakin gado ta zauna a kasa tana daura kanta a saman katifar gadon a maimakon ta hau ta kwanta,
Daga haka ne bacci barawo yayi awan gaba da ita ba tare data shirya ma hakan ba.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*48*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Washegari tana tashi wanka tayi sannan tayi sallah ta koma ta kwanta tana jawo wayarta ta buɗe data,
Bansan me take yi ba amma daga dukkan alamu abu mai muhimmanci take yi,wanda tana yi tana duba agogon dake makale jikin bango lokaci_lokaci saboda ƙarfe goma na safe za'a fara gudanar da nashi shari'ar,
Dan haka sai ƙarfe tara sannan ta tashi tayi break Fast wanda tasa aka kawo mata tun dazu,
Number Alhaji Mansour ta kira tana sanar dashi ta kammala ya turo mata direban sa yace zai mata aiki,
Nan yake sanar da ita ai mutumin yana harabar Hotel din yana jiranta tun ƙarfe takwas na safe,
Kashe wayar tayi ba tare data damu da mai godiya ba ta fito,
Tsayawa tayi a babban harabar Hotel din tana kallon manyan motocin dake farke a wurin,
Ji tayi daga bayanta ana fadin"Hajiya barka da fitowa "
Juyowa tayi ta kalli mutumin wanda bai wuce sa'ar yayanta ba,sai dai bata ce mashi komai ba,
Da hannu ya mata nuni da inda wani lafiyayyen mota ruwan ƙasa ke parke "Hajiya ga motar can"
Bin bayan shi tayi ba tare data jira ya buɗe mata ba ta saka hannu ta buɗe gidan baya tayi zamanta,
Shi kuma buɗe mazaunen Direba yayi ya ta da motar suka fita farfajiyar Hotel ɗin,
"Hajiya ina zamu tafi?
" High court"ta bashi amsa a taƙaice tana kwantar da kanta jikin kujeran motar,
Kunsan yanayin Goslow irin na Legos dan haka ko kafin su isa har ƙarfe goma da rabi ake nima,koda suka shiga koton an daɗe da fara gudanar da shari'a,
_____Acikin koto kuwa ba'a bari wasu mutane masu yawa sun halarci cikin ba,daga dangin Yarinyar sai kuma nashi dangin,wato su Pa dasu Abbu,Dady,sai Nadiya dake ma su Kaka Video kai tsaye suna kallon abinda ke wakana acikin koton,
Haka suma bangaren iyayen yarinyar suma suna da masu kwashe masu,sai dai su kai tsaye suke daurawa a shafikan su na yanar gizo wanda kowa zai iya kallon yanda komai ke gudana,
____A can gida Kano kuwa hankalin su duk a tashe yake,domin gabaɗaya daga manyan gidan iyaye da yara har Ammi a falon kaka suka haɗu suna kallon yanda Lauyan su ke jeho ma Suraj tambaya kuma ya hana shi magana sai dai kawai ya bashi dama in Eh ne yace eh,in A'a ne yace A'a,kuma duka da harshen Turanci suke magana,
Kaka ce ta fashe da kuka"kai Allah ya tsine ma wannan jikan bakin tuwo,ta yaya zai hana yaro magana "
Kuka Amira ta saka tana dafa Ammi dake kusa da ita wanda Allah kaɗai yasan meke gudana a cikin zuciyar ta"Ammi shi kenan yanzun sun kada yaya Suraj,jibi yanda suke zubo mashi tambaya "
"Ai daga ganin yanda wannan lauyan ke jeho tambaya kasan ƙwararre ne, kayar da shi ba abu mai sauƙi bane,gaskiya da wuya akai labari" Cewar Hajiya Saude,
"Koma dai menene karfin addu'ar mu na tare da Suraj Allah zai baiyana gaskiya ta inda basuyi zato ba" Goggon yara ta fada,
Dafa hannun ta tayi"me yasa zaki karaya tun yanzun,bayan ko asalin shari'ar ba'a fara ba "
Duk kallon mamaki suke mata,Ibrahim ne yace"Ammi amma ai har yanyi rabin shari'ar,idan kuma har aka kai karshe ba tare da wani kwakkwaran hujja ba shike nan mun rasa wannan shari'ar "
Nuna masa TV tayi"ai ba kai karshe ba,amma ka kalla ka gani"
"A'a wacece wannan ta shigo?ku kalla ga wata nan ta shigo sanye da kayan lauyoyi"
Duk maida hankalin su kan TV suka kuma yi,
_________*Legos*
Mai gadin bakin ƙofar babban Hall din ne ya buɗe mata ƙofa bayan ta nuna mashi I.D card ɗinta,
Jin an buɗe ƙofar ne yasa Lauyar dakatar da wasu tambayoyin da yake ma Suraj ɗin,
Taku take cikin natsuwa tana juyawa tamkar wata Ɗawisu,har ta iso dai dai in da take da damar tsayawa kafin ta cire gilashin dake Idanunta wanda ya kusa rufe rabin fuskarta ta rike a hannun,
(Kuyi haƙuri da yanda shari'ar zai zo domin bansan yawancin ka'idojin Kotu ba).
