Showing 123001 words to 126000 words out of 159134 words

Chapter 42 - YAR TSANAR ZINARI BOOK COMPELET BY JIDDA UMAR.txt

27 Sep 2025

9779

yaki dagawa kasancewar shi sam baya son ɗaga baƙuwar number,
Tsaki yaja yana faɗin "wannan ko maye ne haka zai ganni ya barni"

"Kai dawa? Cewar Abdulmajid dake ƙoƙarin mika ma Abdulrahman kofin shayin daya hada mashi,

" Wallahi tun jiya wani number ya azabeni da kira"

"To ja ɗauka mana,ka sani ko wani ne da ka sani,ni bansan me yasa kake da irin wannan ra'ayin ba,irin kune idan mutum na niman taimako har a kashe shi baku sani ba saboda wannan ɗabi'ar"

Dariya sukayi shida Abdulrahman dake kurban shayin shi,

"Yama katse bari a ƙara kira sai na ɗaga"

Bai ma gama rufe baki ba kuwa sai gashi an ƙara ƙiran,ɗauka yayi tare da yin sallamah,sai dai jin muryar wanda ke magana ne yasa da sauri ya saka wayar a amsa kuwa ta yanda duk zasu iya jin abinda na cikin wayar ke faɗa,

"Hello,Hello Abdulmalik kana jina Yusuf ne"

"Wani Yusuf? Ya tambaya kamar bai gane me magana ba,

" Yusuf mijin Salma"

"Oh kana nufin tsohon mijin Salma?

" Kaga ba nida lokacin wannan yanzun haka ina Kano na gano Asibitin da salma take ba ta da lafiya sai dai an hana ni shiga dakin da take,dama na maku alkawarin ai duk inda take zan nimota,yanzun haka gani a gaban dakin,dan haka kuna iya zuwa a yau ku dubata ku gani"

Duk shiru suka yi suna sauraren shi har ya kai karshe"yanzun kai kana kofar dakin Salma ne?

"Eh" Ya bashi amsa,

"To ina zuwa" Yana fadar haka ya kashe wayar yana kallon su "hmmm lallai Yusuf,hala shi bai san yanzun sama tayi ma yaro nisa ba ne?

" To me zaka yi da kace ya jira ka?

Ɗan dariya yayi yana kallon agogon dake manne a jikin bangon dakin,"nasan yanzun haka Suraj ya kusa isowa,"mikewa yayi"bari naje na manna mai hauka,domin yanzun ne lokacin ramuwar gaiya "

"Kai dai ka yi a hankali kasan sai za'a ma aiki,karkaje ka yi wani dogon magana"

Bai gama sauraran su ba ya fita yana dariya kasa_kasa.

___________A babban haraban Asibitin motocin suka yi parking,daya daga cikin security din ne ya buɗe mashi ƙofa,har ya sako ƙafa daya waje yaji wayar shi na ƙara,dan dakatawa yayi gani number da take kiran shi,
Sai da yayi ɗan jim kafin ya ɗauka wayar,sai dai bai yi sallamah ba kasancewar ya san da wanda yake magana,

Daga ɗayan bangaren ne aka kira sunan shi cikin harshen Turanci "Suraj Albishirinka?

Murmushi yayi jin abinda yace ya san tabbas akwai labari mai daɗi kenan" Goro fari kar Dr"

Kamar a mafarki yaji yace mai "Kakar ka ta tashi "

Shiru ne ya rasa wayar har tsayin mintuna biyu,
Ya san dama za'a rina "kana jina Suraj"

Wani dogon ajiyar zuciya yaja yana saukewa yanayin da yaji idanun shi na cika da hawayen da bai san ko na menene ba"Umm"

"Da gaske nake yi ta farka bayan dogon suma na tsayin shekaru goma sha ɗaya,sannan munyi observing din ta babu wani damu sai dai dan wanda ba'a rasa shima cikin lokaci ƙanƙani zata dawo dai-dai domin nan a kwai kayan aiki sosai wanda zai taimaka mata har jijiyoyin ta su sake,"

Murmushi ya sake wanda ke fita tare da hawayen dake sauka a fuskar shi "ina take?

