Showing 117001 words to 120000 words out of 180103 words
kayan daki karki manta fa wanan gidan kadai ya rage mishi muma ba Dan gidan Nan ba da yanzu muna titi muna gararamba"
"Toh idan ba a siyar ba Umma da uwar me za'a min kayan dakin tambayar ki nake idan baa siyar ba da uwar me zaamin kayan d'akin"?
Safiyya tace a tsawace
"Naga duk masifar Nan ke Kika janyo mana muna zaman zaman mu Kika k'ona dukiyar Yaya Naseer ya talauce muka Shiga uku yanzu da baki Kona dukiyar sa ba ai da Yanzu Bai gudu akan kin Masa maganar yamin kayan daki ba Dan Haka wlh gidanan zaa siyar kawai ayimin kayan d'aki"
Kamar Mai tsoron Safiyya Hajara tace "toh idan mun siyar da gidan Nan Safiyya a Ina zamu koma da.zama nida Naseer din tunda nasan sabida zakije gidan miji kike cewa mu siyar da gidan nidai nasan wanan gidan yanzu shine rufin asirina Dana Naseer tunda Naeema ta Kara gaba da yaranta"
Sai a lokacin ta sasauta Fuskarta tana "Umma ai wani karamin gidan zamu siya idan muka siyar da Wanan Kinga gidanan babba ne zaa siyi gidan da daraja a ciki zamu siyi karamin gida ki siyamin kayan daki sauran kudin Kuma kija jari kafin ki ankara kema kin zama hajiya har macca ma sai kije ki Naseer dawowa yayi idan yaganki da kudi bazai yi magana ba kinsan shi ba Kamar Yaya Tijjani ba"
Washe baki Hajara tayi Dan maganganun Safiyya sun shigeta ta Kuma Yi naam da shawarar ta
"Toh wa kike ganin xai siyi gidan"
"Ki bar komai a hannuna"
Safiyya tace cikin murna a ranar ta shiga d'akin Naseer ta birkita Kaya har sai data samo takardun gidan
Ta fito sai murna take da zaa samu kudin da zata siyi kayan daki ya zama Dole ma ta koyawa kishiyarta hankali Dan Kaya zatayi na fitar hankali da kishiyar ta zata shak'a sosai take Jin dadi da had'asu waje dayan da zaayi tasan kishiyarta sai ta kwashi kashinta a hannu Dan sai ta bar Mata gidan ta mallake shi ita kadai.
Washegari da sassafe ta bazama ta Nemo dilalai a cikin kwana biyu aka samu mutane masu San gidan har su uku.
Dan gidan Naseer din babba ne kuma a fuska Mai kyau Safiyya Bata yarda anyi cinikn gidan Agaban Hajara ba ita ta saka hannu akayi komai da ita Akan Dole ta Nemo wasu Suka Mata shaidan ta siyar yanzu ba mallakinsu bane ta Basu kudi Suma masu siyan gidan suka bada kudi da shaidunsu suka karbi takardun gida.
Sai da Safiyya ta zabtare kudin wajen rabi ta b'oye.
Ta Kai sauran kudin gaban Hajara.
Hajara dai tana San magana kudin gidan yayi araha da yawa Amma babu yanda zatayi da Safiyya datayi Kane Kane.
Safiyya ita ta raba kudin gida biyu ta dauki iya kudin da zai isheta ta siyi kayan daki da komai
Ta bawa Hajara sauran Hajara kuwa sai a lokacin tace "Safiyya kudin Nan bazai Isa mu siyi wani gidan ba ballantana har na samu na jari"
Karki damu Ni Zan Nemo miki gidan da kaina zaa samu
Jiki a sanyaye Hajara tace "toh yaushe masu gidan suka ce mu tashi nidai Safiyya ba Haka naso ba wlh gidanan babba ne wayanda Suka siyi gidanan sun cucemu"
"Notice din wata daya suka bamu karki damu kafin lokacin na samo Mana wani gidan
Ahaka ta lallab'a Hajara tayi shiru.
Kafin sati daya da tafiyar Naseer har ta Gama siyan kayan daki na gani na fad'a
Iya Nan Bai isheta ba sai data tab'a kudin da ta bawa Hajara data Masa kyakyawan b'uya shirye shiryen bikinta kawai daya rage sati biyu take tana facaka da kudi har wani karamin lefe tayiwa kanta Hajara idan tana San tayi Magana sai ta hayayyako akan Dole take shiru.
