Showing 96001 words to 99000 words out of 180103 words

Chapter 33 - NAGA TAKAINA COMPLET BOOK by Sadnaf.txt

Sadnaf   

17 Sep 2025

2497

ci burin samun kudi dashi ta siyi filaye.

Kamar ta fashe dan bakin ciki wata uku da tafiyar Naeema sai gashi abinda zasu saka a cikinsu Yana neman gaggararsu.

Safiyya kuwa data ga bazata iya ba aikatau taje ta nema a wani gidan masu kudi zata ringa zuwa tana dawowa daddare.

Idan taje abincin da ake Bata shi take kawowa gida taci Hajara na kallo idan tayi Magana kuwa Sai tace Mata kowa tasa ta fishe shi


Naseer kuwa Dan abinda ya fita ya Dan samo sabida tuni ya nemi aikin lebura na gini ya farayi Dan kudin daya samu yake siyowa su Zahira abinda zasuci ahaka ma sai dai shi ya hakura Dan bazai iya barin Hajara da yunwa ba.


Ahaka Safiyya tayi albashi Hajara tayi ta rokon ta Allah da annabi kafin ta yarda ta Bata wani Abun.

Tana Bata kuwa ta siyo shinkafa da kayan Miya ta girka ta kakasafta a kwanu.

Zahira na dawowa daga makaranta tasa ta cire uniform ta Dora Mata farantin

Ta bawa Nadeeya Yar robar miyan tace musu su dau hanya su tafi su siyar Mata taja musu kunne akan kar su sake su dawo gida batare da sun siyar Mata ba idan Naseer ya Isa idan ya dawo ya mata magana yaga yanda zata Yi dashi

Suna fita ta dakawa Minal tsawa Akan su saka kayan islamiyya su tafi.

Minal sai data Dan gwada Mata taurin Kai ta dan bubuge ta kafin suka bar gidan.

Naseer dake ta Dora bullo a wani gida da ake ginawa kamar ance ya daga kansa ya hango Zahira da Nadeeya na tafe a Gefen titi suna rarrabewa a gefe ga uban faranti akan Zahira ga Nadeeya itama da nata robar miyar.

Naseer Bai San sanda ya duro Yana mirtsika Ido ba Dan ya tabbata da su Zahira yake gani.

Jiki na rawa ya Isa wajensu.

Ya sauke farantin dayake ganin yayi wa Zahira nauyi yace musu waye ya Dora musu talla.
Ce Masa sukayi Hajara ce.

Yayi shiru Ransa na balain baci.

Dak'yar ya hadiye b'acin Ransa yace su zauna a wani dakali su jira shi Yana zuwa.

Ba a cikin hankalinsa Suka karasa aikin ba Dan har sai da bulo ya Fado Masa a kafa Sabida tunani.

Ana biyansa kudinsa ya wanke jikinsa ya cire kayan aikinsa ya maida Mai kyau jikinsa.

Ya tsallaka wajen su Zahira ya d'auki farantin abincin.

Ya rarrabawa almajirai

Ya Kama hannunsu ya tare musu bus Suka hau suka nufi gwammaja.

Bashida tabbacin Gane gidan Tijjani Amma ahaka yaje sai da kyar ya Gane gidan da kwantance.


Suna zuwa k'ofar Gidan Tijjani na isowa a vespa.

Ko parking baiyi sosai ba ya duro daga vespan Dan murna ya rungume Naseer cikin murna


Naeema


Kwana biyu kawai nayi a garinmu danaje da Ashe sun Dade suna nemana sosai naji mutuwar Mai unguwa da nake Jinsa tamkar mahaifina ashe shekara daya kenan da rasuwarsa

Kafin rasuwarsa ya siyar da gidanmu ya boyemin kudin Dan lokacin sosai ake San siyan gidan hayan daya saka kuwa sai yaga ma.kamar mutanen ciki Bata gidan suke hakane yasa ya siyar da gidan Akan duk lokacin da Nazo zai bani ya kuma San bazanji Haushin siyarmin da gidan mu da yayi ba

Dubu dari uku da sabain ya siyar da gidan namu.


Kafin rasuwarsa Haka yayi ta rokan yayansa da matansa akan Dan Allah Kar su tabamin kudina duk lokacin Dana Zo a damka min kudina.