" Tana barci a yanzun haka amma daga nan zuwa awanni uku zata tashi,zan haɗa ka da ita,sannan yaushe zaka shigo domin tana buƙatar ka a kusa da ita?

"Nan da awanni goma "

Murmushi shima yayi daga nashi bangaren "sai mun ganka" Daga nan ya sauke wayar,

Hannun ya daga yana kwararo ma Ubangiji yabo da kirari domin ya dawo mashi da ran da ya daɗe da fara cirewa a lokacin da bai yi tsammani ba,
Karasa fitowa yayi yana saisaita yana yin sa,a yanzun burinsa daya ne shine yaga fuskar kakar tasa,

Tafiya yake yi cikin yanayin da zai nuna maka shi din lafiyayye namiji ne mai jini a jika,da kuma takama da kuruciyar sa,yayinda security din shi ke taka masa baya suna doshi cikin Asibitin.......






🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*76*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*

Murmushi kawai suka yi,

"Karku damu babu wata matsala tattare da ita" Cewar likitan da ya gama dubata,

Godiya suka yi masu sannan suka wuce.

Kaka ce da ta kasa hakura tace"Abdulrahman ko?ta faɗa tana nuna shi,

Girgiza kai yayi"A'a Abdulmajid "

"Yauwa Abdulmajid me yasa tunda kuka zo baku shigo cikin gida ba,sannan a ina kuke zaune?

"Da fari a Hotel muka sauka,amma sai Suraj ya matsa sai mun koma gidan shi,"

Kallon su tayi tana kara kallon Biba dake kwance "daga dukkan alamu ku ba matsiyata bane balle ace sabida hakan Biba ke aikatau,ko dai akwai wani dalili ne?

Duk kallon Nurudeen suke suna tunanin amsar daya dace su bashi,

" Tabbas maganar daka faɗa gaskiya ne,sai dai ka sani ita wacce kuke kira da Biba ba shi bane asalin sunan ta,Sunan ta shine Ummu Salma Abdullah,yace yar gata kamar sauran yan gatan yaran da iyayensu ke ji dashi,ita din sanyin idanun ahalin mu ne,abu ɗaya kawai zan iya faɗa maku Kaka"ya juyo yana fuskantar Kaka"tsayin Shekara biyar kenan da muka kwashe muna nimanta bayan barin ta gida,cikin ikon Allah kwanaki uku da suka wuce muka samu kira daga mijinta Suraj,ya faɗa mana yasan komai game da ita,sannan a lokacin da take jin cewar ya kamata ta koma wurin iyayenta da yan'uwan ta,sai gashi ta haɗu da wannan hatsarin, dan haka Kaka muna masu matukar baku haƙuri akan ɓoye maku ita wacece da Salma tayi,sannan muna matukar gode maku akan riƙe ta da kuka yi hannun biyu,Ubangiji ya albarkaci rayuwar ahalunku,sannan Kaka kiyi haƙuri dama muna shirin zuwa har gida wurin ki idan munga ta farka lafiya ita da ɗan uwan mu,da fatan zaki yafe mana?

Murmushi ta saki yana rike hannayen su,"babu komai Allah ya yafe mana ya muka bata lafiya"

Da Amin suka amsa,

Balki ce tace"me yasa to ta bar gida"ta faɗa tana tsare Abdulmajid da ido,

"Idar har ta tashi in har tana da ra'ayin faɗa maku zata faɗa,"

Tabe baki tayi"to ai shikenan"

Murmushi yayi yana rayawa a rashi wannan sai an yi tsiwa,

Nurudeen ya ɗan kara kallon dakin kafin yace"ina Suraj din yake?

"Dazu tafiyar gaggawa ya taso mai kuma ya tafi"Abdulmajid ya basu amsa,

" Bayan anyi ma matar shi aiki ba zai iya tsayawa ta farka ba,yanzun har a kwai tafiyar da yafi matarsa muhimmanci?

Duk shiru suka yi an ma rasa mai bashi amsa,

"Ai ya kira ni ya faɗa min,kuma na tabbatar da koma menene ba karamin abu bane" cewar kaka,

Ba tare daya ce komai ba ya juya ya bar dakin,

"Mu zamu tafi amma dai zuwa gobe zaku shigo ku dubamu ko?