A ranar da Naseer ya koma kuwa sosai Hajara ta tsorata Dan Bata kawo zai dawo kurkusa ba ta d'auka dagaske guduwa yayi.
Safiyya kuwa kwantar Mata da hankali tayi akan Kar ta sake ta gayawa Naseer sun siyar da gidan.
Sai idan sunzo tashi shima idan yasani ta haharde Rai ta Masa fin k'arfi tuni zai mata biyaya.
Naseer kuwa sosai yayi mamaki da Hajara Bata tambayeshi Inda yaje ba sai wani susune Kai take.
Shi kuwa dadi yaji yace Mata Abuja yaje neman kudin da zaiyiwa Safiyya kayan daki toh shima yaje Bai samu ba sai Yan canji ya samo tayi hakuri zai cigaba da nema
Kai a sunkuye Hajara tace Kar ya damu ta siyawa Safiyya komai.
Wani irin dadi Naseer Yaji yace Mata Ina ta samu kudin
Tace Kar ya damu zai sani a hankali
Naseer kuwa har a Ransa yaji dadin ganin Hajara ta Dan sauya Masa Ashe har ta samu kudin kayan d'akin.
A ranar zuciyarsa fes batare da wani fargaba ba ya kwana da tunanin iyalinsa
Washegari da safe yaje gidan Naeema yake Gaya Mata duk yanda sukayi da Hajara
Nidai sosai nayi mamakin Inda Umma ta samu kudin.
Haka kawai jikina ke gayamin akwai dai ta hanyar da aka samu kudin bandai cewa Naseer komai ba danaga yanda yake murna Yana cemin ko fada Umma Bata Masa ba kila Allah ya fara karbar adduarsa.
Bandai ce komai ba a ranar ya wunar Mana daddare na raka shi ya tafi
Yawan zuwa da Naseer keyi gidan Naeema yasa Sam bai San halin da ake ciki ba dan Yan canjin daya samu ma shinkafar da Hajara zatayi taron biki ya siyo Mata har da yiwa Hajara dinki kala biyu wai duk Dan ya faranta Mata.
Hajara kuwa damun Safiyya ta ringa Yi da zancen gidan data ce zata siya musu Dan lokacin barin gidansu nata karatowa Amma Safiyya haka ta ringa tsara Hajara tana d'auke mata hankali daga zancen Dan tabi ta Kan kudin tuni burinta kawai a daura auren
Ta bar gidan Hajara da Naseer su San nayi tunda ita dai ta samu cikar burinta.
A Haka aka fara bikin Safiyya Tijjani ma yazo bikin da Murja Dan tuni sukayi katon aiki Akan Tijjani har sai daya je har gidansu Murjan ya dawo da ita.
Duk da kamun da suka Masa ba sosai ya Kama shi ba
Hajara kuwa irin gayyar da Safiyya tayi yasa hankalinta ya d'auke daga zancen gidan Bata Kuma bi takan Murja da suke Yar kallon kallo ba
Sai da aka zo tafiya da Safiyya washegarin daurin Aure.
Hankalin Hajara ya dawo jikinta daki ta ja Safiyya ta hau Mata maganar gidan ita kuwa Safiyya ta Mata karyar ta siyi gidan anjima wani zai zo.ya kaita taga gidan
Hajara badan ta yarda ba tana ji tana gani aka tafi da Safiyya mutane Suka watse ya rage saura ita daya da Naseer.
A lokacin saura sati daya notice din da aka basu ya Kare.
Kamar tayi kuka ta Shiga d'akin
Naseer Kuma ya Shiga har d'akin ta daya hada musu abin karyawa ya Kai Mata Yana "Umma lafiya kuwa Yana ga kamar bakida lafiya"?
Hajara na k'ok'arin Magana
Wani yaro ya doka Sallama Wai Mai gidan Yana Sallama da Safiyya
Gaban Hajara ne ya yanke ya Fadi.
Naseer Kuma cikin mamaki yace "Mai gidan kuma waye Haka"
Yayi waje Dan yaga Mai sallamar......
8/19/21, 10:32 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*🌸🌸
®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
*Page 45*
Da saurinsa ya Isa wajensu ya rik'e hannayen hafsa dake ta buga Kan Safiyya da kasa Dan karfafa ce ita Bata Wasa ba
wani zubin shi kansa Umar din idan Abu ya hadosu tana Masa mugun duka idan fada ya kaure musu.