Sosai naci kuka na Godewa Allah da rashin Mai unguwa a Haka na kwana biyu cikin zuciyata ba dadi uwa uba ga tunanin yarana daya dameni ko baccin kirki bana iya yi sabida Ina tunanin kamar suna can suna Shan duka a wajen Safiyya abinda zai taimakeni kawai shine Kila Naseer bazai yarda a tab'a min su ba da Wanan tunanin hankalina ke Dan kwanciya.

Sosai iyalin Mai unguwa suka nunamin soyaya Dana tashi dawowa Dan Kaya Suka bani sosai na amfani Dan ban Gaya musu abinda ke faruwa Dani ba.

Karfe uku na rana na iso gidan kanwar Aunty Ina zuwa kuwa na tada Aunty a gidan.

Bazan manta Aunty a rayuwata ba tamin abunda har na mutu bazan manta alherinta a gareni ba.

Ina sallahr La'asar muka nufi dorayi da ita.

Ta kaini gidan data kama min ta hau min bayanin da kyar Mai gidan ya yarda ya bada haya Dan yace siyarwa zaiyi Amma ko yanzu ya samu Mai siya zai maidamin kudina ne na siyar.

Gidan Mai kyau ne dakuna biyu da bandaki biyu da Palo sai dan karamin shago a k'ofar gida

Gwada tambayarta nayi nawa ne gidan.

Tacemin Dubu dari uku da ashirin

Take nace Mata Zan siyi gidan Kamar Wasa ta rakani wajen Mai gidan na nemi ya siyarmin Dubu dari biyu da hamsin dak'yar ya siyar min a Dubu dari biyu da casain

Washegari muka Kai Masa kudin gidan ya d'auko takarda gidan ya bani

Aunty sai murna takemin ni kuwa sai tambayarta nake tana ganin yarana cemin tayi tana ganinsu kar na damu Naseer na kula dasu Dan ta saka Ido a kansu

Take naji hankalina ya Dan kwanta.

A. Cikin kwana uku naja wutan.nepa gidan

Aunty ta Nemo min Katifa second hand na biya da Dan ledar tsakar daki da Dan kayan amfanin gida da bazaa rasa ba.

Wata Hassana da take bazawara da ta kasance Yar uwarsu ta kawomin Akan mu ringa kwana tare Dan Ina tsoron kwana Ni kadai.


Hassana kuwa zata iya girme min Amma tana da kirki

Makotana na zaga na Dan duba abinda baa samu unguwar Naga har da dai markaden sai sunyi tafiya Mai nisa suke samu.

Ana Kuma neman ruwan Sanyi kayan provision ma sai sun Yi tafiya Mai nisa.

Take kuwa na nemi engine second hand na siya Dan gaskiya Ina San sanaar markaden dan ya shigomin da kudi

Cikin Ikon Allah kuwa sati daya da siya aka faramin layi.

Dan har Hassana Tayani takeyi idan na gaji.

Kamar Wasa sauran kudin hannuna na Nemo kafinta ya bubbuga min canter na Dan zuba provision din kad'an su Maggi biscuit bredi da alewa da littattafai makaranta Dan Naga Ana yawan nema


Shima sati da fara siyar da provision din Rabbi ya Sanya min albarka a hankali sai gashi shagon k'ofar gida ya cika da kaya.

Sai gashi a cikin wata biyu har freezer na siya shima na saka a shagon Ina siyar da ruwa.

Nikam a wanan gabar sai dai nace Alhamdulillah Dan kudi ko ta Ina shigomin suke abinda yake damuna Bai wuce kewan yarana danake kwana Ina mafarkinsu ba wani zubin a mumunan yanayi wanan Abu shi yake hanani sukuni ko abinci bana iya ci.gashi dai komai na samu cikin rufin asiri Amma tunanin yarana ya Sakani balain Rama Nafi tunanin Zahira Dan jikina na gayamin tana Shan wahala a hannun Umma da Safiyya Koda kuwa Naseer na nan.

Sau uku Ina zuwa unguwar da likkaf na tsaya a k'ofar gida Naga ko Zan ga wani ya fito daga gidan a cikinsu sai dai bana ganinsu sai dai Naga Naseer daya balain Rama ya fita hayyacinsa sosai yake karyamin zuciya idan na ganshi ahaka zan karaci tsayuwata idan na gaji na karasa gidan Aunty tacemin Kar na damu dazu ma tagansu lafiya Lau suke ba Abunda ya samesu har tambayar Zahira tana yi dake da balain zurfin ciki tace mata ba komai.