" Insha Allah Kaka"

Har bakin mota suka raka su sannan suka dawo ciki.

Basu jima da tafiya ba ta farka,nan ma sai da likitoci suka ƙara dubata suka tabbatar da cewa babu wata matsala sannan suka wuce suna masu matuƙar farin ciki,sannan da gindaya ma yanninta abinda ya kama tayi da wanda bai kamata tayi ba a yanzun.

Tunda ta buɗe idanun ta take bin ko ina da idanun ta,da take ganin kamar mafarki take yi ko kuma tayi wani irin tafiya ne mai matukar nisa wanda har yanzun bata dawo ba,ko kuwa ta dawo ne,
Duk in da suka bi da ido kawai take bin su,

Ji tayi an riƙe mata hannu,tare da kiran sunan ta"Salma "

shin da gaske da sunan data manta an taɓa kiranta dashi yanzun dashi aka kira ta,
Tsira mashi ido tayi tana buɗewa yayin dake lumshewa duk a lokaci ɗaya,

Ganin yanda hawaye ke fita daga cikin idanun su ne yasa a hankali ta kwada kiran sunan su dan son tabbatar da ko da gaske su din ne zaune a gabanta,
"Yaya Abdulmajid" Ta furta a hankali,

Kara matse hannun ta suka yi cikin nasu yayin da Abdulrahman ya kara fashewa da kuka"dan Allah ki yafe mana kanwar mu"

"Da gaske ku ne?

" Mu ne,Salma!mu ne"

Mai da idanun ta tayi tana lumshewa jin ta gaji da magana,

"Yaushe kuka zo?

Ganin tamkar ta gaji da maganar ne yasa yace" Muna nan tare da ke,ki samu ki huta zuwa da safe zamu karasa magana "

Tun tana kallon su har bacci mai nauyi ya kara dauke ta,

Sanin dokar Asibitin na ba'a kwana da mara lafiya ne yasa dole ganin baccin ta yayi nisa suka koma masaukin su bayan sun duba Abdulmalik.

Washegari kuwa koda suka shigo cikin Asibitin ƙarfe takwas na safe,dan lokaci ne ake bari a ga masara lafiya,
Tana zaune a saman gadon ta an ɗan dago da gadon ta yanda zata fi jin daɗin zama,idanun ta a lumshe suke sai dai ba barci take yi ba,

Jin sallamar muryoyin da take dokin ji ne yasa ta buɗe manyan idanun da suka shanye saboda ciyo tana daurawa a kansu,

Su kansu kallon ta suke yi cikin tsananin bege da kewa,domin shekaru biyar ba wasa bane,

Tabbas suna,domin a jiya gani take tamkar mafarki kawai take yi,

Gani suke yanzun da ta bude ido kuma ta tashi zaune sai tai masu girma,sai suke ganin tamkar ba wannan yar kanwar tasu ɓace wacce suke kula da ita a duk lokacin da take tafiya,sai suke ganin tamkar ba ita bace take zama a cikin su suke wasa tare da dariya tare,suke kuma dauke duk wani kuruya da hauka bana,yau sau suke ganin ta fita masu daban tamkar dai an canja ta,

Jin hawaye ya sauko daga cikin idanun ta ne yasa tayi sauri saka hannu tana sharewa,sai dai kuma sun kasa tsayawa sai ma ci gaba da zuba da suka ci gaba da yi,

A hankali suka ta kowa suna karasowa in da take zaune,gabaɗaya durkusa suka yi a gaban ta suna masu fashewa da kuka,
"Dan Allah ki ga farcen mu Salma,tabbas mu masu laifi ne a gare ki,ki yafe mana a matsayin mu na ƴan adam ajizai"

Kara share hawayen idonta tayi,lokaci ɗaya kuma tana sakin murmushi tare da dafa hannu su dake saman nata,
"A wancan lokacin naji babu dadi sosai musamman idan na tuna wadanda nake tunanin zasu kasance bango a gare ni,su suka fara watsamin kasa a ido,sai naji na ƙara tunzura da son na kuma yin nisa daku sosai, nisa irin wanda kona waiwaya babu abinda zan gani,sai dai cikin ikon Allah sai gashi na dawo farko,sai dai dan Allah ina roƙon ku akan abar abinda daya wuce,zai maida shi tamkar wani mugun mafarki ne dana taɓa yi a cikin barci na,kuma na tashi,dan Allah karku kuma niman yafiyata "

Gabaɗaya duk rungume ta suka yi suna masu hawayen farin ciki,

"Ina Abdulmalik?