Safiyya dafe keyarta da takejin lema tayi da alamar.jinine ta mik'e da kyar tana jiran Umar ya d'auke Hafsa da Mari sai dai a madadin Marin sai ya hau Bata hakuri Yana rarrashinta.
A wahalce Safiyya tace "Umar kanka daya kuwa Taya zaayi matarka daga kawoni yau ta hau dukana amadadin ka tsawatar Mata sai ka hau Bata hakuri"?
Ko kallonta baiyi ba ya cigaba da bawa hafsa hakuri dake cika tana batsewa.
Mamaki yasa Safiyya wartsakewa daga azabar da takeji a keyarta
Dan Umar din ma hannun Hafsa yaja suka Shiga bangarenta suka rufo k'ofar batare da ma ya Mata ko kallo daya ba
Safiyya kasa ma motsi tayi sabida tsananin mamakin abinda Umar din ya Mata gani take Kamar ba Umar din data aura bane.
Sai da Sauro Suka fara kaiwa fatarta cizo ta koma bangarenta da mugun ciwon Kai ga mugun yunwa da takeji ga ba abinda zata saka a bakinta a tsakiyar palon ta zub'e tana tunanin abinda zai saka Umar ya Mata Haka a Daren ranar da ta tare a gidansa da yake ta dokinta kamar ya cinyeta.
Gwallo Ido tayi data tuna kwallinta data manta dazaa daukota hannu ta Dora aka Dan kwallin Nan shine yake balain tasiri a wajen Umar yau kuwa ko kwallin Bata saka ba.
Ya Zama Dole ta nemi shugabarsu tunda tana garin calabar zata nausa daji nemanta ta Kara Bata kwalli tare da damke Mata Umar ta kuma cin uban kishiyar Nan tata Mai Kama da maza sosai ta zargi kila sabida bata saka kwali ba shiyasa Umar ya wulakanta ta batasan shi kansa Umar din sai yanda uwar gidan sa tayi dashi ba.
A ranar Bata iya bacci ba sabida mugun yunwar da takeji ga azabar ciwon Kai Dan keyarta ya kumbura yayi suntum.
ruwa kawai ta ringa dirkaka wa kanta cikinta na Kara kullewa.
Wajen karfe shidda na asuba baccin wahala yaso ya d'auketa.
Har ta fara baccin sama sama taji an banko k'ofar dakinta da balain k'arfi.
Mik'ewa tayi a firgice Dan ta balain tsorata.
Hafsa ce ta shigo cikin kayan bacci har kasa kanta a bud'e Yana ta digar ruwa.
Cikin wani irin murmushi hafsa tace "Amarya dafatan kin tashi lafiya baccin ya Isa Haka a fito a Dora Mana abincin karyawa Dan Yara zasu tafi makaranta Dan nasan kinsan Yana da Yara masu zuwa makaranta dole zasuci abinci kafin su tafi makaranta".
Wani irin Mugun kallon tsana Safiiya ta kwashe Hafsa da shi tana "Juya ki barmin daki kafin na tureki da kaina uwar abincin Zan dafawa Yara ba abinci ba ke da kwana da miji Ni da dafawa Yara abinci kin dauka Yar aiki aka kawo Miki wlh bashi kikaci duk abinda Kika min sai na Rama bakisan waccece ni bane kina Wasa da wuta Bari na kamaki"
Wani irin Dariya Hafsa ta kwashe dashi tana "Zaki sha wahala idan kikace zaki ja Dani a yau Zan tabbatar.miki da ke Yar aikin ce tunda har.kika auri mijina idan Kika min gardama Kuma wlh na Miki shegen duka da kafarki Zaki bar gidanan"
Ta juya ta fita daga d'akin Safiyya kuwa ta buga uban Tsaki Tana Shan alwashin gari na wayewa zata tafi wajen shugubarsu Kuma indai taje sai ta saka an kashe Mata hafsa.
Fitar Hafsa da Yan mintina sai Gata ta dawo da Umar daya balain had'e Rai ya saka doguwar rigar maza
Safiyya kuwa Ido ta zuba Masa tana mamakin yanda yake mata wulakanci Agaban kishiyar ta duk da tasan idan ta saka kwalli Yana rikicewa akanta Amma wani zubin Bata saka kwalin idan yazo Kuma Baya canja Mata haka.