Ahaka Zan dawo da tunaninsu a Raina Nima rashinsu kusa Dani ne ya saka Ni mugun Rama Dan Sana'ar tawa Dan hassana na rik'ewa ne da bazan iya tab'uka komai ba a yanzu da aka tafi wata uku rabona da yayana naji bazan iya jurewa ba Ina bukatar ganinsu ko ta halin Kaka hakane Yasa na yanke zuwa gidan aunty idan sun zo islamiyya nagansu Koda daga nesa ne.


Naseer..........
8/19/21, 10:32 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*

*NA SADNAF*🌸🌸


®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_



*Free Novel*


*Page 37*


*Naseer*

Tijjani cikin tsananin murna ya rik'e Hannun Zahira da Nadeeya yace su Shiga daga ciki

Naseer ya girgiza Masa Kai Akan bazai shiga ba ya dai Shiga da yaran ciki su gaida Murjan

Tijjani girgiza Kai yayi Yana wlh sai ya shiga ciki Taya ma zai Zo gidansa Bai Shiga ba


Akan dole Naseer ya yarda suka shiga ciki Tijjani sai washe baki yake cikin murna.

A tsakar gida Naseer ya coge.

Tijjani kuwa sanin halinsa yasa ya dau babbar tabarma ya shimfida Naseer ya zauna shi ma ya zauna ya hau kwalawa Murja Kira Su Zahira kuwa sai kalle kalle suke suna daga gefensa hannunsa cikin Na Nadeeya.

Yana tambayarsu Makaranta

Murja fitowa tayi tana Hamma da cikinta da baifi na wata biyar ba ta tsani tana bacci a tasheta ko kad'an batasan da zuwan su Naseer ba hakane yasa ta fito da Daurin kirji

Ganin Kuma Naseer Bai saka ta koma ba illa yatsina fuska da ta farayi tana karewa Su Zahira kallo da Tijjani keta washe baki yana cigaba da Jan su Zahira da Hira Naseer kuwa kansa a sunkuye yake so yake idan matar gidan ta fito su ka gaisa sai su fita da Tijjani waje suyi magana dake tafe dashi.

Tijjani kuwa sai daya d'ago yaga Murjan ta daga labule daga bakin kofa ta toge

Daga yanayin ta yasan Yan rashin mutunci ne Suka motsa hakane yasa ya mik'e ya Shiga ciki tare da Jan Murja su koma ciki yayi kasa da murya Yana "Ya Ina kiranki kizo ki gaisa da yayana zaki kame daga bakin kofa shine fa yayana Naseer danake baki labari wadanan yayansa ne Dan Allah ki Sako hijabi kizo ku gaisa


Bata ce komai ba ta koma daki ta sako hijabin a rayuwarta ko kad'an Bata so wani ya rabesu har Tijjani ma bataso.taga Yana muamalla da mutane Dan ko abokaina ma cikin makirci take rabasu.

Idan kaga wani a gidan toh danginta ko kawayenta ne Amma Tijjani kam bataso wani nasa yazo wajensa hakane yasa ta Sha mugayen alwashi idan tsautsayi ya sa su Hajara suka Kara dawowa gidanta sai ta musu abinda har su koma ga Allah bazasu manta da ita ba.


Tijjani kuwa Yana fitowa Bai tsaya jiran fitowar Murja ba Dan ya Riga da yasan halinta ruwa da abincinsa ya d'auko yazo ya Ajiye a gabansu Naseer Yana yayi hakuri yanzu murjan zata fito yasan halin masu ciki.

Daga Nan ya dau plate ya bud'e flask din ya hau zuba shinkafa da wake da akayi jollof dinsa da bushashen kifi

Murja kuwa har wani turus tayi dan bakin ciki Dan tana da balain rowa ko wani ne ma yazo daga gidansu Haka zai karaci zamansa ya tafi batare da ta Masa tayin abinci ba ko da kuwa Tana cikin girkin kazo zata iya gwammacewa ta zauna da yunwa har sai ka tafi.