Daya daga cikin masunjojin kotu ne ya tashi"Hajiya shin baki san nan kotu bane da zaki shigo kai tsaye tamkar gidan ki?
Ba tare data bashi amsa ba ta maida fuskanta kan Alkalan dake zaune su biyu cikin girmamawa irin nasu tace"ina niman afuwa akan jimawar dana ni ban karaso ba,wanda hakan ya faru ne sakamakon cunkoson abun hawa,
Ni suna na *Ummu Salma Abdullah Lauyan wanda ake tuhuma*
To fa wannan shi ake kira kallo ya koma sama,
Nadiya ce ta dafa yayan ta tana kallon Pa"Pa wannan ai daughter Biba ce,matar Suraj "
Ɗan rankwashi yayan nata ya sakar mata"ba ita ba ce,ke dai ki yi shiru muji "
"Kina iya zama kotu ta maki uziri amma nan gaba ki ki kiyaye"
"Na gode ya mai shari'a" Ta faɗa tana zama a kujerar da aka tanada dan su,wanda ta samu lauyoyi biyu a zaune,
Lauyan dake magana ne ya cigaba da faɗin "Ya mai shari'a,kamar yanda na gabatar ma da kotu kwararan hujjojin na,ina rokon koto data yi gaggawar yanke ma mai laifi hukunci ba tare da bata wa kotu lokaci ba"sannan ya koma ya zauna
Alkalin ne yace" A sakamakon waɗannan hujjojin da Lauyan mai ƙara ya gabatar,koto ta duba kuma ta gamsu dashi,zata kuma yi amfani dashi wurin yanke ma mai laifi hukunci.....
Mikewa tsaye tayi tana daga hannu "ya mai girma mai shari'a,a matsayina na Lauyan wanda ake tuhuma ban yarda da hujjojin da Lauyan wanda yake kara ya bayar ba,sannan ina da tambayoyin da nake da bukatar na ma wanda nake karewa a gaban kotu sannan tare da ba da nawa hujjojin kafin a yanke hukunci"
Ji yayi kamar ya taso ya shake wannan yarinyar daga saman kujeran da yake zaune,wacece ita da zata bata masu shirin su,daga ina take,shi yasa yaso ya yanke hukunci kai tsaye amma ta katse shi,daga ganin kuma yanda take tana da kwarin gwiwa,domin babu alamar tsoro a tattare da ita ko fargaba,chief ya fada a zuciyar shi,wanda ba shi kaɗai yake raya hakan ba,yasan suna da yawa a koton masu tunani irin nashi,dan daga inda yake zaune yana iya hango bacin rai mai tsanani ƙunshe a fuskar Shugaba,
Babu yanda ya iya dan haka dole yace"Kotu ta baki dama"
"Na gode mai shari'a" Ta faɗa tana haurawa saman stage din da yake tsaye yana kallon ta tun shigowar ta,duk da ada ya fara cire rai akan zuwan nata,
"Malam shin zaka iya faɗa mana Asalin Sunan ka? Ta fada cikin kwarewa da harshen turanci,
" Suraj Abdul basir "
"Menene Alakarka da Jusica"
"Ba ni da wata Alka da ita,asalima ban santa ba"
"Idan baka santa ta yaya aka samu gawarta a cikin dakin Hotel din da kake zaune?