Fuska a had'e yace "Ki tashi ki Dora wa Yara abin karyawa Dan zasu tafi makaranta sai kinyi kwana bakwai Zaki ajiye girki kafin hafsa ta karba"
"Idan ni kuke jira na Dora muku muku abinda zakuci wlh sai dai ku mutu da yunwa yaushe kuka tab'a Jin daga auro amarya ta fita ta Dora girki.naga ma ba a d'akina ka kwana ba akan me.zan Dora girki wlh Umar ka bani mamaki ban taba sanin Haka. Kake ba wlh Allah ban taba sanin wulakanta ni kakeso kayi ba shiyasa ka auroni agabanka wanan shegiyar matar taka Mai zubin maza ta Dokeni"
Jinta ne ya d'auke na wucin gadi Sakamakon Marin da Umar din ya d'auke ta dashi Yana "daga yau karki sake ki Kara zagarmin Mata idan kina San zaman lafiya a gidanan ki tashi ki dorawa yarana abinci karyawa karsu makara zuwa makaranta"
Umar yace a fusace Yana barin d'akin Hafsa kuwa cikin wani irin murmushi ta karasa gaban Safiyya dake dafe da kumatunta har lokacin sabida tsananin mamaki Marin da Umar ya Mata tace "Baki ga komai ba wlh da kafarki Zaki bar gidanan Dan mijina yafi karfinki na Gaya miki ba yanda zaayi sama ta kizo ki aure min miji alhalin bakisan wuyan Dana Sha dashi ba"
Daga haka ta fice daga d'akin
Safiyya ta zub'e kasa ta fashe da kukan bakinciki.
A takaice a cikin kwana bakwai da Kai Safiyya tayi wani irin Rama tayi wurjan wurjan Dan duk Inda take tunanin Hafsa ta wuce Nan Dan muguwa ce ta karshe horar yunwa da take Mata yasa ta yarda ta fara girkin duk Yan gidan Sabida ta samu na abinci
Nan ma idan ta girka Hafsa ke zuwa ta juye a babban kula ta bar Mata kanzo ta kankara Dan kudin Hajara data kwaso ma yaranta sun bita har d'akinta sun kwashe ballantana ta siyawa kanta abinci
Duk yanda taso fita Umar ya hanata Dan mugunta ma Safiyya kulle gidan take idan ta saka ta aiki tak'i sai ta jibgeta.
Yaranta ma a palonta sukacin abinci su Mata kaca kaca da Palo da daki Bata Isa tayi Magana ba da mugunta ma yaran Suka fafarka kujerunta da Reza da Zuciya ya d'ebbeta hade Yaran tayi ta zanesu dayake sabida bakin cikin ganin tsadaddun kujerunta da suka yaga
Sai dai yaran na fita sai ga Hafsa Nan daga k'ok'awa ta Mata shegen duka ta kumbura Mata fuska tundaga ranar Bata Kara gigin tab'a yaran ba
Tana ji tana gani yaran Hafsa ke wulakanta Mata Kaya
Bata isa tayi magana ba kuka take ci sosai tana nadamar ma auren Umar din dan gwara Zamanta ba auren da irin wanan kuntacecen rayuwar da take sati daya da kwanakin da ta tafi ji take kamar tayi shekaru a kurkuku ta Sha yunk'urin guduwa daddare Hafsa datake cewa Mayya na dawo da ita Dan Hafsa so take sai ta azababtar da ita kafin tasa Umar ya saketa.
Dan ba karamin kamu tayiwa Umar ba,Bai Isa ya ketare umarninta ba
A yau ma Kamar yanda Hafsa take tilasta Mata aikin gidan.
Ta fito Ana iddar da sallah asuba ta fara aikin gidan.
Da gayya ma yaran da suka jiku da makirci ke B'ata katon gidan ta share ta goge ta zo ta Dora babban tukunya ta Dora musu abinci
Ita kuwa hafsa Haka zata fito da jikakken Kai tana Mata murmushin mugunta Dan Umar sau uku kenan Yana kwasheta da Mari idan ta Bijirewa umarnin Hafsa zuwa yanzu ba abinda ta tsana sama da zaman gidan auren dan tayi auren ne Dan taji dadi sai gashi tana Shan wuyan da ko a mafarki Bata tab'a hasasowa.kanta ba muryar Hafsa kawai fadar.mata da gaba yake
Ahaka ta Gama abincin Hafsa ta juye ta bar Mata kanzo ta kankara taci ta Kara wanke wanken
Yaran Suka
fita gabadaya har da Hafsa.