" Nan suka shiga bata labarin ai shi ya bada koda aka saka mata dan haka yana ɗayan dakin na kusa da ita"

"Yaya amma ya akayi kuka san inda nake?

" Ai mijinki ne ya kira Abdulmajid ya faɗa mashi in da kike,sannan yace in zamu zo karmu zo dasu Mama saboda halin da kike ciki,koda zamu faɗa masu mu fara barin kiji sauƙi "

Wannan karon ko mamakin ta ne ya kasa boyuwa "ta yaya aka yi ya sanku har ya san number Ya Abdulmajid,sannan ya kira?

" Ya ce mana ya san komai akanki har da dalilin barin ki gida"

"In ji shi"

"Tabbas haka yace ranar da muka iso garin nan"

Shiru tayi kawai yayin da zuciyarta ta shiga tunanin dame_dame ya sani game da ita da yake kiran ya san komai game da ita,

Katse mata tunani Abdulrahman yayi da fadin "mijin ki mutumin kirki ne,ya karbe mu hannu bibbiyu,ban taɓa tunanin Allah zai haɗa ki da mutumin kirki irin wannan Salma,ya san mutunci da dattako,muna fatan Allah ya bar ku tare"

Bata bashi amsa ba sai ma cewa da tayi"ina yake?

Hannu Abdulmajid ya saka a Aljihu ya ciro wani Emvelop ƙarami ya mika mata"yace idan kin tashi a baki"

Amsa tayi tana warwarewa,tsirama rubutun shi ido tayi,yanda suka kwanta sosai a jikin takarda gwanin ban sha'awa,: *Assalamu alaikum,ina maki fatan samun lafiya mai ɗorewa,tafiya ya kamani,ki kula da kanki*:

Kara kallon wasikar tayi tana kara juyawa ko akwai wani rubutun ta baya da bata karanta ba,ganin babu komai ne yasa cikin yatsine fuska tace"Yaya iyakar wasikar kenan?

"Eh"

Cikin jin haushi ta dangwaran da wasiƙar a durowar wurin,

Kallon juna suka yi suna tambayar juna da ido ko lafiya,

Jin hayaniya na tashi daga bakin kofa ne yasa suka fita dan su duba ko lafiya,

Ganin wanda ke tsaye ne yasa Abdulrahman kallon Abdulmajid "ya zamu yi dashi"

Murmushi yayi yada dafa kafadarsa tare da faɗa masa wani maganar a kunni wanda banji ba sai gani nayi shima ya saki murmushi "to ai ba komai"

Kallon security wurin sukayi"ku bar shi ya shigo domin shima dan uwa ne"

Shi kanshi kallon mamaki yake masu domin bai taba tsammanin jin haka daga bakin suba,ji yayi wani sanyi ya lullube shi.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*77*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*

Hanya suka buɗa mashi"shigo mana,ka kuma tsaya kamar wani baƙo "

Murmushi yayi yana karasowa cikin ɗakin "na gode"

Jin muryar shi kaɗai ba ƙaramin saka mata bugun zuciya yayi ba,dan har sai da taji kanta ya sara,
Kamar yanda take kallon shi shima haka yake kallon ta,yayin da abubuwa da yawa suke dawo masu,

Wani irin abu ne taji ya sauko ya tsaya mata a zuciya,kauda kai tayi gefe,ji take kamar ta ɓace ta bar wurin,bata son tuno wasu abubuwan da suke dawo mata,sai dai tunda har ya kawo kanshi gare ta a wannan lokacin,bai kamata ta nuna gazawar ta ba,zata tayi amfani da wannan damar wurin nuna masu jiya da yau ba ɗaya bane,

A hankali ya karaso baki n gadon da take,harshen shi har tuntuɓe yake yi wurin faɗin "Partner ya jikin naki?