Zuba mata ido yayi na sakanni,yayin data kauda kanta daga kallon da yake mata,
" Ni ma ban sani ba,domin bansan da gawar ba sai da jami'an tsaro suka zo suka bincika "
Juyawa tayi gaban Alkalan "ya mai girma mai shari'a,ina son kotu tayi duba da waɗannan takardun binciken da likitoci suka gudanar a kan gawar,wanda ke nuna babu shafin hannun wanda ake zargi akan jikin Jusica,ko kuma wuƙar da aka yi amfani da ita wurin cire wani shashi na jikin ta,ina son koto tayi duba ga wannan ta kara nazari akan wannan batun"
Mikewa Lauyan su yayi"ya mai shari'a,Barista Ummu Salama ba ta da wani hujja da zata gabatar ma kotu,so kawai take tayi ma kotu wasa da hankali ta kuma bata ma kotu lokacin "
"Ina da dama da zan fada duk abinda zan faɗa kuma kotu ta saurare ni a matsiya na Lauyan under Section 10 a kundin littafin lauyoyi,"
"Kotu ta baki dama,Barista Wale ka kiyaye"
Dole ya koma ya zauna yana hararanta,ƙarama da ita tana ƙoƙarin maida masu da aiki baya,
"Yamai shari'a ina rokon kotu ta Bani damar yi na shugaban yan sanda na wannan yanki tambayoyi?
" Kotu ta baki dama"
Nan matsinjan ya fara shelan mutumin kafin katon Bayaraben ya fito yazo ya tsaya gaban kotun,
"Ya sunan ka?
" Suna na Akintola "
"Malam Akintola ko zaka iya faɗa ma kotu ta yaya ka samu labarin cewa akwai Gawa acikin wannan Hotel din a kuma dakin da wanda ake tuhuma yake ciki"
"Eh na samu labari ne daga kiran dana samu"
"Muna bukatar jin daga waye ka samu kiran?
Ɗan shiru yayi kamar mai nazari kafin yace" Nima ban san ko waye ba kawai dai number ne ya kira ni ya faɗa min,ni kuma naje domin na tabbatar shine na samu abinda na samu"
"Ina butar ganin wannan number da aka kira ka dashi"
"Wayar ya faɗi,an sace wayar"
Jin ji na kai tayi"shin an sace ne ko ya faɗi ?
"Ya faɗi ne"
"Zaka iya komawa ka zauna"
"Na gode" Ya faɗa yana sauke wani ɓoyayyen ajiyar zuciya,
"Ya mai shari'a ina butar kotu ta Bani dama domin nayi magana da Manager Hotel"
Daya daga cikin masunjojin yace" Manager wannan Hotel din baya nan saka makon wani uziri da ya kama shi ta tafi garin su Jos"
Komawa tayi gaban koton"Ya mai shari'a sakamakon rashin kammala haɗa hujjoji na ina rokon wannan koton mai adalcin data ɗaga wannan shari'a daga nan zuwa ranar Ishirin ga watan nan"
Ɗayan Alkalin ne yace"sakamakon duba da wannan lamarin da kotu tayi,Kotu ta daga wannan shari'ar daga yau hudu ga watan April shekara ta dubu biyu da ishirin da uku zuwa goma ga wannan watan na April shekara dubu biyu da ishirin da uku"daga nan ya buga wannan ɗan sandan nasu,
Duk mikewa suka yi cikin girmamawa,
Duk da taso ta samu ƙarin ƙwanaki ta yanda zata yi bincike sosai a kan komai amma shine suka bata kwana shida kawai,
Duk da taga sanda suka biyo dashi ta gabanta zasu tafi dashi gakan baisa ta dakata daga haɗa takardun da take yi ba,har suka wuce dashi,
Tana fitowa ta samu su Dady suna jiran fitowar ta a harabar wurin
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*49*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Karasawa tayi in da suke tsaye,sai da ta kalli agogon dake hannun ta wanda ya nuna mata ƙarfe goma sha-biyu na rana,
"Barka da rana"
"Habiba me ke faruwa ne?cewar Abbu,
Murmushi ta saki,dama ta san hakan zai faru" Ba wani abu bane Abbu,ku kwantar da hankalin ku na maku Alkawarin idan komai ya lafa an gama wannan shari'ar zan sanar daku komai "
Pa ne yace "ki faɗa mana komai yanzun dai,da Ummu Salma muka ji fa kin gabatar da kanki"ya faɗa kamar adan hasale,
" Abu mai muhimmanci shine yanda Suraj zai fito,sannan koma menene ya biyo baya, na bar ku lafiya sai mun haɗu a kutu"tana gama fadar haka ta juya ta wuce,dan ba zata manta maganar A'i da tace mata karta yarda da kowa har a cikin gidan,
__________*Kano*
"Kaka wannan ba Biba ba ce?