Sosai Safiyya taji dadin fitarta ta Shiga d'aki da Sauri ta d'auko mayafinta ta fita itama.
Duk da nisan dajin da suke zuwa wajen shugabarsu ahaka ta Nadi tafiya Mai nisa tana Isa bukkar ta hau yaren tsafin su sai dai har ta Gama babu shugubarsu babu dalilinta.
Kamar tayi kuka ahaka ta fito daga dajin ta koma gida tana Shan alwashin kwashe Kayanta ta tafi Dan bazata iya cigaba da zaman bauta ba.
Sai dai tana dawowa ta tarar Da Umar a d'akinta.
Ya wani marairace ya hau Bata hakurin Bai San Mai ya hau kansa ba a takaice a ranar ya kwanta da Safiyya Yana samun nutsuwa ya sauka daga kanta ya rufeta da dukan ita ba budurwa bace Yar iska ce ita a ranar Umar ne ya karbi ragamar mugunta yayi ta azabtar da ita da aiki.yana zaginta akan ita Yar iska ce .
A irin wanna yanayin da Safiyya ke fuskantar.azabar wahala daga wajen Umar da Hafsa da yamma Safiyya na jidar wankin da Hafsa ta loda Mata bayan ta gama wawanka Mata Mari Hajara kuwa suna isa Calaba ta d'au hanyar gidan Umar da yake sananne da lodin Kayanta data Dora aka.
Ko Sallama batayi ba ta Shiga katon gidan da tun a waje ta fara dan Jin sanyi samun wajen da zata zauna Mai kyau Dan ko Mai zaayi sai dai a ayi wlh Zamanta zatayi a gidan tunda Safiyya ce silar siyar da gidan da take zaune cikin rufin asiri.
Kamar a mafarki Safiyya taji muryar Hajara tana dagowa kuwa taga itace
Aguje tayi wurgi da bokitin hannunta taje da zumar kankame hajara Dan gani take kamar zuwanta ne zai saka ta bar gidan
Hajara.kuwa sakin kayanta tayi a kasa ta matsa tana isowa wajenta ta kwashe Safiyya da wani mahaukacin Mari tana "har ni Zaki yaudara Ina uwarki Safiyya har Ni Dana Haifeki Zaki cuta ki hainceni kisa na siyar da gidan Naseer Dan na Miki kayan daki iya nan Bai isheki ba sai da Kika kwashe kudin da Kika bani dan na siyi karamin gida
Toh wlh Tallahi sai kin fito mun da kudin gidan ko Kuma na zauna a gidanan tunda banida gidan da Zan zauna"
"Safiyya hannunta ta fara k'ok'arin ja Dan ta kaita daki sabida Hafsa dake zaune a Kan tabarma data zubo musu Ido sam.bata san tasan abinda ke faruwa.
Hajara cigaba da bambamin masifa tayi tana kwashewa Saffiya albarka dake ta Jan hannunta
Hafsa kuwa ta mik'e tana dakawa Hafsa tsawa tana "Wacce wanan Zaki shigo.mana da.ita gida"?
Hajara wani mugun kallo ta Mata ta kalli Safiyya tana "Halan wanan Mai zubin mazan ce kishiyarki"?
"Nice Mai zubin mazan?
Hafsa tace cikin mamakin Hajara .
Hajara kuwa ta ja Tsaki ta fara k'ok'arin Shiga b'angaren Safiyya.
Hafsa kuwa ta jawota ta kifa mata Marin da sai da Hajara taga walkiya a takaice har waje Hafsa ta fitar da Hajaran ta Kuma rantse bazata kwana a gidan ba.
Hajara haka ta kwashi Kayanta ta nufi gidan Lami tana Shan mugayen alwashi akan kishiyar Safiyya Dan ta Gane Safiyya Bora ce a gidan.
Sai dai shima gidan lamin data Isa kwana uku ta iya yi Sabida abinci sau daya ake dorawa a gidan Sabida talaucin da suke fama dashi.
Gashi shi kansa mijin Lami wani gani gani yake wa Hajaran