Sai da tayi tamkar ba zata kula shi ba kafin ta amsa " Alhamdulillah "

Ji yayi duk ta kara mashi kwarjini,sai yake jin shakkar yi mata magana kuma,dan gani yake tamkar ba Salman daya sani shekara biyar baya bane,wannan ta daban ce,duk da akan gadon jinya take da ka kalle ta kasan ita din macece mai aji,

Ganin ko kallon in da yake ba tayi ba yasa cikin sanyi jiki ya koma ya zauna kan kushin kusa da Abdulmajid da suka yi tamkar basu san da zaman shi ba,

"Abdulrahman nace ba,amma idan ta ji sauki zata koma Minna ne tare damu ko?

Wani kallon banzar ya watsa mashi" Ban sani ba amma gaka gata ai kana iya tambayarta "

Juyawa yayi ya kalle ta sai kuma ya dauke kanshi ba tare daya ce mata komai,

A hakan sai da suka yi zaman mintuna Ishirin babu wanda ya ƙara cewa komai,asali ma dakin kamar babu kowa acikin shi,
Jin yanda ya tsargu ne yasa ya tashi "zanje na dawo anjima" Babu wanda ya bashi amsa har ya bar ɗakin,

Juyowa tayi kansu"Yaya"

Dukansu lokaci ɗaya suku amsa suna juyowa,

"Kar a ƙara barin shi ya shigo"

"Me yasa? Abdulrahman ya tambayeta,

" Kodai har yanzun kina son shi ne? Abdulmajid ya ƙara jefa mata wani tambayar,

Ji tayi zuciyar na wani irin tafarfasa da suya,ta ma rasa wani amsa ya kamata ta basu,dan haka komawa kawai tayi ta kwanta ta juya masu baya ba tare da tace masu komai ba,

Kollo juna suka yi suna tabe baki,

Har sun cire rai akan zata sake yi masu magana,sai cewa tayi"yaushe yace zai dawo?

"Waye?

" Suraj"

"Ina ce ya fada maki komai a cikin wasiƙar,'

Juyowa tayi daga kwancen da take,cikin shagwabe fuska tace" Yaya,ni dai in kun dai na sona ku tashi ku tafi"

Makale dariyar dake taso masu suka yi,
"Oh Sorry ba haka bane,ta yaya zamu dai na son hasken idaniyar mu,Kin ga bai faɗa mana komai ba illa fada mana cewar tafiya ta kama shi,sannan ya bamu wasika mu baki"

"Amma shine baku hana shi tafiya ba?

Wannan karon ko buɗe baki suka yi suna mata kallon mamaki,

Ganin kallon da suke mata ne yasa ta kyaf_kyafta idanu tana ɗan turo baki gaba," To me yasa zaku bari ya tafi ya bar ƙanwar ku a kwance rai a hannun Allah?

"To me zamu masa?

" Well I don't now kawai dai naga bai kamata bane,sannan ko irin ku tambaye shi yaushe zai dawo baku yi ba,I am disappointed with you gay "

Da hannu ya nuna ta"you..

Maida kanta tayi ta kwantar tana kulle ido,

Ganin daga kulle ido bacce ya kwashe ta ne yasa suka fito suka komawa wurin Abdulmalik,

*Bayan Sati Ɗaya*

Alhamdulillah jiki ya fara warwarewa dan har ta fara dan takawa,sai dai abubuwa da yawa sun faru koma dai in ce suna kan faruwa,domin kullun sai Yusuf ya zo Asibiti sai dai ba mai hana shi shiga wurin ta,amma in ya shigo kuma babu mai kula shi har ya gaji ya fito,ba zai sa gobe kuma yaki dawowa ba,

Kamar yanda suka ma Kaka Alkawarin zasu je,basu samu zuwa ba dan sun roki Suraj ya basu number ta kuma ya basu,Abbulrahman ne ya kira ta da kanshi,ya bata haƙuri akan idan Salma da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login