Duk ƙara kurama TV ido suka yi,
" Kanbu,wallahi ita ce,kaka nifa na fara tsoron lamarin yarinyar nan,ki duba yanda tayi mana bazata a wurin taron mata malamai,yanzun kuma Lauya?
"Shi yasa naso tun farko na aure ta saboda nasan ita din Materiel ce"
Duk kallon mamaki suke mai,
"Ka nada hankali Nurudeen?
Bata fuska yayi yana kauda kai,dan abinda ya faɗa har cikin zuciyar shi ne,
" Ni dai in komai ya wuce a bin cike ta"cewar Hajiya Rahama
"Wallahi Momy na fasa zama likita lauya zan karanta,dubi yanda Biba ke zuba Turanci kamar ba a bikinta ya ke fitowa ba"cewar Hadiza,
" Ammi me ke faruwa? Ta faɗa tana kallon TV yanda ake zuba challenge,
"Koma me ke faruwa lokaci zai nuna"
_____________tana shiga mota tace ma direban"muje gidan yari"
"To Hajiya" Ya faɗa yana karya kwana,
Koda suka isa buɗe mata kofa aka yi aka bata damar yin magana dashi kamar dai jiya a wannan ɗakin,
Jan kujera tayi ta zauna suna fuskantar juna,
"Ina yini"
"Assalamu alaikum" Ya fada,
"Oh Assalamu alaikum"
"Wa'alaikumussalam,wannan ya zama abu na farko da zaki fara yi aduk sanda muka haɗu"
Turo baki tayi"har yana da bakin korafi"
"I can hear you"
"Akwai abunda nake buƙatar na sani ne?
Ganin irin kallon da yake mata ne yasa tace" Ina nufin a matsayina na lauyan ka"
"Babu"
"Akwai mana,kamar daga lokacin da gawar ya kasance a dakin da kake,ko kuma wani yanayi ko kuma dai abinda kake zargi ko wanda kake zargi, dole za'a samu wani"
"Duka babu" Ya faɗa a takaice,
Ajiyar zuciya ta sauke tana dafe kumatunta,yayin da hankalin ta ya tafi kan wani nazari na daban,
Zame hannun nata yayi daga tagumin da tayi wanda hakan yasa goshinta ya bugu da center table ɗin,
Dafe goshinta tayi tana shafawa,cikin jin haushi tace "me haka?
Kafaɗa ya daga" What"
Mikewa tayi sai kuma ta koma ta zauna da sauri tana sakin murmushi,"yauwa ina Kakan ka take,ina nufin a wani Country take "
Shiru yayi kawai yana kallon ta ba tare daya bata amsa ba,
Ɗan marairaice fuska tayi"bana son irin wannan kallon pls"
Kauda kai yayi yana ɗan lumshe ido kafin yace"me za'a "
"So nake kasa a canja mata Asibiti daga in da take,idan so samu ne har likita ka canja mata,idan kuma ka yarda da wannan kana ita daukar shi aiki har zuwa sanda komai zai kammala ya zama na babu wanda yasan in da take"
Tambayar daya jeho mata ne yasa ta dakata daga maganar da take yi,
"Me yasa zan yarda da ke?