Dak'yar ta saki Fuskarta
Ta tsugunna daga bakin kofa ta hau gaida Naseer cikin faraa

Naseer kuwa ya d'ago ya amsa cikin sakin fuska Yana Dan karantar yanayin Murja a fuska dai Kamar babu ruwanta zatayi saukin Kai hakane yasa ya Dan ji sanyi a Ransa

Bayan sun Gama gaisawa ta koma ciki ta lab'e a jikin labule tana kallon

Zahira da Nadeeya dake ta zabga Loma Sabida yunwar da suke ji Dan uniform kawai suka cire Hajara ta Dora musu talla Bata Bari sun ci abinci da Naseer ya boye musu a daki ba dan waje na musamman Naseer yake boye musu abinci a d'akin da iya su zahiran ne kawai zasu San abinci ne a wajen sabida Kar ma Hajara ko Safiyya suzo d'akin su dauke

Kamar ta fashe Dan bakin ciki shi kuwa Naseer ture abincin da Tijjani ya ajiye daga gabansa yayi ya gyara murya ya Dan fara bawa Tijjani labarin duk halin da yake ciki da tafiyar Da Naeema tayi Sabida masifar Mahaifiyarsu da yanda itama Safiyya take cin zalin yaransa har zuwa Kan tallan da Mahaifiyarsa take dorawa yaransa da yasa ya zarto gidansa dasu.


Tijjani shima labarin irin zaman da sukayi da ita ya bashi a karashe da "Wlh Naga bazan iya ba nace su tafi Dan wlh bazan iya jure abinda kake iya jurewar ba Umma a madadin ta ringa rike girmanta tana kwantar Mana da hankali sabida halin da muka tsinci kanmu na babu wanda duk ita ta jawo Mana fa hakan Bai isheta ba sai ta daga Mana hankali ba irin surutan da bata yimin Akan na rabu da Murja ba daga Aurenmu fa Ni ban taba ganin Mai irin Halin Umma ba wlh ita Kuma shegiya Safiyya a madadin ta ringa Gaya Mata gaskiya shine take tunzurata kamin daidai da ka Hana ta dorawa su Zahira talla Dan nikam bama Zan iya da ita ba Dan da nine ma wlh siyar da gidan zanyi na gudu da yarana k'arfi da yaji kana zaune kalau da matar rufin asiri ta rabaku toh Yaya yanzu wane aiki kake yi Taya zaka ringa aikin lebura dake da wahala nawa ma kudin yake da zai isheka ka kula da yaran nan.mai zai Hana ka nemi aiki wani wajen ko Allah zai saka ka Dace Kamar yanda Nima Allah ya taimakeni na samu aiki a wani company robobbi a sharada duk sati suna bamu Dubu biyu karshen wata Kuma su biyani Dubu goma da zaka samu irin wanan aikin Yaya nakega da yafi nima wani ne ya nemo min aikin Zan Masa magana idan Allah yasa. An Dace sai Kai ma ka ringa zuwa da Wanan aikin wahalar da kakeyi.

"Tijjani Ina neman aikin samun ne dai banyi ba bazan iya kirga guraren Dana Kai takarduna ba Amma har yanzu baa Dace ba ya zanyi dole na ringa leburancin mu samu na abinci.

Yanzu dai abinda yasa nazo wajenka so nake ka taimaka min Dan Allah Yaran Nan su zauna a wajenka zuwa Dan wani lokaci kafin na Shawo Kan Umma Dan wlh bana San tallan Nan duba kaga Zahira ta girma dan ma Bata da girman jiki Amma kana gani kasan ta fara Zama budurwa Taya Zan yarda a ringa Dora Mata talla Zahira da Nadeeya Umma tafi takura wa hakane yasa nace Bari na kawo su wajenka su zauna Ni Kuma yanzu idan na koma Zan nuna kamar bansan Inda suke ba kaga idan an kwana biyu sai nazo na daukesu Kamar angansu ne inaga hakane kawai zai saka Umma ta hakura da tallan da takeso suyi na k'arfi da yaji.