Shiru tayi na wasu sakanni yayin da suka shiga musayar kallon na sakanni kafin ta dauke nata idanun" Wannan zabinka ne ka yarda da ni ko akasin haka"busar da iskar bakin ta tayi sannan ta dawo da kallon ta kanshi"ni ba kamar yanda kake gani na nake ba,ko da yake ina dauke da Najasa,haka ne tunda ni din *ƘARUWA CE* kana iya saka Hausar a haka,ta iya yuwa kasan abinda ya shigo da ni rayuwar ka ko baka sani ba,amma ina mai tabbatar maka haɗin kanka shi kawai zai saka mu tsira tare da kai,
Idan kuma har mukaci nasara zan bar rayuwar gabaɗaya ba tare da na bar maka wani abinda zaka tuna da ni ba,"
Jin kalmar data kira kanta dashi kaɗai ya saka zuciyar shi dukawa,
"Idan har baki ci nasara ba fa?zaki fita ki bar rayuwata?
" Duka daya ne?idan ka yi tunani akai kana iya sakawa a kira ni"ta faɗa tana mikewa,
Har ta kusa kaiwa ƙofa ta ji yace"Germany,Berlin, Mitte,Orthopedic Clinic (Campus Charite Mitte)
Takardar da ke ajiye a gabanshi da biro ya ɗauka yayi dan rubutun da bai wuce layi uku ba ya turo mata,sannan ya tashi ya wuce,
Murmushi ta saki tana bin shi da kallo kafin ta dauki takardan ta fita,
Daganan ta wuce cike da tunanin dole gobe zata tafi domin bata da isasshen lokaci.
______karan saukar Mari ne ya karaɗe dan madaidaicin falon,
Cikin masifa da tsananin bacin rai yace"i will killed you,me yasa baka faɗa min tun tuni ba sai yanzun,gashi saboda kai aikin da muka yi shekaru muna shiryawa kana kokarin ruguza komai,bayan mun sha matukar wahala kafin mu samu wacce zata iya "
Cikin tsoro da rawar jiki ya tsugunna a gabanshi "dan Allah shugaba kamin rai ba zan sake ba,ko da na bar ta Lafiya ta qlau ban San zata mutu ba"
Wani marin ya ƙara sauke mashi yana huci,"ita ce yanzun ta tsaya masa a matsayin lauya,bayan kwangilan da muka dauke ta,kalli sakon data turomin"ya faɗa yana nuna ma Abokin nashi saƙon,
"Yanzun mu kirata muji me zata faɗa"cewar Chief,
Duk na'am suka yi da hakan,dan haka wayar shi da yake kiranta dashi ya ɗauka ya shiga kiran number ta,
Sai da yayi ringin uku ba'a dauka,har ya cire rai za'a daga sai gashi yaji an daga,
Sai saita kanshi yayi,kafin ya ce" Me haka ke nufi?
Daga in da take zaune tana shirya wasu takardu ta bashi amsa"kamar me kenan?
Danne duk wani bacin ranshi yake kokarin yi"Ummu Salma,"
"Suna na ne"
"Sunan ki fa?Kotu fa?Barrister?me kike shirin yi ne,me manufar ki na kare wanda kike aiki a kanshi?ina bukatar karin bayani domin kinsan haka baya cikin tsarin aikin mu"
Dariya tayi irin mai tsayawa a zuciya na takaici "tsarin aiki fa kace?ohh na manta ashe aikin yana da wani tsari?" Ajiyar zuciya ta sauke tana busar da iska mai zafi daga bakin ta"ina da amsar duk tambayoyin ka,sai dai ba zan amsa maka su ba,da kanka zaka fitar da amsar ta hanyar aiki na,
Hmm kai har kana da wani ka'idar aiki,ai tuni na ajiye naka aikin a sanda ka karya alkawarin mu,mun maka aiki na tsayin shekara huɗu,amma ba kaji kunya ko tausayi ba ka kashe Ummi ta,sai dai ka sani wannan shine babban kuskuren da ka yi a cikin aikin ka wanda zai iya mai da maka aikin ka Sifili,kamar yanda bansan ko kai waye ba haka kaima baka san kome a kai na ba,dan haka wasa tsakanina dakai yanzun aka fara,
Ba zan taba bari ka samu nasara ba sai na tarwatsa duk wani guziri naka,sai na