Naso Naeema data tashi guduwa ta tafi da ko iya zahiran ne Ni Kuma bana San bin Bayan ta sabida Naeema tayi.hakurin da Umma koni bazan soma bin bayanta nace ta dawo ba gwara ta huta idan an kwana biyu sai na Kai Mata yaran intaga zata rikesu shikenan idan taga bazata iya ba sai mu dawo

"Yaya ba sai ka hadani da Allah ba yaran Nan nima yayana ne Nan ma gidansu ne sauran ma idan kana ganin Umma zata takura musu ka kawo su wlh Zan rik'e su yanzu Ina cikin rufin asiri abinda zasu ci bazai gagareni ba insha Allahu Umma Kuma Allah ya shiryeta sai dai makarantarsu ne bansan ya zaayi ba tunda kace Zahira na primary 4 Kuma 3rd term

"Hakura zasuyi na Dan lokaci kafin komai ya warware zanje makarantar da kaina Tijjani Nagode sosai da taimakonka a gareni Zahira da Nadeeya kawai nakeso su zauna anan Dan su tafi matsawa gobe zan dauko musu kayansu a boye na kawo musu insha Allahu sai dai ka taimaka min Kar su zauna haka su ringa zuwa islamiyya Dan Naga kamar akwai makarantun islamiyya a layin naku

"Haba Yaya wlh bazan iya biyanka alherinka a gareni insha Allahu baka da matsala Kaya ka barshi Zan siya musu Koda gwanjo ne basai ka wahalar da kanka ba Zan Kuma saka su a islamiyya Ina samu kudi har bokon Zan iya saka su insha Allahu"


Dafatan matarka bazata damu ba Dan bana San na takura ta

"Haba Yaya wlh bazata damu ba ai Tama samu Yan tayin hira tana da san mutane sosai"


"Tabdijam"

Murja tace bayan ta Gama Jin duk abinda sukace

Ta nufi d'akinta a fusace

Naseer kuwa yayi ta yiwa Tijjani godiya

Ya mike akan zai tafi ya Kira Murja ya Mata sallama.

A daki ya tadda Murjan tana kad'a kafa ko lura da Fuskarta baiyi ba yace ta fito suyi Sallama yayansa zai tafi

Daga hakanya saki labulen yayi waje

Murjan ta bishi a baya tana kakalo faraa tana fitowa tayi kasa da Kai tana "Har zaku Tafi"


"A uwargida Ni Kadai Zan tafi dai Su Zahira zasu Dan zauna su kwana biyu sabida wani Dan dalili dafatan Dan Allah ban takuraki ba" ?


"Haba Yaya wane irin takura Nan ma ai gidane karka wani damu"


Godiya Naseer yayi ta yiwa Murja.

Murja kuwa har da rike hannun Nadeeya suyi rakiya har waje.

Sai da suka daina hango su Tijjanin da suka hau Vespa Dan ya fita dashi titi

Murja naganin sun wuce ta yarfar da Hannun Nadeeya ta ja baya tare da musu wani irin Mugun kallo tana "Yan bura uba daga zuwanku sabida kwadayi zaku hau cinye min abincin Dana girka shegu dangin kwadayi zaku ci.ubanku ne Dani kuke maganar Haka kawai Ina zaman zamana a kwaso.min gayya Yaya har guda biyu Uwarku ma ta kasa rikeku ta gudu shine Ni aka rainawa wayo.zaa wani kawoku wajena shi Kuma Tijjanin zai Zo ya sameni Kuma wlh kun Gama cin rabonku"


Daga Haka ta wuce daki fuuu tana bakin cikin abincin ta da suka ci sosai ta ringa shirya ukubar da zatayi wa Yara da basuji ba Basu gani ba Wanda idan sukaji azaba da kafarsu zasu gudu.

Zahira kuwa kuka ta fara yi Nadeeya kuwa na kikifta Ido Zahira duk da kankantar shekarunta gani take Bayan mahaifiyarsu da mahaifinsu Babu Mai kaunarsu har suna murna zasu zauna a gidan baba Tijjani da suke ganin kamar sai sunfi jinn dadin zaman Nan Akan gidansu sai dai daga yanda Murja ta musu yasa Zahira taji dama sun bi Bayan mahaifinsu.

Tijjani kuwa Yana fita da Naseer bakin titi ya d'auko duk kudin jikinsa ya bashi ya kara Masa alkawarin idan ya samu sarari zai Zo idan sukayi albashi.

Godiya Naseer ya Masa sosai ya tari bus da zai je gadon Kaya ya hau

Tijjani Kuma ya juya ya koma gida

Murja tana Jin karar vespa ta duro daga Kan gado tayi waje tayi wajen da su Zahira ke rab'e ta ruk'o hannun su biyun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login